< Farawa 34 >
1 To, Dina,’yar da Liyatu ta haifa wa Yaƙub, ta je ta ziyarci matan ƙasar.
Men Dina Leas dotter, den hon Jacob födt hade, gick ut till att bese dess landsens döttrar.
2 Sa’ad da Shekem ɗan Hamor Bahiwiye mai mulkin wurin ya gan ta, sai ya kama ta, ya kwana da ita, ya ɓata ta.
Då Sichem, Hemors Heveens son, som var dess landsens herre, såg henne, tog han henne, och belägrade henne, och förkränkte henne.
3 Zuciyarsa kuwa ta damu da son Dina’yar Yaƙub, ya kuwa ƙaunaci yarinyar, ya yi mata magana a hankali.
Och hon låg honom hårdt på hjertat, och han hade pigona kära, och talade ljufliga med henne.
4 Sai Shekem ya ce wa mahaifinsa Hamor, “Ka auro mini wannan yarinya ta zama matata.”
Och Sichem sade till sin fader Hemor: Tag mig den pigona till hustru.
5 Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa an ɓata’yarsa Dina, sai ya yi shiru game da batun sai’ya’yansa maza sun dawo gida, gama’ya’yansa suna a jeji tare da dabbobinsa suna kiwo.
Och Jacob förnam, att hans dotter Dina var skämd, och hans söner voro med boskapenom ute på markene: Och Jacob tigde till dess de kommo.
6 Sai Hamor mahaifin Shekem ya je don yă yi magana da Yaƙub.
Då gick Hemor Sichems fader ut till Jacob, till att tala med honom.
7 Da’ya’yan Yaƙub maza suka dawo daga jeji sai suka ji labarin. Abin kuwa ya zafe su ƙwarai, don Shekem ya jawo abin kunya wa jama’ar Isra’ila ta wurin kwana da’yar Yaƙub, don bai kamata wannan abu yă faru ba.
I det kommo Jacobs söner af markene; och då de det hörde, förtröt det männerna, och vordo ganska vrede, att han hade gjort en dårskap i Israel, och belägrat Jacobs dotter; ty det var icke rätt gjordt.
8 Amma Hamor ya ce musu, “Ɗana Shekem ya sa zuciyarsa a kan’yarku. Ina roƙonku ku ba shi ita yă aura.
Då talade Hemor med dem, och sade: Mins sons Sichems hjerta trängtar efter edra dotter; käre, gifver honom henne till hustru.
9 Ku yi auratayya da mu; ku aurar mana da’ya’yanku mata, ku kuma ku auro’ya’yanmu mata wa kanku.
Befrynder eder med oss; gifver oss edra döttrar, och tager I våra döttrar.
10 Za ku iya zauna a cikinmu, ƙasar tana nan a buɗe dominku. Ku yi zama a cikinta, ku yi sana’a, ku kuma sami dukiya.”
Och bor när oss: Landet skall stå eder öppet; bygger och bruker, och bor derinne.
11 Sai Shekem ya ce wa mahaifin Dina da kuma’yan’uwanta. “Bari in sami tagomashi a idanunku, zan kuwa ba ku duk abin da kuka tambaya.
Och Sichem sade till hennes fader och bröder: Låter mig finna nåd när eder, hvad I mig sägen, det vill jag gifva.
12 Ku faɗa mini nawa ne dukiyar aure da kuma sadakin da zan kawo bisa ga yadda kuke so, zan kuwa biya duk abin da kuka ce. Ku dai bar ni in aure yarinyar ta zama matata.”
Begärer man troliga af mig morgongåfvor och skänker, jag vill gifva, som I begären; gifver mig allenast pigona till hustru.
13 Domin an ɓata’yar’uwansu Dina, sai’ya’yan Yaƙub maza suka amsa a ha’ince yayinda suke wa Shekem da mahaifinsa Hamor magana.
Då svarade Jacobs söner Sichem, och hans fader Hemor, och talade bedrägeliga, derföre, att deras syster Dina var skämd:
14 Suka ce musu, “Ba za mu iya yin wannan abu ba, ba za mu iya ba da’yar’uwarmu ga mutumin da ba shi da kaciya ba. Wannan zai zama abin kunya ne a gare mu.
Och sade till dem: Vi kunne det icke göra, att vi skole gifva våra syster enom oomskornom manne; ty det vore oss en skam.
15 Za mu yarda da wannan kaɗai ta wannan sharaɗi, cewa za ku zama kamar mu ta wurin yin wa dukan’ya’yanku maza kaciya.
Dock likväl vilje vi vara eder till viljes, om I varden oss like, och allt mankön ibland eder varder omskoret.
16 Sa’an nan za mu ba da’ya’yanmu mata aure gare ku, mu kuma mu aure’ya’yanku mata wa kanmu. Za mu zauna a cikinku mu kuma zama mutane ɗaya da ku.
Då vilje vi gifva eder våra döttrar, och taga oss edra döttrar, och bo när eder, och vara ett folk.
17 Amma in ba za ku yarda a yi muku kaciya ba, za mu ɗauki’yar’uwanmu mu tafi.”
Men hvar I icke viljen lyda oss, och omskära eder, så vilje vi taga våra dotter, och fara vår väg.
18 Sharuɗansu sun gamshi Hamor da ɗansa, Shekem.
Det talet behagade Hemer och hans son väl.
19 Saurayin wanda aka fi girmamawa a cikin dukan gidan mahaifinsa, bai ɓata lokaci a yin abin da suka ce ba, domin ya ji daɗin’yar Yaƙub.
Och den unge mannen fördröjde intet att göra så; förty han hade lust till Jacobs dotter, och han var härlig hållen öfver alla i hans faders huse.
20 Saboda haka Hamor da ɗansa Shekem suka tafi ƙofar birninsu don su yi magana da mutanen garinsu.
Så gingo Hemor och hans son Sichem i stadsporten, och talade med borgarena i stadenom, och sade:
21 Suka ce, “Waɗannan mutane ba su da damuwa, bari su zauna a cikin ƙasarmu, su kuma yi sana’a a ciki; ƙasar tana da isashen fili dominsu. Za mu iya auro’ya’yansu mata, su kuma su auri namu.
Desse män äro fridsamme när oss, och vilja bygga och bo i landena. Så är nu landet vidt begripet; vi vilje taga oss deras döttrar, och gifva dem våra döttrar.
22 Amma mutanen za su yarda su zauna tare da mu kamar mutane ɗaya kawai bisa wannan sharaɗi, cewa a yi wa mazanmu kaciya, kamar yadda su kansu suke.
Men då vilja de vara oss till viljes, så att de bo när oss, och varda ett folk med oss, om vi omskäre allt det som mankön är ibland oss, såsom de omskorne äro.
23 Ashe, shanunsu, dukiyarsu da dukan sauran dabbobinsu, ba za su zama namu ba? Saboda haka mu yarda, za su kuwa zauna a cikinmu.”
Deras boskap och ägodelar, och allt det de hafva, blifver vårt, om vi eljest blifvom dem till viljes, så att de bo när oss.
24 Dukan mazan da suka fito ƙofar birnin suka yarda da Hamor da kuma ɗansa Shekem, aka kuwa yi wa kowane namiji a birnin kaciya.
Och de lydde Hemor och Sichem hans sone, alle de som genom hans stadsport ut och in gingo, och omskoro allt det som mankön var, det som i deras stad ut och in gick.
25 Bayan kwana uku, yayinda dukansu suna cikin zafi mikin kaciya, sai biyu daga cikin’ya’yan Yaƙub maza, Simeyon da Lawi,’yan’uwan Dina, suka ɗauki takubansu suka fāɗa wa birnin ba labari, suka kashe kowane namiji.
Och på tredje dagenom, då det värkte dem, togo de två Jacobs söner, Simeon och Levi, Dinas bröder, hvardera sitt svärd, och gingo dristeliga in i staden, och slogo ihjäl allt det som var mankön.
26 Suka kashe Hamor da ɗansa Shekem da takobi, suka ɗauko Dina daga gidan Shekem suka tafi.
Och slogo också ihjäl Hemor och hans son Sichem med svärds ägg, och togo sina syster Dina utaf Sichems huse, och gingo sin väg.
27 Sa’an nan’ya’yan Yaƙub maza suka bi kan gawawwakin, suka washe arzikin birni saboda an ɓata’yar’uwarsu.
Då kommo Jacobs söner öfver de slagna, och skinnade staden, derföre, att de skämt hade deras syster.
28 Suka kwashe garkunansu na shanu da jakuna, da kuma kome na mutanen a birnin da kuma cikin gonaki.
Och togo deras får, fä, åsnar, och hvad i stadenom och på markene var:
29 Suka kwashe dukan dukiyarsu da dukan matansu da’ya’yansu, suka kwashe kome da yake cikin gidaje.
Och alla deras håfvor; all barn och qvinnor togo de till fångar, och skinnade allt det i husen var.
30 Sai Yaƙub ya ce wa Simeyon da Lawi, “Kun jawo mini wahala ta wurin sa in zama abin ƙi ga Kan’aniyawa da Ferizziyawa, mazaunan wannan ƙasa. Mu kima ne, in kuwa suka haɗa kai gāba da ni, suka fāɗa mini, za su hallaka ni da gidana.”
Och Jacob sade till Simeon och Levi: I hafven åstadkommit, att jag blifver illa känder för alla dessa lands inbyggare, de Cananeer och Phereseer: Och jag är en ringa hop; när de nu församla sig öfver mig, så slå de mig ihjäl, så varder jag om intet gjord med mino huse.
31 Amma’ya’yansa suka amsa, “To, ya dace ke nan da ya yi da’yar’uwarmu kamar karuwa?”
Men de svarade: Skulle de då handla med våra syster, såsom med ene sköko?