< Farawa 35 >
1 Sa’an nan Allah ya ce wa Yaƙub, “Haura zuwa Betel ka yi zama a can, ka kuma gina bagade a can wa Allah wanda ya bayyana gare ka sa’ad da kake gudu daga ɗan’uwanka Isuwa.”
[Some time later] God said to Jacob, “Go up to Bethel, and live there. Build an altar to worship me, God, who appeared to you when you were fleeing from your older brother Esau.”
2 Saboda haka Yaƙub ya ce wa gidansa da kuma dukan waɗanda suke tare da shi, “Ku zubar da baƙin allolin da kuke da su, ku tsarkake kanku, ku kuma canja tufafinku.
So Jacob said to his household and to all the others who were with him, “Get rid of the idols you brought from Mesopotamia. Also, bathe yourselves and put on clean clothes.
3 Sa’an nan ku zo, mu haura zuwa Betel, inda zan gina bagade wa Allah wanda ya amsa mini a ranar wahalata, wanda kuma ya kasance tare da ni a dukan inda na tafi.”
Then we will get ready and go up to Bethel. There I will make an altar to worship God. He is the one who helped me at the time when I was greatly distressed and afraid, and he has been with me wherever I have gone.”
4 Saboda haka suka ba Yaƙub dukan baƙin allolin da suke da su, da zoban da suke kunnuwansu, sai Yaƙub ya binne su a ƙarƙashin itacen oak a Shekem.
So they gave to Jacob all the idols that they had brought, and all their earrings. Jacob buried them in the ground under the big oak tree that was near Shechem [town].
5 Sa’an nan suka kama hanya, tsoron Allah kuwa ya kama dukan garuruwan da suke kewayensu har babu wanda ya iya bin su.
As they prepared to leave there, God caused the people who lived in the cities around them to be extremely afraid of Jacob’s family [PRS], so that they did not pursue and attack them.
6 Yaƙub da dukan mutanen da suke tare da shi suka zo Luz (wato, Betel) a ƙasar Kan’ana.
Jacob and all those who were with him came to Luz, which is now called Bethel, in the Canaan region.
7 A can ya gina bagade, ya kuma kira wurin El Betel, gama a can ne Allah ya bayyana kansa gare shi sa’ad da yake gudu daga ɗan’uwansa.
There he built an altar. He named the place El-Bethel, [which means ‘God of Bethel]’, because it was there that God revealed himself to Jacob when he was fleeing from his older brother Esau.
8 To, Debora, ungozomar Rebeka ta rasu aka kuma binne ta a ƙarƙashin itacen oak, ƙasa da Betel. Saboda haka aka kira wurin Allon Bakut.
Deborah, who had taken care of Isaac’s wife Rebekah when Rebekah was a small girl, was now very old. She died and was buried under an oak tree south of Bethel. So they named that place Allon-Bacuth, [which means ‘oak of weeping’].
9 Bayan Yaƙub ya komo daga Faddan Aram, sai Allah ya bayyana gare shi, ya kuma albarkace shi.
After Jacob and his family returned from Paddan-Aram/Mesopotamia, while they were still at Bethel, God appeared to Jacob again and blessed him.
10 Allah ya ce masa, “Sunanka Yaƙub ne, amma ba za a ƙara kira ka Yaƙub ba; sunanka zai zama Isra’ila.” Saboda haka ya ba shi suna Isra’ila.
God said to him again, “Your name will no longer be Jacob. It will be Israel.” So Jacob was then called ‘Israel’.
11 Sai Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi ta haihuwa, ka kuma riɓaɓɓanya. Al’umma da tarin al’ummai za su fito daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga jikinka.
Then God said to him, “I am God Almighty. Produce many children. Your descendants will become many nations, and some of your descendants will be kings.
12 Ƙasar da na ba wa Ibrahim da Ishaku, zan kuma ba ka, zan kuma ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka.”
The land that I promised to give to [your grandfather] Abraham and [your father] Isaac, I will give to you. I will also give it to your descendants.”
13 Sa’an nan Allah ya tashi sama daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.
When God finished talking there with Jacob, he left him.
14 Yaƙub kuwa ya kafa al’amudin dutse a inda Allah ya yi magana da shi, ya zuba hadaya ta sha a kansa; ya kuma zuba mai a kansa.
Jacob set up a large stone at the place where God had talked with him. He poured some wine and some [olive] oil on it to dedicate it to God.
15 Yaƙub ya kira inda Allah ya yi magana da shi, Betel.
Jacob named that place Bethel, [which means ‘house of God]’, because God had spoken to him there.
16 Sa’an nan suka tashi daga Betel. Yayinda suna da ɗan nisa da Efrat, sai Rahila ta fara naƙuda ta kuwa sha wahala sosai.
Jacob and his family left Bethel and traveled south toward Ephrath [town]. When they were still some distance from Ephrath, Rachel began to have severe childbirth pains.
17 Sa’ad da take cikin zafin haihuwa, sai macen da ta karɓi haihuwar ta ce mata, “Kada ki ji tsoro, gama yanzu kin sami wani ɗa.”
When her pain was the most severe, the (midwife/woman who helped her to give birth) said to Rachel, “Do not be afraid, because now you have given birth to another son!”
18 Yayinda take jan numfashinta na ƙarshe, sai ta ba wa ɗanta suna Ben-Oni. Amma mahaifinsa ya kira shi Benyamin.
But she was dying, and with her last breath she said, “Name him Benoni,” [which means ‘son of my sorrow]’, but his father named him Benjamin, [which means ‘son of my right hand]’.
19 Ta haka Rahila ta rasu, aka kuma binne ta a hanya zuwa Efrata (wato, Betlehem).
After Rachel died, she was buried alongside the road to Ephrath, which is [now called] Bethlehem.
20 Yaƙub ya kafa al’amudi bisa kabarinta, al’amudin kabarin Rahila ke nan, wanda yake can har wa yau.
Jacob set up a large stone over her grave, and it is still there, showing where Rachel’s grave is.
21 Isra’ila ya yi gaba, ya kafa tentinsa gaba da Migdal Eder.
Jacob, whose new name was Israel, continued traveling with his family, and he set up his tents on the south side of the watchtower at Eder [town].
22 Yayinda Isra’ila yana zama a wancan yanki, Ruben ya shiga ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra’ila kuwa ya ji labari. Yaƙub ya haifi’ya’ya maza goma sha biyu.
While they were living in that area, Jacob’s son Reuben had sex [EUP] with Bilhah, one of his father’s (concubines/female slaves whom he had taken as a secondary wife). Someone told Jacob about it, and it made him very angry. (I will now give you/Here is) a list of Jacob’s twelve sons.
23 ’Ya’yan Liyatu maza, Ruben shi ne ɗan fari na Yaƙub. Sauran su ne, Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar da Zebulun.
The sons of Leah were Reuben, who was Jacob’s oldest son, then Simeon, Levi, Judah, Issachar and Zebulon.
24 ’Ya’yan Rahila maza su ne, Yusuf da Benyamin.
The sons of Rachel were Joseph and Benjamin.
25 ’Ya’yan Bilha maza, mai hidimar Rahila su ne, Dan da Naftali.
The sons of Rachel’s female slave Bilhah were Dan and Naphtali.
26 ’Ya’yan Zilfa maza, mai hidimar Liyatu su ne, Gad da Asher. Waɗannan su ne’ya’yan Yaƙub maza, waɗanda aka haifa masa a Faddan Aram.
The sons of Leah’s female slave Zilpah were Gad and Asher. All those sons of Jacob, except Benjamin, were born while he was living in Paddan-Aram/Mesopotamia.
27 Yaƙub ya dawo gida wurin mahaifinsa Ishaku a Mamre, kusa da Kiriyat Arba (wato, Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna.
Jacob had returned back home to see his father Isaac at Mamre, which is also named Kiriath-Arba, and which is now named Hebron. Isaac’s father Abraham had also lived there.
28 Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin,
Isaac lived until he was 180 years old.
29 sa’an nan ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuwa mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa da kyakkyawan tsufa da kuma cikakken shekaru.’Ya’yansa maza, Isuwa da Yaƙub suka binne shi.
He was very old when he died, joining his ancestors who had died previously. His sons Esau and Jacob buried his body.