< Farawa 34 >

1 To, Dina,’yar da Liyatu ta haifa wa Yaƙub, ta je ta ziyarci matan ƙasar.
A Dina kæi Lijina, koju rodi Jakovu, izaðe da gleda djevojke u onom kraju.
2 Sa’ad da Shekem ɗan Hamor Bahiwiye mai mulkin wurin ya gan ta, sai ya kama ta, ya kwana da ita, ya ɓata ta.
A ugleda je Sihem, sin Emora Evejina, kneza od one zemlje, i uze je i leže s njom i osramoti je.
3 Zuciyarsa kuwa ta damu da son Dina’yar Yaƙub, ya kuwa ƙaunaci yarinyar, ya yi mata magana a hankali.
I prionu srce njegovo za Dinu kæer Jakovljevu, i djevojka mu omilje, i on joj se umiljavaše.
4 Sai Shekem ya ce wa mahaifinsa Hamor, “Ka auro mini wannan yarinya ta zama matata.”
I reèe Sihem Emoru ocu svojemu govoreæi: oženi me ovom djevojkom.
5 Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa an ɓata’yarsa Dina, sai ya yi shiru game da batun sai’ya’yansa maza sun dawo gida, gama’ya’yansa suna a jeji tare da dabbobinsa suna kiwo.
A Jakov èu da je osramotio Dinu kæer njegovu; a sinovi njegovi bijahu u polju sa stokom njegovom, i Jakov oæutje dokle oni ne doðu.
6 Sai Hamor mahaifin Shekem ya je don yă yi magana da Yaƙub.
A Emor otac Sihemov izide k Jakovu da se razgovori s njim.
7 Da’ya’yan Yaƙub maza suka dawo daga jeji sai suka ji labarin. Abin kuwa ya zafe su ƙwarai, don Shekem ya jawo abin kunya wa jama’ar Isra’ila ta wurin kwana da’yar Yaƙub, don bai kamata wannan abu yă faru ba.
A kad doðoše sinovi Jakovljevi iz polja i èuše šta je bilo, žao bi ljudima vrlo i razgnjeviše se veoma, što uèini sramotu Izrailju obležav kæer Jakovljevu, kako ne bi valjalo èiniti.
8 Amma Hamor ya ce musu, “Ɗana Shekem ya sa zuciyarsa a kan’yarku. Ina roƙonku ku ba shi ita yă aura.
Tada im reèe Emor govoreæi: sin moj Sihem srcem prionu za vašu kæer; podajte mu je za ženu.
9 Ku yi auratayya da mu; ku aurar mana da’ya’yanku mata, ku kuma ku auro’ya’yanmu mata wa kanku.
I oprijateljite se s nama; kæeri svoje udajite za nas i kæerima našim ženite se.
10 Za ku iya zauna a cikinmu, ƙasar tana nan a buɗe dominku. Ku yi zama a cikinta, ku yi sana’a, ku kuma sami dukiya.”
Pa živite s nama, i zemlja æe vam biti otvorena; nastanite se i trgujte i držite baštine u njoj.
11 Sai Shekem ya ce wa mahaifin Dina da kuma’yan’uwanta. “Bari in sami tagomashi a idanunku, zan kuwa ba ku duk abin da kuka tambaya.
I reèe Sihem ocu djevojèinu i braæi joj: da naðem milost pred vama, i daæu što mi god kažete.
12 Ku faɗa mini nawa ne dukiyar aure da kuma sadakin da zan kawo bisa ga yadda kuke so, zan kuwa biya duk abin da kuka ce. Ku dai bar ni in aure yarinyar ta zama matata.”
Ištite mi koliko god hoæete uzdarja i dara, ja æu dati što god kažete; samo mi dajte djevojku za ženu.
13 Domin an ɓata’yar’uwansu Dina, sai’ya’yan Yaƙub maza suka amsa a ha’ince yayinda suke wa Shekem da mahaifinsa Hamor magana.
A sinovi Jakovljevi odgovoriše Sihemu i Emoru ocu njegovu prijevarno, jer osramoti Dinu sestru njihovu.
14 Suka ce musu, “Ba za mu iya yin wannan abu ba, ba za mu iya ba da’yar’uwarmu ga mutumin da ba shi da kaciya ba. Wannan zai zama abin kunya ne a gare mu.
I rekoše im: ne možemo to uèiniti ni dati sestre svoje za èovjeka neobrezana, jer je to sramota nama.
15 Za mu yarda da wannan kaɗai ta wannan sharaɗi, cewa za ku zama kamar mu ta wurin yin wa dukan’ya’yanku maza kaciya.
Nego æemo vam uèiniti po volji, ako æete se izjednaèiti s nama i obrezati sve muškinje izmeðu sebe.
16 Sa’an nan za mu ba da’ya’yanmu mata aure gare ku, mu kuma mu aure’ya’yanku mata wa kanmu. Za mu zauna a cikinku mu kuma zama mutane ɗaya da ku.
Onda æemo udavati svoje kæeri za vas i ženiæemo se vašim kæerima, i postaæemo jedan narod.
17 Amma in ba za ku yarda a yi muku kaciya ba, za mu ɗauki’yar’uwanmu mu tafi.”
Ako li ne pristanete da se obrežete, mi æemo uzeti svoju djevojku i otiæi æemo.
18 Sharuɗansu sun gamshi Hamor da ɗansa, Shekem.
I po volji biše rijeèi njihove Emoru i Sihemu sinu Emorovu.
19 Saurayin wanda aka fi girmamawa a cikin dukan gidan mahaifinsa, bai ɓata lokaci a yin abin da suka ce ba, domin ya ji daɗin’yar Yaƙub.
I momak ne oklijevaše uèiniti to; jer mu kæi Jakovljeva omilje veoma; i on bješe najviše poštovan izmeðu svijeh u kuæi oca svojega.
20 Saboda haka Hamor da ɗansa Shekem suka tafi ƙofar birninsu don su yi magana da mutanen garinsu.
I otide Emor i sin mu Sihem na vrata grada svojega, i rekoše graðanima govoreæi:
21 Suka ce, “Waɗannan mutane ba su da damuwa, bari su zauna a cikin ƙasarmu, su kuma yi sana’a a ciki; ƙasar tana da isashen fili dominsu. Za mu iya auro’ya’yansu mata, su kuma su auri namu.
Ovi ljudi hoæe mirno da žive s nama, da se nastane u ovoj zemlji i da trguju po njoj; a evo zemlja je široka i za njih; pa æemo se kæerima njihovijem ženiti i svoje æemo kæeri udavati za njih.
22 Amma mutanen za su yarda su zauna tare da mu kamar mutane ɗaya kawai bisa wannan sharaɗi, cewa a yi wa mazanmu kaciya, kamar yadda su kansu suke.
Ali æe tako pristati da žive s nama i da postanemo jedan narod, ako se sve muškinje meðu nama obreže, kao što su oni obrezani.
23 Ashe, shanunsu, dukiyarsu da dukan sauran dabbobinsu, ba za su zama namu ba? Saboda haka mu yarda, za su kuwa zauna a cikinmu.”
Njihova stoka i njihovo blago i sva goveda njihova neæe li biti naša? složimo se samo s njima, pa æe ostati kod nas.
24 Dukan mazan da suka fito ƙofar birnin suka yarda da Hamor da kuma ɗansa Shekem, aka kuwa yi wa kowane namiji a birnin kaciya.
I koji god izlažahu na vrata grada njegova, svi poslušaše Emora i Sihema sina njegova; i obreza se sve muškinje, svi koji izlažahu na vrata grada njegova.
25 Bayan kwana uku, yayinda dukansu suna cikin zafi mikin kaciya, sai biyu daga cikin’ya’yan Yaƙub maza, Simeyon da Lawi,’yan’uwan Dina, suka ɗauki takubansu suka fāɗa wa birnin ba labari, suka kashe kowane namiji.
A treæi dan kad oni bijahu u bolovima, uzeše dva sina Jakovljeva, Simeun i Levije, braæa Dinina, svaki svoj maè i uðoše slobodno u grad i pobiše sve muškinje.
26 Suka kashe Hamor da ɗansa Shekem da takobi, suka ɗauko Dina daga gidan Shekem suka tafi.
Ubiše i Emora i sina mu Sihema oštrim maèem, i uzevši Dinu iz kuæe Sihemove otidoše.
27 Sa’an nan’ya’yan Yaƙub maza suka bi kan gawawwakin, suka washe arzikin birni saboda an ɓata’yar’uwarsu.
Tada doðoše sinovi Jakovljevi na pobijene, i oplijeniše grad, jer u njemu bi osramoæena sestra njihova.
28 Suka kwashe garkunansu na shanu da jakuna, da kuma kome na mutanen a birnin da kuma cikin gonaki.
I uzeše ovce njihove i goveda njihova i magarce njihove, što god bješe u gradu i što god bješe u polju.
29 Suka kwashe dukan dukiyarsu da dukan matansu da’ya’yansu, suka kwashe kome da yake cikin gidaje.
I sve blago njihovo, i svu djecu i žene njihove pohvataše i odvedoše, i što god bješe u kojoj kuæi.
30 Sai Yaƙub ya ce wa Simeyon da Lawi, “Kun jawo mini wahala ta wurin sa in zama abin ƙi ga Kan’aniyawa da Ferizziyawa, mazaunan wannan ƙasa. Mu kima ne, in kuwa suka haɗa kai gāba da ni, suka fāɗa mini, za su hallaka ni da gidana.”
A Jakov reèe Simeunu i Leviju; smetoste me, i omraziste me narodu ove zemlje, Hananejima i Ferezejima; u mene ima malo ljudi, pa ako se skupe na me, hoæe me ubiti te æu se istrijebiti ja i dom moj.
31 Amma’ya’yansa suka amsa, “To, ya dace ke nan da ya yi da’yar’uwarmu kamar karuwa?”
A oni rekoše: zar sa sestrom našom da rade kao s kurvom?

< Farawa 34 >