< Farawa 33 >
1 Yaƙub ya ɗaga ido ke nan, sai ga Isuwa yana zuwa tare da mutanensa ɗari huɗu; saboda haka sai ya rarraba’ya’yan wa Liyatu, Rahila da kuma matan nan biyu masu hidima.
Et Jacob leva les yeux et regarda, et voilà qu'Esaü arrivait, et avec lui quatre cents hommes. Alors il distribua les enfants à Léa et Rachel, et aux deux servantes;
2 Ya sa matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu a gaba, Liyatu da’ya’yanta biye, sa’an nan Rahila da Yusuf a baya.
et il plaça les servantes et leurs enfants en tête et Léa et ses enfants ensuite et Rachel et Joseph à l'arrière.
3 Shi kansa ya sha gabansu, ya rusuna har ƙasa sau bakwai, kafin ya kai kusa da inda ɗan’uwansa Isuwa yake.
Lui-même marchait devant eux, et il s'inclina sept fois contre terre jusqu'à ce qu'il fût près de son frère.
4 Amma Isuwa ya ruga a guje ya sadu da Yaƙub ya rungume shi; ya faɗa a wuyansa ya sumbace shi. Suka kuma yi kuka.
Alors Esaü courut à sa rencontre, et l'étreignit et se jeta à son cou et l'embrassa; et ils pleurèrent.
5 Sa’an nan Isuwa ya ɗaga ido ya ga mata da’ya’ya. Ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan tare da kai?” Yaƙub ya amsa, “Su ne’ya’yan da Allah cikin alheri ya ba bawanka.”
Et levant les yeux il aperçut les femmes et les enfants et il dit: Qui as-tu là? Et il répondit: Les enfants dont Dieu a gratifié ton serviteur.
6 Sai matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu suka matso kusa suka durƙusa.
Alors les servantes s'avancèrent avec leurs enfants et se prosternèrent.
7 Biye da su, Liyatu da’ya’yanta suka zo suka rusuna. A ƙarshe duka, sai Yusuf da Rahila suka zo, su ma suka rusuna.
Et Léa s'avança aussi avec ses enfants et ils se prosternèrent; puis Joseph s'avança et Rachel, et ils se prosternèrent.
8 Isuwa ya yi tambaya, “Me kake nufi da dukan abubuwan nan da na sadu da su ana korarsu?” Sai Yaƙub ya ce, “Don in sami tagomashi a idanunka ne, ranka yă daɗe.”
Et il dit: Que te proposes-tu avec toute cette caravane que j'ai rencontrée? Et il répondit: De trouver grâce aux yeux de mon seigneur.
9 Amma Isuwa ya ce, “Na riga na sami abin da ya ishe ni, ɗan’uwana. Riƙe abin da kake da shi don kanka.”
Et Esaü dit: Je suis dans l'abondance, mon frère! garde ce que tu as!
10 Sai Yaƙub ya ce, “A’a, ina roƙonka, in na sami tagomashi a idanunka, sai ka karɓi wannan kyautai daga gare ni. Gama ganin fuskarka kamar ganin fuskar Allah ne, yanzu da ka karɓe ni da farin ciki.
Et Jacob dit: Mais non! si j'ai pu trouver grâce à tes yeux, tu accepteras mon présent de ma main; c'est pourquoi j'ai regardé ta face comme on regarde la face de Dieu, et tu m'as fait un gracieux accueil.
11 Ina roƙonka ka karɓi kyautar da aka kawo maka, gama Allah ya yi mini alheri kuma ina da kome da nake bukata.” Ganin yadda Yaƙub ya nace, sai Isuwa ya karɓa.
Accepte donc mon présent qui t'a été offert; car Dieu m'a été propice et le tout m'appartient. Et il le pressa, et il accepta.
12 Sa’an nan Isuwa ya ce, “Bari mu tafi, zan yi maka rakiya.”
Et Esaü dit: Partons et mettons-nous en route, et je te précéderai.
13 Amma Yaƙub ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ka san cewa’ya’yan ƙanana ne, dole in lura da tumaki da shanun da suke shayar da jariransu. In aka kore su da gaggawa a rana guda kaɗai, dukan dabbobin za su mutu.
Et Jacob dit: Mon seigneur sait que les enfants sont délicats et que j'ai des brebis et des vaches qui allaitent; et si on leur faisait hâter le pas un seul jour, tout le troupeau périrait.
14 Saboda haka bari ranka yă daɗe yă sha gaban bawansa, ni kuma in tafi a hankali bisa ga saurin abin da ake kora a gabana da kuma saurin’ya’yan, sai na iso wurinka ranka yă daɗe, a Seyir.”
Que mon seigneur prenne l'avance sur son serviteur, et moi je pourrai cheminer à mon aise en suivant le pas des troupeaux qui me précéderont, et le pas des enfants jusqu'à ce que j'arrive chez mon seigneur à Seïr.
15 Sai Isuwa ya ce, “To, bari in bar waɗansu mutanena tare da kai.” Yaƙub ya ce, “Amma me ya sa za ka yi haka? Bari dai in sami tagomashi a idanunka ranka yă daɗe.”
Et Esaü dit: Je te laisserai une escorte des gens qui sont avec moi. Et il répondit: Pourquoi donc? que je trouve seulement grâce aux yeux de mon seigneur!
16 Saboda haka a wannan rana Isuwa ya kama hanyar komawa zuwa Seyir.
Et ce jour-là Esaü prit son chemin vers Séïr.
17 Yaƙub kuwa, ya tafi Sukkot, inda ya gina wuri domin kansa, ya kuma yi bukkoki domin dabbobinsa. Shi ya sa aka kira wurin Sukkot.
Jacob de son côté se transporta à Succoth et il bâtit une maison pour lui, et pour ses troupeaux il fit des huttes; c'est pourquoi on appelle ce lieu du nom de Succoth (huttes).
18 Bayan Yaƙub ya zo daga Faddan Aram, ya iso lafiya a birnin Shekem a Kan’ana, ya kuma kafa sansani a ƙofar birni.
Et Jacob arriva sain et sauf à la ville de Sichem située dans le pays de Canaan, lors de son retour de Mésopotamie, et il campa devant la ville.
19 Ya sayi fili daga’ya’yan Hamor maza, mahaifin Shekem inda ya kafa tentinsa, a bakin azurfa ɗari.
Et il acheta la portion de terrain où il avait dressé sa tente, des fils de Hémor, père de Sichem, pour le prix de cent kesitas.
20 A can ya kafa bagade ya kuma kira shi El Elohe Isra’ila.
Et là il érigea un autel qu'il nomma [Autel] de Dieu, du Dieu d'Israël.