< Farawa 33 >

1 Yaƙub ya ɗaga ido ke nan, sai ga Isuwa yana zuwa tare da mutanensa ɗari huɗu; saboda haka sai ya rarraba’ya’yan wa Liyatu, Rahila da kuma matan nan biyu masu hidima.
Et Jacob leva les yeux et regarda. Et voici, Ésaü venait, et quatre cents hommes avec lui. Alors il répartit les enfants entre Léa, Rachel, et les deux servantes.
2 Ya sa matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu a gaba, Liyatu da’ya’yanta biye, sa’an nan Rahila da Yusuf a baya.
Et il plaça en tête les servantes et leurs enfants; Léa et ses enfants ensuite, et Rachel et Joseph au dernier rang.
3 Shi kansa ya sha gabansu, ya rusuna har ƙasa sau bakwai, kafin ya kai kusa da inda ɗan’uwansa Isuwa yake.
Quant à lui, il passa devant eux, et se prosterna en terre sept fois, jusqu'à ce qu'il se fût approché de son frère.
4 Amma Isuwa ya ruga a guje ya sadu da Yaƙub ya rungume shi; ya faɗa a wuyansa ya sumbace shi. Suka kuma yi kuka.
Mais Ésaü courut au-devant de lui, et l'embrassa, et se jeta à son cou, et le baisa, et ils pleurèrent.
5 Sa’an nan Isuwa ya ɗaga ido ya ga mata da’ya’ya. Ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan tare da kai?” Yaƙub ya amsa, “Su ne’ya’yan da Allah cikin alheri ya ba bawanka.”
Puis il leva les yeux, et vit les femmes et les enfants, et il dit: Qui as-tu là? Et il répondit: Ce sont les enfants que Dieu a accordés à ton serviteur.
6 Sai matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu suka matso kusa suka durƙusa.
Et les servantes s'approchèrent, elles et leurs enfants, et se prosternèrent.
7 Biye da su, Liyatu da’ya’yanta suka zo suka rusuna. A ƙarshe duka, sai Yusuf da Rahila suka zo, su ma suka rusuna.
Léa aussi s'approcha, et ses enfants, et ils se prosternèrent. Et ensuite Joseph et Rachel s'approchèrent, et ils se prosternèrent.
8 Isuwa ya yi tambaya, “Me kake nufi da dukan abubuwan nan da na sadu da su ana korarsu?” Sai Yaƙub ya ce, “Don in sami tagomashi a idanunka ne, ranka yă daɗe.”
Et Ésaü dit: Que veux-tu faire avec tout ce camp que j'ai rencontré? Et il répondit: C'est pour trouver grâce aux yeux de mon seigneur.
9 Amma Isuwa ya ce, “Na riga na sami abin da ya ishe ni, ɗan’uwana. Riƙe abin da kake da shi don kanka.”
Et Ésaü dit: Je suis dans l'abondance, mon frère. Garde ce qui est à toi.
10 Sai Yaƙub ya ce, “A’a, ina roƙonka, in na sami tagomashi a idanunka, sai ka karɓi wannan kyautai daga gare ni. Gama ganin fuskarka kamar ganin fuskar Allah ne, yanzu da ka karɓe ni da farin ciki.
Et Jacob répondit: Non, je te prie, si j'ai trouvé grâce à tes yeux, tu accepteras mon offrande de ma main, puisque j'ai vu ta face comme on voit la face de Dieu, et que tu m'as accueilli favorablement.
11 Ina roƙonka ka karɓi kyautar da aka kawo maka, gama Allah ya yi mini alheri kuma ina da kome da nake bukata.” Ganin yadda Yaƙub ya nace, sai Isuwa ya karɓa.
Accepte, je te prie, mon présent qui t'a été offert; car Dieu m'a comblé de grâces, et j'ai de tout. Il le pressa donc tant, qu'il l'accepta.
12 Sa’an nan Isuwa ya ce, “Bari mu tafi, zan yi maka rakiya.”
Et Ésaü dit: Partons, et marchons; et je marcherai devant toi.
13 Amma Yaƙub ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ka san cewa’ya’yan ƙanana ne, dole in lura da tumaki da shanun da suke shayar da jariransu. In aka kore su da gaggawa a rana guda kaɗai, dukan dabbobin za su mutu.
Et Jacob lui dit: Mon seigneur sait que les enfants sont délicats; et je suis chargé de brebis et de vaches qui allaitent; si on les presse un seul jour, tout le troupeau mourra.
14 Saboda haka bari ranka yă daɗe yă sha gaban bawansa, ni kuma in tafi a hankali bisa ga saurin abin da ake kora a gabana da kuma saurin’ya’yan, sai na iso wurinka ranka yă daɗe, a Seyir.”
Que mon seigneur passe, je te prie, devant son serviteur; et moi, je m'avancerai tout doucement, au pas du bétail qui est devant moi, et au pas des enfants, jusqu'à ce que j'arrive chez mon seigneur, à Séir.
15 Sai Isuwa ya ce, “To, bari in bar waɗansu mutanena tare da kai.” Yaƙub ya ce, “Amma me ya sa za ka yi haka? Bari dai in sami tagomashi a idanunka ranka yă daɗe.”
Et Ésaü dit: Je te prie, que je fasse demeurer avec toi quelques-uns des gens qui sont avec moi. Et il répondit: Pourquoi cela? Que je trouve grâce aux yeux de mon seigneur!
16 Saboda haka a wannan rana Isuwa ya kama hanyar komawa zuwa Seyir.
Et Ésaü retourna ce jour-là par son chemin, à Séir.
17 Yaƙub kuwa, ya tafi Sukkot, inda ya gina wuri domin kansa, ya kuma yi bukkoki domin dabbobinsa. Shi ya sa aka kira wurin Sukkot.
Mais Jacob partit pour Succoth; et il bâtit une maison pour lui, et fit des cabanes pour son bétail; c'est pourquoi, il nomma le lieu Succoth (cabanes).
18 Bayan Yaƙub ya zo daga Faddan Aram, ya iso lafiya a birnin Shekem a Kan’ana, ya kuma kafa sansani a ƙofar birni.
Et Jacob, venant de Paddan-Aram, arriva sain et sauf à la ville de Sichem, au pays de Canaan; et il campa devant la ville.
19 Ya sayi fili daga’ya’yan Hamor maza, mahaifin Shekem inda ya kafa tentinsa, a bakin azurfa ɗari.
Et il acheta, de la main des fils de Hémor, père de Sichem, pour cent pièces d'argent, la portion de champ où il avait dressé sa tente.
20 A can ya kafa bagade ya kuma kira shi El Elohe Isra’ila.
Et il dressa là un autel, et il l'appela El-Elohé-Israël (Dieu est le Dieu d'Israël).

< Farawa 33 >