< Farawa 33 >

1 Yaƙub ya ɗaga ido ke nan, sai ga Isuwa yana zuwa tare da mutanensa ɗari huɗu; saboda haka sai ya rarraba’ya’yan wa Liyatu, Rahila da kuma matan nan biyu masu hidima.
And he lifted up Jacob eyes his and he saw and there! Esau [was] coming and [were] with him four hundred man and he divided the children with Leah and with Rachel and with [the] two the maidservants.
2 Ya sa matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu a gaba, Liyatu da’ya’yanta biye, sa’an nan Rahila da Yusuf a baya.
And he put the maidservants and children their first and Leah and children her behind and Rachel and Joseph behind.
3 Shi kansa ya sha gabansu, ya rusuna har ƙasa sau bakwai, kafin ya kai kusa da inda ɗan’uwansa Isuwa yake.
And he he passed on before them and he bowed down [the] ground towards seven times until drew near he to brother his.
4 Amma Isuwa ya ruga a guje ya sadu da Yaƙub ya rungume shi; ya faɗa a wuyansa ya sumbace shi. Suka kuma yi kuka.
And he ran Esau to meet him and he embraced him and he fell on (neck his *Q(k)*) and he kissed him and they wept.
5 Sa’an nan Isuwa ya ɗaga ido ya ga mata da’ya’ya. Ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan tare da kai?” Yaƙub ya amsa, “Su ne’ya’yan da Allah cikin alheri ya ba bawanka.”
And he lifted up eyes his and he saw the women and the children and he said who? [are] these to you and he said the children whom he has shown favor to God servant your.
6 Sai matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu suka matso kusa suka durƙusa.
And they approached the maidservants they and children their and they bowed down.
7 Biye da su, Liyatu da’ya’yanta suka zo suka rusuna. A ƙarshe duka, sai Yusuf da Rahila suka zo, su ma suka rusuna.
And she approached also Leah and children her and they bowed down and after he approached Joseph and Rachel and they bowed down.
8 Isuwa ya yi tambaya, “Me kake nufi da dukan abubuwan nan da na sadu da su ana korarsu?” Sai Yaƙub ya ce, “Don in sami tagomashi a idanunka ne, ranka yă daɗe.”
And he said who? to you [is] all the camp this which I have met and he said to find favor in [the] eyes of lord my.
9 Amma Isuwa ya ce, “Na riga na sami abin da ya ishe ni, ɗan’uwana. Riƙe abin da kake da shi don kanka.”
And he said Esau there [belongs] to me much O brother my let it be[long] to you [that] which [belongs] to you.
10 Sai Yaƙub ya ce, “A’a, ina roƙonka, in na sami tagomashi a idanunka, sai ka karɓi wannan kyautai daga gare ni. Gama ganin fuskarka kamar ganin fuskar Allah ne, yanzu da ka karɓe ni da farin ciki.
And he said Jacob may not [it be] please if please I have found favor in view your and you will accept gift my from hand my for since I have seen face your like seeing [the] face of God and you have accepted favorably me.
11 Ina roƙonka ka karɓi kyautar da aka kawo maka, gama Allah ya yi mini alheri kuma ina da kome da nake bukata.” Ganin yadda Yaƙub ya nace, sai Isuwa ya karɓa.
Take please blessing my which it was brought to you for he has shown favor to me God and that there [belongs] to me everything and he urged him and he took [it].
12 Sa’an nan Isuwa ya ce, “Bari mu tafi, zan yi maka rakiya.”
And he said let us set out and let us go and I will go to before you.
13 Amma Yaƙub ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ka san cewa’ya’yan ƙanana ne, dole in lura da tumaki da shanun da suke shayar da jariransu. In aka kore su da gaggawa a rana guda kaɗai, dukan dabbobin za su mutu.
And he said to him lord my [is] knowing that the children [are] weak and the sheep and the cattle [are] nursing with me and people will drive hard them a day one and they will die all the flock.
14 Saboda haka bari ranka yă daɗe yă sha gaban bawansa, ni kuma in tafi a hankali bisa ga saurin abin da ake kora a gabana da kuma saurin’ya’yan, sai na iso wurinka ranka yă daɗe, a Seyir.”
Let him pass on please lord my before servant his and I (I will journey on *LBH(a)*) to gentleness my to [the] foot of the property which [is] before me and to [the] foot of the children until that I will come to lord my Seir towards.
15 Sai Isuwa ya ce, “To, bari in bar waɗansu mutanena tare da kai.” Yaƙub ya ce, “Amma me ya sa za ka yi haka? Bari dai in sami tagomashi a idanunka ranka yă daɗe.”
And he said Esau let me place please with you some of the people which [is] with me and he said why? this let me find favor in [the] eyes of lord my.
16 Saboda haka a wannan rana Isuwa ya kama hanyar komawa zuwa Seyir.
And he returned on the day that Esau to way his Seir towards.
17 Yaƙub kuwa, ya tafi Sukkot, inda ya gina wuri domin kansa, ya kuma yi bukkoki domin dabbobinsa. Shi ya sa aka kira wurin Sukkot.
And Jacob he set out Succoth towards and he built for himself a house and for livestock his he made shelters there-fore he called [the] name of the place Succoth.
18 Bayan Yaƙub ya zo daga Faddan Aram, ya iso lafiya a birnin Shekem a Kan’ana, ya kuma kafa sansani a ƙofar birni.
And he came Jacob safe [the] city of Shechem which [is] in [the] land of Canaan when came he from Paddan Aram and he camped with [the] face of the city.
19 Ya sayi fili daga’ya’yan Hamor maza, mahaifin Shekem inda ya kafa tentinsa, a bakin azurfa ɗari.
And he bought [the] portion of the field where he had pitched there tent his from [the] hand of [the] sons of Hamor [the] father of Shechem for a hundred piece[s] of money.
20 A can ya kafa bagade ya kuma kira shi El Elohe Isra’ila.
And he set up there an altar and he called it El Elohe Israel.

< Farawa 33 >