< Farawa 35 >
1 Sa’an nan Allah ya ce wa Yaƙub, “Haura zuwa Betel ka yi zama a can, ka kuma gina bagade a can wa Allah wanda ya bayyana gare ka sa’ad da kake gudu daga ɗan’uwanka Isuwa.”
Then God sayde to Iaakob, Arise, goe vp to Beth-el and dwell there, and make there an altar vnto God, that appeared vnto thee, when thou fleddest from Esau thy brother.
2 Saboda haka Yaƙub ya ce wa gidansa da kuma dukan waɗanda suke tare da shi, “Ku zubar da baƙin allolin da kuke da su, ku tsarkake kanku, ku kuma canja tufafinku.
Then saide Iaakob vnto his houshold and to all that were with him, Put away the strange gods that are among you, and clense your selues, and change your garments:
3 Sa’an nan ku zo, mu haura zuwa Betel, inda zan gina bagade wa Allah wanda ya amsa mini a ranar wahalata, wanda kuma ya kasance tare da ni a dukan inda na tafi.”
For we will rise and goe vp to Beth-el, and I will make an altar there vnto God, which heard me in the day of my tribulation, and was with me in the way which I went.
4 Saboda haka suka ba Yaƙub dukan baƙin allolin da suke da su, da zoban da suke kunnuwansu, sai Yaƙub ya binne su a ƙarƙashin itacen oak a Shekem.
And they gaue vnto Iaakob all the strange gods, which were in their hands, and all their earings which were in their eares, and Iaakob hidde them vnder an oke, which was by Shechem.
5 Sa’an nan suka kama hanya, tsoron Allah kuwa ya kama dukan garuruwan da suke kewayensu har babu wanda ya iya bin su.
Then they went on their iourney, and the feare of God was vpon the cities that were roud about them: so that they did not follow after the sonnes of Iaakob.
6 Yaƙub da dukan mutanen da suke tare da shi suka zo Luz (wato, Betel) a ƙasar Kan’ana.
So came Iaakob to Luz, which is in the land of Canaan: (the same is Beth-el) hee and all the people that was with him.
7 A can ya gina bagade, ya kuma kira wurin El Betel, gama a can ne Allah ya bayyana kansa gare shi sa’ad da yake gudu daga ɗan’uwansa.
And he built there an altar, and had called the place, The God of Beth-el, because that God appeared vnto him there, when he fled from his brother.
8 To, Debora, ungozomar Rebeka ta rasu aka kuma binne ta a ƙarƙashin itacen oak, ƙasa da Betel. Saboda haka aka kira wurin Allon Bakut.
Then Deborah Rebekahs nourse dyed, and was buried beneath Beth-el vnder an oke: and he called the name of it Allon Bachuth.
9 Bayan Yaƙub ya komo daga Faddan Aram, sai Allah ya bayyana gare shi, ya kuma albarkace shi.
Againe God appeared vnto Iaakob, after he came out of Padan Aram, and blessed him.
10 Allah ya ce masa, “Sunanka Yaƙub ne, amma ba za a ƙara kira ka Yaƙub ba; sunanka zai zama Isra’ila.” Saboda haka ya ba shi suna Isra’ila.
Moreouer God said vnto him, Thy name is Iaakob: thy name shalbe no more called Iaakob, but Israel shalbe thy name: and hee called his name Israel.
11 Sai Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi ta haihuwa, ka kuma riɓaɓɓanya. Al’umma da tarin al’ummai za su fito daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga jikinka.
Againe God said vnto him, I am God all sufficient. growe, and multiplie. a nation and a multitude of nations shall spring of thee, and Kings shall come out of thy loynes.
12 Ƙasar da na ba wa Ibrahim da Ishaku, zan kuma ba ka, zan kuma ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka.”
Also I will giue the lande, which I gaue to Abraham and Izhak, vnto thee: and vnto thy seede after thee will I giue that land.
13 Sa’an nan Allah ya tashi sama daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.
So God ascended from him in the place where he had talked with him.
14 Yaƙub kuwa ya kafa al’amudin dutse a inda Allah ya yi magana da shi, ya zuba hadaya ta sha a kansa; ya kuma zuba mai a kansa.
And Iaakob set vp a pillar in the place where he talked with him, a pillar of stone, and powred drinke offring thereon: also hee powred oyle thereon.
15 Yaƙub ya kira inda Allah ya yi magana da shi, Betel.
And Iaakob called the name of the place, where God spake with him, Beth-el.
16 Sa’an nan suka tashi daga Betel. Yayinda suna da ɗan nisa da Efrat, sai Rahila ta fara naƙuda ta kuwa sha wahala sosai.
Then they departed from Beth-el, and when there was about halfe a daies iourney of ground to come to Ephrath, Rahel trauailed, and in trauailing she was in perill.
17 Sa’ad da take cikin zafin haihuwa, sai macen da ta karɓi haihuwar ta ce mata, “Kada ki ji tsoro, gama yanzu kin sami wani ɗa.”
And whe she was in paines of her labour, the midwife saide vnto her, Feare not: for thou shalt haue this sonne also.
18 Yayinda take jan numfashinta na ƙarshe, sai ta ba wa ɗanta suna Ben-Oni. Amma mahaifinsa ya kira shi Benyamin.
Then as she was about to yeelde vp the Ghost (for she died) she called his name Ben-oni, but his father called him Beniamin.
19 Ta haka Rahila ta rasu, aka kuma binne ta a hanya zuwa Efrata (wato, Betlehem).
Thus died Rahel, and was buried in the way to Ephrath, which is Beth-lehem.
20 Yaƙub ya kafa al’amudi bisa kabarinta, al’amudin kabarin Rahila ke nan, wanda yake can har wa yau.
And Iaakob set a pillar vpon her graue: This is the pillar of Rahels graue vnto this day.
21 Isra’ila ya yi gaba, ya kafa tentinsa gaba da Migdal Eder.
Then Israel went forwarde, and pitched his tent beyond Migdal-eder.
22 Yayinda Isra’ila yana zama a wancan yanki, Ruben ya shiga ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra’ila kuwa ya ji labari. Yaƙub ya haifi’ya’ya maza goma sha biyu.
Now, when Israel dwelt in that land, Reuben went, and lay with Bilhah his fathers concubine, and it came to Israels eare. And Iaakob had twelue sonnes.
23 ’Ya’yan Liyatu maza, Ruben shi ne ɗan fari na Yaƙub. Sauran su ne, Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar da Zebulun.
The sonnes of Leah: Reuben Iaakobs eldest sonne, and Simeon, and Leui, and Iudah, and Issachar, and Zebulun.
24 ’Ya’yan Rahila maza su ne, Yusuf da Benyamin.
The sonnes of Rahel: Ioseph and Beniamin.
25 ’Ya’yan Bilha maza, mai hidimar Rahila su ne, Dan da Naftali.
And the sonnes of Bilhah Rahels maide: Dan and Naphtali.
26 ’Ya’yan Zilfa maza, mai hidimar Liyatu su ne, Gad da Asher. Waɗannan su ne’ya’yan Yaƙub maza, waɗanda aka haifa masa a Faddan Aram.
And the sonnes of Zilpah Leahs maide: Gad and Asher. These are the sonnes of Iaakob, which were borne him in Padan Aram.
27 Yaƙub ya dawo gida wurin mahaifinsa Ishaku a Mamre, kusa da Kiriyat Arba (wato, Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna.
Then Iaakob came vnto Izhak his father to Mamre a citie of Arbah: this is Hebron, where Abraham and Izhak were strangers.
28 Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin,
And the daies of Izhak were an hundreth and fourescore yeeres.
29 sa’an nan ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuwa mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa da kyakkyawan tsufa da kuma cikakken shekaru.’Ya’yansa maza, Isuwa da Yaƙub suka binne shi.
And Izhak gaue vp the ghost and died, and was gathered vnto his people, being olde and full of daies: and his sonnes Esau and Iaakob buried him.