< Farawa 33 >

1 Yaƙub ya ɗaga ido ke nan, sai ga Isuwa yana zuwa tare da mutanensa ɗari huɗu; saboda haka sai ya rarraba’ya’yan wa Liyatu, Rahila da kuma matan nan biyu masu hidima.
Iacob lyfte vp his eyes and sawe hys brother Esau come and with him. iiij. hundred men. And he deuyded the childern vnto Lea and vnto Rahel and vnto ye ij. maydens.
2 Ya sa matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu a gaba, Liyatu da’ya’yanta biye, sa’an nan Rahila da Yusuf a baya.
And he put the maydens ad their childern formest ad Lea and hir childern after and Rahel ad Ioseph hindermost.
3 Shi kansa ya sha gabansu, ya rusuna har ƙasa sau bakwai, kafin ya kai kusa da inda ɗan’uwansa Isuwa yake.
And he went before them and fell on the grownde, vij. tymes vntill he came vnto his brother.
4 Amma Isuwa ya ruga a guje ya sadu da Yaƙub ya rungume shi; ya faɗa a wuyansa ya sumbace shi. Suka kuma yi kuka.
Esau ranne agaynst him and enbraced hym and fell on his necke and kyssed him and they wepte.
5 Sa’an nan Isuwa ya ɗaga ido ya ga mata da’ya’ya. Ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan tare da kai?” Yaƙub ya amsa, “Su ne’ya’yan da Allah cikin alheri ya ba bawanka.”
And he lifte vp his eyes and sawe the wyves and their childern and sayde: what are these which thou there hast? And he sayde: they are the childern which God hath geuen thy seruaunte.
6 Sai matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu suka matso kusa suka durƙusa.
Than came the maydens forth ad dyd their obaysaunce.
7 Biye da su, Liyatu da’ya’yanta suka zo suka rusuna. A ƙarshe duka, sai Yusuf da Rahila suka zo, su ma suka rusuna.
Lea also and hir childern came and dyd their obaysaunce. And last of all came Ioseph and Rahel and dyd their obaysaunce.
8 Isuwa ya yi tambaya, “Me kake nufi da dukan abubuwan nan da na sadu da su ana korarsu?” Sai Yaƙub ya ce, “Don in sami tagomashi a idanunka ne, ranka yă daɗe.”
And he sayde: what meanyst thou with all ye drooues which I mett. And he answered: to fynde grace in the syghte of my lorde.
9 Amma Isuwa ya ce, “Na riga na sami abin da ya ishe ni, ɗan’uwana. Riƙe abin da kake da shi don kanka.”
And Esau sayde: I haue ynough my brother kepe that thou hast vnto thy silf.
10 Sai Yaƙub ya ce, “A’a, ina roƙonka, in na sami tagomashi a idanunka, sai ka karɓi wannan kyautai daga gare ni. Gama ganin fuskarka kamar ganin fuskar Allah ne, yanzu da ka karɓe ni da farin ciki.
Iacob answered: oh nay but yf I haue founde grace in thy syghte receaue my preaset of my hade: for I haue sene thy face as though I had sene ye face of God: wherfore receaue me to grace
11 Ina roƙonka ka karɓi kyautar da aka kawo maka, gama Allah ya yi mini alheri kuma ina da kome da nake bukata.” Ganin yadda Yaƙub ya nace, sai Isuwa ya karɓa.
and take my blessynge that I haue brought the for God hath geuen it me frely. And I haue ynough of all thynges. And so he compelled him to take it.
12 Sa’an nan Isuwa ya ce, “Bari mu tafi, zan yi maka rakiya.”
And he sayde: let us take oure iourney and goo and I will goo in thy copany.
13 Amma Yaƙub ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ka san cewa’ya’yan ƙanana ne, dole in lura da tumaki da shanun da suke shayar da jariransu. In aka kore su da gaggawa a rana guda kaɗai, dukan dabbobin za su mutu.
And he sayde vnto him: my lorde knoweth that I haue tendre childern ewes and kyne with yonge vnder myne hande which yf men shulde ouerdryue but euen one daye the hole flocke wolde dye.
14 Saboda haka bari ranka yă daɗe yă sha gaban bawansa, ni kuma in tafi a hankali bisa ga saurin abin da ake kora a gabana da kuma saurin’ya’yan, sai na iso wurinka ranka yă daɗe, a Seyir.”
Let my lorde therfore goo before his servaunte and I will dryue fayre and softly accordynge as the catell that goth before me and the childern be able to endure: vntill I come to mi lorde vnto Seir.
15 Sai Isuwa ya ce, “To, bari in bar waɗansu mutanena tare da kai.” Yaƙub ya ce, “Amma me ya sa za ka yi haka? Bari dai in sami tagomashi a idanunka ranka yă daɗe.”
And Esau sayde: let me yet leaue some of my folke with the. And he sayde: what neadeth it? let me fynde grace in the syghte of my lorde
16 Saboda haka a wannan rana Isuwa ya kama hanyar komawa zuwa Seyir.
So Esau went his waye agayne yt same daye vnto Seir.
17 Yaƙub kuwa, ya tafi Sukkot, inda ya gina wuri domin kansa, ya kuma yi bukkoki domin dabbobinsa. Shi ya sa aka kira wurin Sukkot.
And Iacob toke his iourney toward Sucoth and bylt him an house and made boothes for his catell: wherof the name of the place is called Sucoth.
18 Bayan Yaƙub ya zo daga Faddan Aram, ya iso lafiya a birnin Shekem a Kan’ana, ya kuma kafa sansani a ƙofar birni.
And Iacob went to Salem to ye cytie of Sichem in the lande of Canaa after that he was come from Mesopotamia and pitched before the cyte
19 Ya sayi fili daga’ya’yan Hamor maza, mahaifin Shekem inda ya kafa tentinsa, a bakin azurfa ɗari.
and bought a parcell of ground where he pitched his tent of the childern of Hemor Sichems father for an hundred lambes.
20 A can ya kafa bagade ya kuma kira shi El Elohe Isra’ila.
And he made there an aulter and there called vpon the myghtie God of Israell.

< Farawa 33 >