< Farawa 34 >

1 To, Dina,’yar da Liyatu ta haifa wa Yaƙub, ta je ta ziyarci matan ƙasar.
Vyšla pak Dína, dcera Líe, kterouž porodila Jákobovi, aby se dívala na dcery té země.
2 Sa’ad da Shekem ɗan Hamor Bahiwiye mai mulkin wurin ya gan ta, sai ya kama ta, ya kwana da ita, ya ɓata ta.
Kteroužto uzřev Sichem, syn Emora Hevejského, knížete v krajině té, vzal ji, i ležel s ní, a ponížil jí.
3 Zuciyarsa kuwa ta damu da son Dina’yar Yaƙub, ya kuwa ƙaunaci yarinyar, ya yi mata magana a hankali.
I připojila se duše jeho k Díně, dceři Jákobově; a zamilovav děvečku, mluvil k srdci jejímu.
4 Sai Shekem ya ce wa mahaifinsa Hamor, “Ka auro mini wannan yarinya ta zama matata.”
Mluvil potom Sichem k Emorovi, otci svému, těmito slovy: Vezmi mi děvečku tuto za manželku.
5 Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa an ɓata’yarsa Dina, sai ya yi shiru game da batun sai’ya’yansa maza sun dawo gida, gama’ya’yansa suna a jeji tare da dabbobinsa suna kiwo.
Uslyšev pak Jákob, že poškvrnil Díny dcery jeho, (a synové jeho byli s stádem na poli), mlčel, až oni přišli.
6 Sai Hamor mahaifin Shekem ya je don yă yi magana da Yaƙub.
Tedy vyšel Emor, otec Sichemův, k Jákobovi, aby mluvil s ním o to.
7 Da’ya’yan Yaƙub maza suka dawo daga jeji sai suka ji labarin. Abin kuwa ya zafe su ƙwarai, don Shekem ya jawo abin kunya wa jama’ar Isra’ila ta wurin kwana da’yar Yaƙub, don bai kamata wannan abu yă faru ba.
A v tom synové Jákobovi přišli s pole; a uslyšavše o tom, bolestí naplněni jsou muži ti, a rozhněvali se velmi, proto že hanebnou věc učinil v Izraeli, ležav se dcerou Jákobovou, čehož činiti nenáleželo.
8 Amma Hamor ya ce musu, “Ɗana Shekem ya sa zuciyarsa a kan’yarku. Ina roƙonku ku ba shi ita yă aura.
I mluvil Emor s nimi na tento způsob: Sichem, syn můj, hoří milostí k vaší dceři; prosím, dejte mu ji za manželku.
9 Ku yi auratayya da mu; ku aurar mana da’ya’yanku mata, ku kuma ku auro’ya’yanmu mata wa kanku.
A spřízněte se s námi: Dcery své dávejte nám, a naše dcery pojímejte sobě.
10 Za ku iya zauna a cikinmu, ƙasar tana nan a buɗe dominku. Ku yi zama a cikinta, ku yi sana’a, ku kuma sami dukiya.”
A bydlete s námi, nebo všecka země bude před vámi; osaďte se a obchod veďte v ní, a vládněte jí.
11 Sai Shekem ya ce wa mahaifin Dina da kuma’yan’uwanta. “Bari in sami tagomashi a idanunku, zan kuwa ba ku duk abin da kuka tambaya.
Mluvil i Sichem otci jejímu, a bratřím jejím: Nechť naleznu milost před očima vašima, dám, co mi koli díte.
12 Ku faɗa mini nawa ne dukiyar aure da kuma sadakin da zan kawo bisa ga yadda kuke so, zan kuwa biya duk abin da kuka ce. Ku dai bar ni in aure yarinyar ta zama matata.”
Jmenujte mi věno i dary jak chcete veliké, dám, jak mi koli řeknete; jen mi tu děvečku dejte za manželku.
13 Domin an ɓata’yar’uwansu Dina, sai’ya’yan Yaƙub maza suka amsa a ha’ince yayinda suke wa Shekem da mahaifinsa Hamor magana.
Odpovídajíce pak synové Jákobovi Sichemovi a Emorovi, otci jeho, lstivě mluvili, proto že poškvrnil Díny sestry jich.
14 Suka ce musu, “Ba za mu iya yin wannan abu ba, ba za mu iya ba da’yar’uwarmu ga mutumin da ba shi da kaciya ba. Wannan zai zama abin kunya ne a gare mu.
A řekli jim: Nemůžeme učiniti toho, abychom dali sestru svou za muže neobřezaného; nebo to ohavnost jest u nás.
15 Za mu yarda da wannan kaɗai ta wannan sharaɗi, cewa za ku zama kamar mu ta wurin yin wa dukan’ya’yanku maza kaciya.
Než na tento způsob vám povolíme: Jestliže se chcete srovnati s námi, aby obřezán byl každý z vás pohlaví mužského:
16 Sa’an nan za mu ba da’ya’yanmu mata aure gare ku, mu kuma mu aure’ya’yanku mata wa kanmu. Za mu zauna a cikinku mu kuma zama mutane ɗaya da ku.
Tedy budeme dávati dcery své vám, a dcery vaše bráti sobě; a budeme bydliti s vámi, a budeme lid jeden.
17 Amma in ba za ku yarda a yi muku kaciya ba, za mu ɗauki’yar’uwanmu mu tafi.”
Pakli neuposlechnete nás, abyste se obřezali, vezmeme zase dceru svou a odejdeme.
18 Sharuɗansu sun gamshi Hamor da ɗansa, Shekem.
Tedy líbila se řeč jejich Emorovi i Sichemovi, synu Emorovu.
19 Saurayin wanda aka fi girmamawa a cikin dukan gidan mahaifinsa, bai ɓata lokaci a yin abin da suka ce ba, domin ya ji daɗin’yar Yaƙub.
A nemeškal mládenec učiniti toho; nebo se mu zalíbila dcera Jákobova. A on byl nejvzácnější ze všech v domě otce svého.
20 Saboda haka Hamor da ɗansa Shekem suka tafi ƙofar birninsu don su yi magana da mutanen garinsu.
I přišel Emor a Sichem, syn jeho, k bráně města svého; a mluvili mužům města svého, řkouce:
21 Suka ce, “Waɗannan mutane ba su da damuwa, bari su zauna a cikin ƙasarmu, su kuma yi sana’a a ciki; ƙasar tana da isashen fili dominsu. Za mu iya auro’ya’yansu mata, su kuma su auri namu.
Muži tito pokojně se mají k nám, nechť tedy bydlí v zemi této, a obchod vedou v ní, (nebo země jest dosti široká a prostranná před nimi; ) dcery jejich budeme sobě bráti za manželky, a dcery své budeme dávati jim.
22 Amma mutanen za su yarda su zauna tare da mu kamar mutane ɗaya kawai bisa wannan sharaɗi, cewa a yi wa mazanmu kaciya, kamar yadda su kansu suke.
Než na tento způsob přivolí nám ti muži k tomu, aby bydlili s námi, a abychom byli jeden lid: Jestliže obřezán bude každý pohlaví mužského mezi námi, tak jako oni jsou obřezáni.
23 Ashe, shanunsu, dukiyarsu da dukan sauran dabbobinsu, ba za su zama namu ba? Saboda haka mu yarda, za su kuwa zauna a cikinmu.”
Dobytek jejich a statek jejich, i všecka hovada jejich, zdaliž nebudou naše? Toliko v tom jim povolme, a budou bydliti s námi.
24 Dukan mazan da suka fito ƙofar birnin suka yarda da Hamor da kuma ɗansa Shekem, aka kuwa yi wa kowane namiji a birnin kaciya.
I uposlechli Emora a Sichema, syna jeho, všickni vycházející branou města jeho; a obřezali se všickni pohlaví mužského, což jich koli vycházelo z brány města jeho.
25 Bayan kwana uku, yayinda dukansu suna cikin zafi mikin kaciya, sai biyu daga cikin’ya’yan Yaƙub maza, Simeyon da Lawi,’yan’uwan Dina, suka ɗauki takubansu suka fāɗa wa birnin ba labari, suka kashe kowane namiji.
A toť dne třetího, když oni největší bolest měli, dva synové Jákobovi, Simeon a Léví, bratří Díny, vzav každý z nich meč svůj, vpadli do města směle, a pomordovali všecky pohlaví mužského.
26 Suka kashe Hamor da ɗansa Shekem da takobi, suka ɗauko Dina daga gidan Shekem suka tafi.
Emora také a Sichema, syna jeho, zamordovali mečem, a vzavše Dínu z domu Sichemova, odešli.
27 Sa’an nan’ya’yan Yaƙub maza suka bi kan gawawwakin, suka washe arzikin birni saboda an ɓata’yar’uwarsu.
Potom synové Jákobovi přišedše na zbité, vzebrali město, proto že poškvrnili sestry jejich.
28 Suka kwashe garkunansu na shanu da jakuna, da kuma kome na mutanen a birnin da kuma cikin gonaki.
Stáda jejich, a voly i osly jejich, a což bylo v městě i po poli, pobrali.
29 Suka kwashe dukan dukiyarsu da dukan matansu da’ya’yansu, suka kwashe kome da yake cikin gidaje.
K tomu i všecko jmění jejich, a všecky malé dítky jejich, a ženy jejich zajali, a vybrali, co kde v domích bylo.
30 Sai Yaƙub ya ce wa Simeyon da Lawi, “Kun jawo mini wahala ta wurin sa in zama abin ƙi ga Kan’aniyawa da Ferizziyawa, mazaunan wannan ƙasa. Mu kima ne, in kuwa suka haɗa kai gāba da ni, suka fāɗa mini, za su hallaka ni da gidana.”
Řekl pak Jákob Simeonovi a Léví: Zkormoutili jste mne, a zošklivili jste mne u obyvatelů krajiny této, u Kananejských a Ferezejských, a já jsem s malým počtem lidí. Seberou-li se na mne, zbijí mne, a tak vyhlazen budu já i dům můj.
31 Amma’ya’yansa suka amsa, “To, ya dace ke nan da ya yi da’yar’uwarmu kamar karuwa?”
A oni odpověděli: A což měli jako nevěstky zle užívati sestry naší?

< Farawa 34 >