< Farawa 35 >

1 Sa’an nan Allah ya ce wa Yaƙub, “Haura zuwa Betel ka yi zama a can, ka kuma gina bagade a can wa Allah wanda ya bayyana gare ka sa’ad da kake gudu daga ɗan’uwanka Isuwa.”
Dieu dit à Jacob: « Lève-toi, monte à Béthel, et tu y habiteras. Fais-y un autel à Dieu, qui t'est apparu lorsque tu fuyais la face d'Ésaü, ton frère. »
2 Saboda haka Yaƙub ya ce wa gidansa da kuma dukan waɗanda suke tare da shi, “Ku zubar da baƙin allolin da kuke da su, ku tsarkake kanku, ku kuma canja tufafinku.
Alors Jacob dit à sa famille et à tous ceux qui étaient avec lui: « Otez les dieux étrangers qui sont au milieu de vous, purifiez-vous et changez de vêtements.
3 Sa’an nan ku zo, mu haura zuwa Betel, inda zan gina bagade wa Allah wanda ya amsa mini a ranar wahalata, wanda kuma ya kasance tare da ni a dukan inda na tafi.”
Levons-nous, et montons à Béthel. J'y ferai un autel à Dieu, qui m'a exaucé au jour de ma détresse et qui a été avec moi sur le chemin que j'ai parcouru. »
4 Saboda haka suka ba Yaƙub dukan baƙin allolin da suke da su, da zoban da suke kunnuwansu, sai Yaƙub ya binne su a ƙarƙashin itacen oak a Shekem.
Ils donnèrent à Jacob tous les dieux étrangers qui étaient dans leurs mains et les anneaux qui étaient à leurs oreilles, et Jacob les cacha sous le chêne qui était près de Sichem.
5 Sa’an nan suka kama hanya, tsoron Allah kuwa ya kama dukan garuruwan da suke kewayensu har babu wanda ya iya bin su.
Ils voyagèrent, et la terreur de Dieu était sur les villes qui les entouraient, et elles ne poursuivirent pas les fils de Jacob.
6 Yaƙub da dukan mutanen da suke tare da shi suka zo Luz (wato, Betel) a ƙasar Kan’ana.
Jacob arriva à Luz (c'est-à-dire à Béthel), qui est dans le pays de Canaan, lui et tout le peuple qui était avec lui.
7 A can ya gina bagade, ya kuma kira wurin El Betel, gama a can ne Allah ya bayyana kansa gare shi sa’ad da yake gudu daga ɗan’uwansa.
Il y bâtit un autel et appela le lieu El Beth El, car c'est là que Dieu se révéla à lui, lorsqu'il fuyait la face de son frère.
8 To, Debora, ungozomar Rebeka ta rasu aka kuma binne ta a ƙarƙashin itacen oak, ƙasa da Betel. Saboda haka aka kira wurin Allon Bakut.
Débora, la nourrice de Rebecca, mourut, et elle fut enterrée au-dessous de Béthel, sous le chêne; et son nom fut appelé Allon Bacuth.
9 Bayan Yaƙub ya komo daga Faddan Aram, sai Allah ya bayyana gare shi, ya kuma albarkace shi.
Dieu apparut de nouveau à Jacob, lorsqu'il revint de Paddan Aram, et il le bénit.
10 Allah ya ce masa, “Sunanka Yaƙub ne, amma ba za a ƙara kira ka Yaƙub ba; sunanka zai zama Isra’ila.” Saboda haka ya ba shi suna Isra’ila.
Dieu lui dit: « Ton nom est Jacob. Ton nom ne sera plus Jacob, mais ton nom sera Israël. » Il lui donna le nom d`Israël.
11 Sai Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi ta haihuwa, ka kuma riɓaɓɓanya. Al’umma da tarin al’ummai za su fito daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga jikinka.
Dieu lui dit: « Je suis le Dieu tout-puissant. Sois fécond et multiplie. Une nation et une multitude de nations naîtront de toi, et des rois sortiront de ton corps.
12 Ƙasar da na ba wa Ibrahim da Ishaku, zan kuma ba ka, zan kuma ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka.”
Le pays que j'ai donné à Abraham et à Isaac, je te le donnerai, et je le donnerai à ta postérité après toi. »
13 Sa’an nan Allah ya tashi sama daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.
Dieu se retira de lui dans le lieu où il lui avait parlé.
14 Yaƙub kuwa ya kafa al’amudin dutse a inda Allah ya yi magana da shi, ya zuba hadaya ta sha a kansa; ya kuma zuba mai a kansa.
Jacob dressa une colonne dans le lieu où il lui avait parlé, une colonne de pierre. Il y versa une libation et y répandit de l'huile.
15 Yaƙub ya kira inda Allah ya yi magana da shi, Betel.
Jacob appela « Béthel » le nom du lieu où Dieu lui avait parlé.
16 Sa’an nan suka tashi daga Betel. Yayinda suna da ɗan nisa da Efrat, sai Rahila ta fara naƙuda ta kuwa sha wahala sosai.
Ils partirent de Béthel. Il y avait encore de la distance à parcourir jusqu'à Ephrath, et Rachel était en travail. Elle a eu un travail difficile.
17 Sa’ad da take cikin zafin haihuwa, sai macen da ta karɓi haihuwar ta ce mata, “Kada ki ji tsoro, gama yanzu kin sami wani ɗa.”
Comme elle était en plein travail, la sage-femme lui dit: « N'aie pas peur, car tu vas avoir un autre fils. »
18 Yayinda take jan numfashinta na ƙarshe, sai ta ba wa ɗanta suna Ben-Oni. Amma mahaifinsa ya kira shi Benyamin.
Comme son âme s'en allait (car elle est morte), elle l'appela Benoni, mais son père l'appela Benjamin.
19 Ta haka Rahila ta rasu, aka kuma binne ta a hanya zuwa Efrata (wato, Betlehem).
Rachel mourut, et elle fut enterrée sur le chemin d'Éphrata (appelée aussi Bethléhem).
20 Yaƙub ya kafa al’amudi bisa kabarinta, al’amudin kabarin Rahila ke nan, wanda yake can har wa yau.
Jacob dressa un pilier sur son tombeau. C'est encore aujourd'hui le pilier du tombeau de Rachel.
21 Isra’ila ya yi gaba, ya kafa tentinsa gaba da Migdal Eder.
Israël partit en voyage et étendit sa tente au-delà de la tour d'Eder.
22 Yayinda Isra’ila yana zama a wancan yanki, Ruben ya shiga ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra’ila kuwa ya ji labari. Yaƙub ya haifi’ya’ya maza goma sha biyu.
Pendant qu'Israël habitait dans ce pays, Ruben alla coucher avec Bilha, la concubine de son père, et Israël en entendit parler. Les fils de Jacob étaient au nombre de douze.
23 ’Ya’yan Liyatu maza, Ruben shi ne ɗan fari na Yaƙub. Sauran su ne, Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar da Zebulun.
Fils de Léa: Ruben (premier-né de Jacob), Siméon, Lévi, Juda, Issacar et Zabulon.
24 ’Ya’yan Rahila maza su ne, Yusuf da Benyamin.
Fils de Rachel: Joseph et Benjamin.
25 ’Ya’yan Bilha maza, mai hidimar Rahila su ne, Dan da Naftali.
Fils de Bilha (servante de Rachel): Dan et Nephtali.
26 ’Ya’yan Zilfa maza, mai hidimar Liyatu su ne, Gad da Asher. Waɗannan su ne’ya’yan Yaƙub maza, waɗanda aka haifa masa a Faddan Aram.
Fils de Zilpa (servante de Léa): Gad et Aser. Ce sont là les fils de Jacob, qui lui sont nés à Paddan Aram.
27 Yaƙub ya dawo gida wurin mahaifinsa Ishaku a Mamre, kusa da Kiriyat Arba (wato, Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna.
Jacob vint auprès d'Isaac, son père, à Mamré, à Kiriath Arba (qui est Hébron), où Abraham et Isaac vivaient en étrangers.
28 Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin,
Les jours d'Isaac furent de cent quatre-vingts ans.
29 sa’an nan ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuwa mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa da kyakkyawan tsufa da kuma cikakken shekaru.’Ya’yansa maza, Isuwa da Yaƙub suka binne shi.
Isaac rendit l'esprit et mourut, et il fut recueilli auprès de son peuple, âgé et rassasié de jours. Ésaü et Jacob, ses fils, l'ensevelirent.

< Farawa 35 >