< Farawa 33 >

1 Yaƙub ya ɗaga ido ke nan, sai ga Isuwa yana zuwa tare da mutanensa ɗari huɗu; saboda haka sai ya rarraba’ya’yan wa Liyatu, Rahila da kuma matan nan biyu masu hidima.
[Then Jacob joined the rest of his family]. [Later that day] Jacob looked up and saw Esau coming, and there were 400 men with him. [Jacob was worried because of that], so he separated the children. He put Leah’s children with Leah, Rachel’s children with Rachel, and the two female slaves’ children with their mothers.
2 Ya sa matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu a gaba, Liyatu da’ya’yanta biye, sa’an nan Rahila da Yusuf a baya.
He put the two female slaves and their children in front. He put Leah and her children next. He put Rachel and Joseph at the rear.
3 Shi kansa ya sha gabansu, ya rusuna har ƙasa sau bakwai, kafin ya kai kusa da inda ɗan’uwansa Isuwa yake.
He himself went ahead of them all, and as he continued to approach his older brother, he prostrated himself with his face on the ground seven times.
4 Amma Isuwa ya ruga a guje ya sadu da Yaƙub ya rungume shi; ya faɗa a wuyansa ya sumbace shi. Suka kuma yi kuka.
But Esau ran to Jacob. He hugged him, put his arms around his neck, and kissed him on the cheek. And they both cried.
5 Sa’an nan Isuwa ya ɗaga ido ya ga mata da’ya’ya. Ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan tare da kai?” Yaƙub ya amsa, “Su ne’ya’yan da Allah cikin alheri ya ba bawanka.”
Then Esau looked up and saw the women and the children. He asked, “Who are these people who are with you?” Jacob replied, “These are the wives and children that God has graciously/kindly given to me.”
6 Sai matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu suka matso kusa suka durƙusa.
Then the female slaves and their children came near and bowed in front of Esau.
7 Biye da su, Liyatu da’ya’yanta suka zo suka rusuna. A ƙarshe duka, sai Yusuf da Rahila suka zo, su ma suka rusuna.
Then Leah and her children came and bowed down. Finally Joseph and Rachel came near and bowed down.
8 Isuwa ya yi tambaya, “Me kake nufi da dukan abubuwan nan da na sadu da su ana korarsu?” Sai Yaƙub ya ce, “Don in sami tagomashi a idanunka ne, ranka yă daɗe.”
Esau asked, “What is the meaning of all the animals that I saw?” Jacob replied, “I am giving them to you, sir, so that you will feel good toward me.”
9 Amma Isuwa ya ce, “Na riga na sami abin da ya ishe ni, ɗan’uwana. Riƙe abin da kake da shi don kanka.”
But Esau replied, “My [younger] brother, I have enough animals! Keep for yourself the animals that you have!”
10 Sai Yaƙub ya ce, “A’a, ina roƙonka, in na sami tagomashi a idanunka, sai ka karɓi wannan kyautai daga gare ni. Gama ganin fuskarka kamar ganin fuskar Allah ne, yanzu da ka karɓe ni da farin ciki.
But Jacob said, “No, please, if you feel good toward me, accept these gifts from me. You have greeted me very kindly. Seeing your smiling face assures me [that you have forgiven me]. It is like seeing the face of God!
11 Ina roƙonka ka karɓi kyautar da aka kawo maka, gama Allah ya yi mini alheri kuma ina da kome da nake bukata.” Ganin yadda Yaƙub ya nace, sai Isuwa ya karɓa.
Please accept these gifts that I have brought to you, because God has acted kindly toward me, and I still have plenty of animals!” Jacob kept on urging him to accept the animals, and finally he accepted them.
12 Sa’an nan Isuwa ya ce, “Bari mu tafi, zan yi maka rakiya.”
Then Esau said, “Let’s continue traveling together, and I will show the road to you.”
13 Amma Yaƙub ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ka san cewa’ya’yan ƙanana ne, dole in lura da tumaki da shanun da suke shayar da jariransu. In aka kore su da gaggawa a rana guda kaɗai, dukan dabbobin za su mutu.
Jacob [had no intention to go with Esau], but he said, “You know, sir, that the children are weak, and that I must take care of the female sheep and cows that are (sucking their mother’s milk/nursing their young). If I force them to walk fast for a long distance in just one day, the animals will all die.
14 Saboda haka bari ranka yă daɗe yă sha gaban bawansa, ni kuma in tafi a hankali bisa ga saurin abin da ake kora a gabana da kuma saurin’ya’yan, sai na iso wurinka ranka yă daɗe, a Seyir.”
You go ahead of me. I will lead the animals slowly, but I will walk as fast as the children and animals can walk. I will catch up with you in Seir, [in the land where the descendants of Edom live].”
15 Sai Isuwa ya ce, “To, bari in bar waɗansu mutanena tare da kai.” Yaƙub ya ce, “Amma me ya sa za ka yi haka? Bari dai in sami tagomashi a idanunka ranka yă daɗe.”
Esau said, “Then allow me to leave with you some of the men who came with me, [to protect you].” But Jacob replied, “(Why do that?/There is no need to do that!) [RHQ] The only thing that I want is for you to act friendly toward me.”
16 Saboda haka a wannan rana Isuwa ya kama hanyar komawa zuwa Seyir.
So on that day Esau left to return to Seir.
17 Yaƙub kuwa, ya tafi Sukkot, inda ya gina wuri domin kansa, ya kuma yi bukkoki domin dabbobinsa. Shi ya sa aka kira wurin Sukkot.
But [instead of going to Seir], Jacob and his family went to [a place called] Succoth. There he built a house for himself and his family, and built shelters for his livestock. That is the reason they named the place Succoth, [which means ‘shelters’].
18 Bayan Yaƙub ya zo daga Faddan Aram, ya iso lafiya a birnin Shekem a Kan’ana, ya kuma kafa sansani a ƙofar birni.
[Some time later, ] Jacob and his family left Paddan-Aram [in Mesopotamia], and they traveled safely to the Canaan region. There they set up their tents in a field near Shechem city.
19 Ya sayi fili daga’ya’yan Hamor maza, mahaifin Shekem inda ya kafa tentinsa, a bakin azurfa ɗari.
One of the leaders of the people in that area was named Hamor. Hamor had several sons. Jacob paid the sons of Hamor 100 pieces of silver for the piece of ground on which they set up their tents.
20 A can ya kafa bagade ya kuma kira shi El Elohe Isra’ila.
He built a stone altar there, and named it El-Elohe Israel, [which means ‘God, the God of Israel].’

< Farawa 33 >