< Farawa 35 >
1 Sa’an nan Allah ya ce wa Yaƙub, “Haura zuwa Betel ka yi zama a can, ka kuma gina bagade a can wa Allah wanda ya bayyana gare ka sa’ad da kake gudu daga ɗan’uwanka Isuwa.”
And God saith unto Jacob, 'Rise, go up to Bethel, and dwell there, and make there an altar to God, who appeared unto thee in thy fleeing from the face of Esau thy brother.'
2 Saboda haka Yaƙub ya ce wa gidansa da kuma dukan waɗanda suke tare da shi, “Ku zubar da baƙin allolin da kuke da su, ku tsarkake kanku, ku kuma canja tufafinku.
And Jacob saith unto his household, and unto all who [are] with him, 'Turn aside the gods of the stranger which [are] in your midst, and cleanse yourselves, and change your garments;
3 Sa’an nan ku zo, mu haura zuwa Betel, inda zan gina bagade wa Allah wanda ya amsa mini a ranar wahalata, wanda kuma ya kasance tare da ni a dukan inda na tafi.”
and we rise, and go up to Bethel, and I make there an altar to God, who is answering me in the day of my distress, and is with me in the way that I have gone.'
4 Saboda haka suka ba Yaƙub dukan baƙin allolin da suke da su, da zoban da suke kunnuwansu, sai Yaƙub ya binne su a ƙarƙashin itacen oak a Shekem.
And they give unto Jacob all the gods of the stranger that [are] in their hand, and the rings that [are] in their ears, and Jacob hideth them under the oak which [is] by Shechem;
5 Sa’an nan suka kama hanya, tsoron Allah kuwa ya kama dukan garuruwan da suke kewayensu har babu wanda ya iya bin su.
and they journey, and the terror of God is on the cities which [are] round about them, and they have not pursued after the sons of Jacob.
6 Yaƙub da dukan mutanen da suke tare da shi suka zo Luz (wato, Betel) a ƙasar Kan’ana.
And Jacob cometh in to Luz which [is] in the land of Canaan (it [is] Bethel), he and all the people who [are] with him,
7 A can ya gina bagade, ya kuma kira wurin El Betel, gama a can ne Allah ya bayyana kansa gare shi sa’ad da yake gudu daga ɗan’uwansa.
and he buildeth there an altar, and proclaimeth at the place the God of Bethel: for there had God been revealed unto him, in his fleeing from the face of his brother.
8 To, Debora, ungozomar Rebeka ta rasu aka kuma binne ta a ƙarƙashin itacen oak, ƙasa da Betel. Saboda haka aka kira wurin Allon Bakut.
And Deborah, Rebekah's nurse, dieth, and she is buried at the lower part of Bethel, under the oak, and he calleth its name 'Oak of weeping.'
9 Bayan Yaƙub ya komo daga Faddan Aram, sai Allah ya bayyana gare shi, ya kuma albarkace shi.
And God appeareth unto Jacob again, in his coming from Padan-Aram, and blesseth him;
10 Allah ya ce masa, “Sunanka Yaƙub ne, amma ba za a ƙara kira ka Yaƙub ba; sunanka zai zama Isra’ila.” Saboda haka ya ba shi suna Isra’ila.
and God saith to him, 'Thy name [is] Jacob: thy name is no more called Jacob, but Israel is thy name;' and He calleth his name Israel.
11 Sai Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi ta haihuwa, ka kuma riɓaɓɓanya. Al’umma da tarin al’ummai za su fito daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga jikinka.
And God saith to him, 'I [am] God Almighty; be fruitful and multiply, a nation and an assembly of nations is from thee, and kings from thy loins go out;
12 Ƙasar da na ba wa Ibrahim da Ishaku, zan kuma ba ka, zan kuma ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka.”
and the land which I have given to Abraham and to Isaac — to thee I give it, yea to thy seed after thee I give the land.'
13 Sa’an nan Allah ya tashi sama daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.
And God goeth up from him, in the place where He hath spoken with him.
14 Yaƙub kuwa ya kafa al’amudin dutse a inda Allah ya yi magana da shi, ya zuba hadaya ta sha a kansa; ya kuma zuba mai a kansa.
And Jacob setteth up a standing pillar in the place where He hath spoken with him, a standing pillar of stone, and he poureth on it an oblation, and he poureth on it oil;
15 Yaƙub ya kira inda Allah ya yi magana da shi, Betel.
and Jacob calleth the name of the place where God spake with him Bethel.
16 Sa’an nan suka tashi daga Betel. Yayinda suna da ɗan nisa da Efrat, sai Rahila ta fara naƙuda ta kuwa sha wahala sosai.
And they journey from Bethel, and there is yet a kibrath of land before entering Ephratha, and Rachel beareth, and is sharply pained in her bearing;
17 Sa’ad da take cikin zafin haihuwa, sai macen da ta karɓi haihuwar ta ce mata, “Kada ki ji tsoro, gama yanzu kin sami wani ɗa.”
and it cometh to pass, in her being sharply pained in her bearing, that the midwife saith to her, 'Fear not, for this also [is] a son for thee.'
18 Yayinda take jan numfashinta na ƙarshe, sai ta ba wa ɗanta suna Ben-Oni. Amma mahaifinsa ya kira shi Benyamin.
And it cometh to pass in the going out of her soul (for she died), that she calleth his name Ben-Oni; and his father called him Benjamin;
19 Ta haka Rahila ta rasu, aka kuma binne ta a hanya zuwa Efrata (wato, Betlehem).
and Rachel dieth, and is buried in the way to Ephratha, which [is] Bethlehem,
20 Yaƙub ya kafa al’amudi bisa kabarinta, al’amudin kabarin Rahila ke nan, wanda yake can har wa yau.
and Jacob setteth up a standing pillar over her grave; which [is] the standing pillar of Rachel's grave unto this day.
21 Isra’ila ya yi gaba, ya kafa tentinsa gaba da Migdal Eder.
And Israel journeyeth, and stretcheth out his tent beyond the tower of Edar;
22 Yayinda Isra’ila yana zama a wancan yanki, Ruben ya shiga ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra’ila kuwa ya ji labari. Yaƙub ya haifi’ya’ya maza goma sha biyu.
and it cometh to pass in Israel's dwelling in that land, that Reuben goeth, and lieth with Bilhah his father's concubine; and Israel heareth.
23 ’Ya’yan Liyatu maza, Ruben shi ne ɗan fari na Yaƙub. Sauran su ne, Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar da Zebulun.
And the sons of Jacob are twelve. Sons of Leah: Jacob's first-born Reuben, and Simeon, and Levi, and Judah, and Issachar, and Zebulun.
24 ’Ya’yan Rahila maza su ne, Yusuf da Benyamin.
Sons of Rachel: Joseph and Benjamin.
25 ’Ya’yan Bilha maza, mai hidimar Rahila su ne, Dan da Naftali.
And sons of Bilhah, Rachel's maid-servant: Dan and Naphtali.
26 ’Ya’yan Zilfa maza, mai hidimar Liyatu su ne, Gad da Asher. Waɗannan su ne’ya’yan Yaƙub maza, waɗanda aka haifa masa a Faddan Aram.
And sons of Zilpah, Leah's maid-servant: Gad and Asher. These [are] sons of Jacob, who have been born to him in Padan-Aram.
27 Yaƙub ya dawo gida wurin mahaifinsa Ishaku a Mamre, kusa da Kiriyat Arba (wato, Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna.
And Jacob cometh unto Isaac his father, at Mamre, the city of Arba (which [is] Hebron), where Abraham and Isaac have sojourned.
28 Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin,
And the days of Isaac are a hundred and eighty years,
29 sa’an nan ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuwa mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa da kyakkyawan tsufa da kuma cikakken shekaru.’Ya’yansa maza, Isuwa da Yaƙub suka binne shi.
and Isaac expireth, and dieth, and is gathered unto his people, aged and satisfied with days; and bury him do Esau and Jacob his sons.