< Farawa 35 >
1 Sa’an nan Allah ya ce wa Yaƙub, “Haura zuwa Betel ka yi zama a can, ka kuma gina bagade a can wa Allah wanda ya bayyana gare ka sa’ad da kake gudu daga ɗan’uwanka Isuwa.”
Then God told Jacob, “Get ready to go to Bethel and live there. Build an altar there to God, who appeared to you when you were running away from your brother Esau.”
2 Saboda haka Yaƙub ya ce wa gidansa da kuma dukan waɗanda suke tare da shi, “Ku zubar da baƙin allolin da kuke da su, ku tsarkake kanku, ku kuma canja tufafinku.
So Jacob told his family and everyone who was with him, “Get rid of the pagan idols you have with you. Purify yourselves and change your clothes.
3 Sa’an nan ku zo, mu haura zuwa Betel, inda zan gina bagade wa Allah wanda ya amsa mini a ranar wahalata, wanda kuma ya kasance tare da ni a dukan inda na tafi.”
We have to get ready and go to Bethel so I can build an altar to God who answered me in my time of trouble. He has been with me wherever I went.”
4 Saboda haka suka ba Yaƙub dukan baƙin allolin da suke da su, da zoban da suke kunnuwansu, sai Yaƙub ya binne su a ƙarƙashin itacen oak a Shekem.
They handed over to Jacob all the pagan idols they had, as well as their earrings, and he buried them under the oak tree at Shechem.
5 Sa’an nan suka kama hanya, tsoron Allah kuwa ya kama dukan garuruwan da suke kewayensu har babu wanda ya iya bin su.
As they left on their journey, the terror of God spread over all the surrounding towns, so nobody tried to retaliate against Jacob's sons.
6 Yaƙub da dukan mutanen da suke tare da shi suka zo Luz (wato, Betel) a ƙasar Kan’ana.
Jacob and everyone with him arrived at Luz (also known as Bethel) in the country of Canaan.
7 A can ya gina bagade, ya kuma kira wurin El Betel, gama a can ne Allah ya bayyana kansa gare shi sa’ad da yake gudu daga ɗan’uwansa.
He built an altar there and called the place El-Bethel, because that was where God had appeared to him when he was running away from his brother Esau.
8 To, Debora, ungozomar Rebeka ta rasu aka kuma binne ta a ƙarƙashin itacen oak, ƙasa da Betel. Saboda haka aka kira wurin Allon Bakut.
Deborah, Rebekah's nurse, died and was buried under the oak near Bethel. So it was named “the oak of weeping.”
9 Bayan Yaƙub ya komo daga Faddan Aram, sai Allah ya bayyana gare shi, ya kuma albarkace shi.
God appeared to Jacob again and blessed him after his return from Paddan-aram.
10 Allah ya ce masa, “Sunanka Yaƙub ne, amma ba za a ƙara kira ka Yaƙub ba; sunanka zai zama Isra’ila.” Saboda haka ya ba shi suna Isra’ila.
God told him, “Jacob will not be your name any longer. Instead of Jacob your name will be Israel.” So God called him Israel.
11 Sai Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi ta haihuwa, ka kuma riɓaɓɓanya. Al’umma da tarin al’ummai za su fito daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga jikinka.
Then God said, “I am God Almighty! Reproduce, increase, and you will become a nation—in fact a group of nations—and kings will be among your descendants.
12 Ƙasar da na ba wa Ibrahim da Ishaku, zan kuma ba ka, zan kuma ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka.”
I will give to you and to your descendants the land I also gave to Abraham and Isaac.”
13 Sa’an nan Allah ya tashi sama daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.
Then God left the place where he had been speaking to Jacob.
14 Yaƙub kuwa ya kafa al’amudin dutse a inda Allah ya yi magana da shi, ya zuba hadaya ta sha a kansa; ya kuma zuba mai a kansa.
Afterwards Jacob set up a stone pillar where God had spoken with him. He poured out a drink offering on it, and also olive oil.
15 Yaƙub ya kira inda Allah ya yi magana da shi, Betel.
Jacob called the place Bethel, because he had spoken with God there.
16 Sa’an nan suka tashi daga Betel. Yayinda suna da ɗan nisa da Efrat, sai Rahila ta fara naƙuda ta kuwa sha wahala sosai.
Then they moved on from Bethel. While they were still some distance from Ephrath, Rachel went into labor and had great difficulty giving birth.
17 Sa’ad da take cikin zafin haihuwa, sai macen da ta karɓi haihuwar ta ce mata, “Kada ki ji tsoro, gama yanzu kin sami wani ɗa.”
When she was in the worst birth-pains, the midwife told her, “Don't give up—you have another son!”
18 Yayinda take jan numfashinta na ƙarshe, sai ta ba wa ɗanta suna Ben-Oni. Amma mahaifinsa ya kira shi Benyamin.
But she was dying, and with her last breath she named him Benoni. But his father named him Benjamin.
19 Ta haka Rahila ta rasu, aka kuma binne ta a hanya zuwa Efrata (wato, Betlehem).
Rachel died and was buried on the way to Ephrath (also known as Bethlehem).
20 Yaƙub ya kafa al’amudi bisa kabarinta, al’amudin kabarin Rahila ke nan, wanda yake can har wa yau.
Jacob set up a stone memorial over Rachel's grave, and it's still there to this day.
21 Isra’ila ya yi gaba, ya kafa tentinsa gaba da Migdal Eder.
Israel moved on and camped beyond the watch tower at Eder.
22 Yayinda Isra’ila yana zama a wancan yanki, Ruben ya shiga ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra’ila kuwa ya ji labari. Yaƙub ya haifi’ya’ya maza goma sha biyu.
During the time he was living there, Reuben went and slept with Bilhah, his father's concubine, and Israel found out about it. These were the twelve sons of Jacob:
23 ’Ya’yan Liyatu maza, Ruben shi ne ɗan fari na Yaƙub. Sauran su ne, Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar da Zebulun.
The sons of Leah: Reuben (Jacob's firstborn), Simeon, Levi, Judah, Issachar, and Zebulun.
24 ’Ya’yan Rahila maza su ne, Yusuf da Benyamin.
The sons of Rachel: Joseph and Benjamin.
25 ’Ya’yan Bilha maza, mai hidimar Rahila su ne, Dan da Naftali.
The sons of Rachel's personal maid Bilhah: Dan and Naphtali.
26 ’Ya’yan Zilfa maza, mai hidimar Liyatu su ne, Gad da Asher. Waɗannan su ne’ya’yan Yaƙub maza, waɗanda aka haifa masa a Faddan Aram.
The sons of Leah's personal maid Zilpah: Gad and Asher. These were the sons of Jacob, who were born to him while in Paddan-aram.
27 Yaƙub ya dawo gida wurin mahaifinsa Ishaku a Mamre, kusa da Kiriyat Arba (wato, Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna.
Jacob returned home to his father Isaac at Mamre, near Kiriath-arba (also known as Hebron), where Abraham and Isaac had lived.
28 Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin,
Isaac lived to be 180
29 sa’an nan ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuwa mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa da kyakkyawan tsufa da kuma cikakken shekaru.’Ya’yansa maza, Isuwa da Yaƙub suka binne shi.
when he breathed his last and died at an old age. He had lived a full life, and now he joined his forefathers in death. His sons Esau and Jacob buried him.