< Farawa 34 >

1 To, Dina,’yar da Liyatu ta haifa wa Yaƙub, ta je ta ziyarci matan ƙasar.
Dina the doughter of Lea which she bare vnto Iacob went out to see the doughters of the lande.
2 Sa’ad da Shekem ɗan Hamor Bahiwiye mai mulkin wurin ya gan ta, sai ya kama ta, ya kwana da ita, ya ɓata ta.
And Siche the sonne of Hemor the Heuite lorde of the countre sawe her and toke her and laye with her and forced her:
3 Zuciyarsa kuwa ta damu da son Dina’yar Yaƙub, ya kuwa ƙaunaci yarinyar, ya yi mata magana a hankali.
and his harte laye vnto Dina ye doughter of Iacob. And he loued yt damsell and spake kidly vnto her
4 Sai Shekem ya ce wa mahaifinsa Hamor, “Ka auro mini wannan yarinya ta zama matata.”
and spake vnto his father Hemor saynge gett me this mayde vnto my wyfe.
5 Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa an ɓata’yarsa Dina, sai ya yi shiru game da batun sai’ya’yansa maza sun dawo gida, gama’ya’yansa suna a jeji tare da dabbobinsa suna kiwo.
And Iacob herde that he had defyled Dina his doughter but his sonnes were with the catell in the felde and therfore he helde his peace vntill they were come.
6 Sai Hamor mahaifin Shekem ya je don yă yi magana da Yaƙub.
Then Hemor the father of Sichem went out vnto Iacob to come with him.
7 Da’ya’yan Yaƙub maza suka dawo daga jeji sai suka ji labarin. Abin kuwa ya zafe su ƙwarai, don Shekem ya jawo abin kunya wa jama’ar Isra’ila ta wurin kwana da’yar Yaƙub, don bai kamata wannan abu yă faru ba.
And the sonnes of Iacob came out of the felde as soone as they herde it for it greued them and they were not a litle wrooth because he had wrought folie in Israell in that he had lyen with Iacobs doughter which thinge oughte not to be done.
8 Amma Hamor ya ce musu, “Ɗana Shekem ya sa zuciyarsa a kan’yarku. Ina roƙonku ku ba shi ita yă aura.
And Hemor comened with the sainge? the soule of my sonne Siche logeth for youre doughter geue her him to wyfe
9 Ku yi auratayya da mu; ku aurar mana da’ya’yanku mata, ku kuma ku auro’ya’yanmu mata wa kanku.
and make mariages with vs: geue youre doughters vnto vs ad take oure doughters vnto you
10 Za ku iya zauna a cikinmu, ƙasar tana nan a buɗe dominku. Ku yi zama a cikinta, ku yi sana’a, ku kuma sami dukiya.”
and dwell with vs and the lande shall be at youre pleasure dwell and do youre busynes and haue youre possessions there in.
11 Sai Shekem ya ce wa mahaifin Dina da kuma’yan’uwanta. “Bari in sami tagomashi a idanunku, zan kuwa ba ku duk abin da kuka tambaya.
And Sichem sayde vnto hyr father and hir brethern: let me fynde grace in youre eyes and what soeuer ye apoynte me that will I geue.
12 Ku faɗa mini nawa ne dukiyar aure da kuma sadakin da zan kawo bisa ga yadda kuke so, zan kuwa biya duk abin da kuka ce. Ku dai bar ni in aure yarinyar ta zama matata.”
Axe frely of me both the dowry and gyftes and I will geue acordynge as ye saye vnto me and geue me the damsell to wyfe.
13 Domin an ɓata’yar’uwansu Dina, sai’ya’yan Yaƙub maza suka amsa a ha’ince yayinda suke wa Shekem da mahaifinsa Hamor magana.
Then the sonnes of Iacob answered to Sichem ad Hemor his father deceytefully because he had defyled Dina their syster.
14 Suka ce musu, “Ba za mu iya yin wannan abu ba, ba za mu iya ba da’yar’uwarmu ga mutumin da ba shi da kaciya ba. Wannan zai zama abin kunya ne a gare mu.
And they sayde vnto them we can not do this thinge yt we shulde geue oure syster to one that is vncircumcysed for that were a shame vnto us.
15 Za mu yarda da wannan kaɗai ta wannan sharaɗi, cewa za ku zama kamar mu ta wurin yin wa dukan’ya’yanku maza kaciya.
Only in this will we consent vnto you? Yf ye will be as we be that all the men childern amonge you be circumcysed
16 Sa’an nan za mu ba da’ya’yanmu mata aure gare ku, mu kuma mu aure’ya’yanku mata wa kanmu. Za mu zauna a cikinku mu kuma zama mutane ɗaya da ku.
tha will we geue oure doughter to you and take youres to vs and will dwell with you and be one people.
17 Amma in ba za ku yarda a yi muku kaciya ba, za mu ɗauki’yar’uwanmu mu tafi.”
But and yf ye will not harken vnto vs to be circumcysed than will we take oure doughter and goo oure wayes.
18 Sharuɗansu sun gamshi Hamor da ɗansa, Shekem.
And their wordes pleased Hemor and Sichem his sonne.
19 Saurayin wanda aka fi girmamawa a cikin dukan gidan mahaifinsa, bai ɓata lokaci a yin abin da suka ce ba, domin ya ji daɗin’yar Yaƙub.
And the yonge man deferde not for to do the thinge because he had a lust to Iacobs doughter: he was also most sett by of all that were in his fathers house.
20 Saboda haka Hamor da ɗansa Shekem suka tafi ƙofar birninsu don su yi magana da mutanen garinsu.
Tha Hemor and Sichem went vnto the gate of their cyte and comened with the men of their cyte sayncte.
21 Suka ce, “Waɗannan mutane ba su da damuwa, bari su zauna a cikin ƙasarmu, su kuma yi sana’a a ciki; ƙasar tana da isashen fili dominsu. Za mu iya auro’ya’yansu mata, su kuma su auri namu.
These men ar peasable with us and will dwell in the lade and do their occupatio therin And in the land is rowme ynough for the let us take their doughters to wyues and geue them oures:
22 Amma mutanen za su yarda su zauna tare da mu kamar mutane ɗaya kawai bisa wannan sharaɗi, cewa a yi wa mazanmu kaciya, kamar yadda su kansu suke.
only herin will they consent vnto vs for to dwell with vs and to be one people: yf all the men childern that are amonge vs be circumcysed as they are.
23 Ashe, shanunsu, dukiyarsu da dukan sauran dabbobinsu, ba za su zama namu ba? Saboda haka mu yarda, za su kuwa zauna a cikinmu.”
Their goodes and their substance and all their catell are oures only let vs consente vnto them that they maye dwell with vs.
24 Dukan mazan da suka fito ƙofar birnin suka yarda da Hamor da kuma ɗansa Shekem, aka kuwa yi wa kowane namiji a birnin kaciya.
And vnto Hemor and Sichem his sonneharkened all that went out at the gate of his cyte. And all the men childern were circumcysed what soeuer went out at the gates of his cyte.
25 Bayan kwana uku, yayinda dukansu suna cikin zafi mikin kaciya, sai biyu daga cikin’ya’yan Yaƙub maza, Simeyon da Lawi,’yan’uwan Dina, suka ɗauki takubansu suka fāɗa wa birnin ba labari, suka kashe kowane namiji.
And the third daye when it was paynefull to them ij. of the sonnes of Iacob Simeon and Leui Dinas brethren toke ether of them his swerde and went in to the cyte boldly and slewe all yt was male
26 Suka kashe Hamor da ɗansa Shekem da takobi, suka ɗauko Dina daga gidan Shekem suka tafi.
and slewe also Hemor and Sichem his sonne with the edge of the swerde ad toke Dina their sister out of Sichems house and went their waye.
27 Sa’an nan’ya’yan Yaƙub maza suka bi kan gawawwakin, suka washe arzikin birni saboda an ɓata’yar’uwarsu.
Than came the sonnes of Iacob vpon the deede and spoyled the cyte because they had defyled their sister:
28 Suka kwashe garkunansu na shanu da jakuna, da kuma kome na mutanen a birnin da kuma cikin gonaki.
and toke their shepe oxen asses and what so euer was in the cyte and also in ye feldes
29 Suka kwashe dukan dukiyarsu da dukan matansu da’ya’yansu, suka kwashe kome da yake cikin gidaje.
And all their goodes all their childern and their wyues toke they captyue and made havock of all that was in the houses.
30 Sai Yaƙub ya ce wa Simeyon da Lawi, “Kun jawo mini wahala ta wurin sa in zama abin ƙi ga Kan’aniyawa da Ferizziyawa, mazaunan wannan ƙasa. Mu kima ne, in kuwa suka haɗa kai gāba da ni, suka fāɗa mini, za su hallaka ni da gidana.”
And Iacob sayde to Simeon and Leui: ye haue troubled me ad made me styncke vnto the inhabitatours of the lande both to the Canaanytes and also vnto the Pherezites. And I am fewe in nombre. Wherfore they shall gather them selves together agaynst me and sley me and so shall I and my house be dystroyed.
31 Amma’ya’yansa suka amsa, “To, ya dace ke nan da ya yi da’yar’uwarmu kamar karuwa?”
And they answered: shuld they deall with oure sister as wyth an whoore?

< Farawa 34 >