< Farawa 32 >

1 Yaƙub shi ma ya kama hanyarsa, sai mala’ikun Allah suka sadu da shi.
یعقوب به سفر خود ادامه داد. در بین راه فرشتگان خدا بر او ظاهر شدند.
2 Sa’ad da Yaƙub ya gan su sai ya ce, “Wannan sansanin Allah ne!” Saboda haka ya kira wannan wuri Mahanayim.
یعقوب وقتی آنها را دید، گفت: «این است اردوی خدا.» پس آنجا را مَحَنایِم نامید.
3 Sai Yaƙub ya aiki manzanni su sha gabansa zuwa wurin ɗan’uwansa Isuwa a ƙasar Seyir, a ƙauyen Edom.
آنگاه یعقوب، قاصدانی با این پیام نزد برادر خود عیسو به ادوم، واقع در سرزمین سعیر فرستاد: «بنده‌ات یعقوب تا چندی قبل نزد دایی خود لابان سکونت داشتم.
4 Ya umarce su, “Ga abin da za ku faɗa wa maigidana Isuwa, ‘Bawanka Yaƙub ya ce, na yi zama tare da Laban na kuwa kasance a can sai yanzu.
5 Ina da shanu da jakuna, tumaki da awaki, bayi maza da mata. Yanzu ina aika da wannan saƙo zuwa ga ranka yă daɗe, don in sami tagomashi a idanunka.’”
اکنون گاوها، الاغها، گوسفندها، غلامان و کنیزان فراوانی به دست آورده‌ام. این قاصدان را فرستاده‌ام تا تو را از آمدنم آگاه سازند. ای سَروَرم، امیدوارم مورد لطف تو قرار بگیرم.»
6 Sa’ad da manzannin suka komo wurin Yaƙub, suka ce, “Mun tafi wurin ɗan’uwanka Isuwa, yanzu kuwa yana zuwa ya sadu da kai, da kuma mutum ɗari huɗu tare da shi.”
قاصدان پس از رساندن پیام، نزد یعقوب برگشته، به وی گفتند: «برادرت عیسو را دیدیم و او الان با چهارصد نفر به استقبال تو می‌آید!»
7 Da tsoro mai yawa da kuma damuwa, Yaƙub ya rarraba mutanen da suke tare da shi ƙungiyoyi biyu, haka ma garkunan tumaki da awaki, da garkunan shanu da raƙuma.
یعقوب با شنیدن این خبر بی‌نهایت ترسان و مضطرب شد. او افراد خانوادهٔ خود را با گله‌ها و رمه‌ها و شترها به دو دسته تقسیم کرد
8 Ya yi tunani, “In Isuwa ya zo ya fāɗa wa ƙungiya ɗaya, sai ƙungiya ɗayan da ta ragu ta tsira.”
تا اگر عیسو به یک دسته حمله کند، دستهٔ دیگر بگریزد.
9 Sa’an nan Yaƙub ya yi addu’a, “Ya Allah na mahaifina Ibrahim, Allah na mahaifina Ishaku. Ya Ubangiji kai da ka ce mini, ‘Koma ƙasarka zuwa wurin danginka, zan kuma sa ka yi albarka.’
سپس یعقوب چنین دعا کرد: «ای خدای جدم ابراهیم و خدای پدرم اسحاق، ای خداوندی که به من گفتی به وطن خود نزد خویشاوندانم برگردم و قول دادی که مرا برکت دهی،
10 Ban cancanci dukan alheri da amincin da ka nuna wa bawanka ba. Da sanda kaɗai nake sa’ad da na ƙetare wannan Urdun, amma ga shi yanzu na zama ƙungiyoyi biyu.
من لیاقت این همه لطف و محبتی که به خادمت نموده‌ای ندارم. آن زمان که زادگاه خود را ترک کردم و از رود اردن گذشتم، چیزی جز یک چوبدستی همراه خود نداشتم، ولی اکنون مالک دو گروه هستم!
11 Ka cece ni, ina roƙonka daga hannun ɗan’uwana Isuwa, gama ina tsoro zai zo yă fāɗa mini, yă karkashe mu duka,’ya’ya da iyaye.
خداوندا، التماس می‌کنم مرا از دست برادرم عیسو رهایی دهی، چون از او می‌ترسم. از این می‌ترسم که مبادا او این زنان و کودکان را هلاک کند.
12 Amma ka riga ka faɗa, ‘Tabbatacce zan sa ka yi albarka. Zan kuma sa zuriyarka su zama kamar yashin teku da ba a iya ƙirgawa.’”
به یاد آور که تو قول داده‌ای که مرا برکت دهی و نسل مرا چون شنهای ساحل دریا بی‌شمار گردانی.»
13 Ya kwana a can, daga cikin abin da yake tare da shi kuwa, ya zaɓi kyauta domin ɗan’uwansa Isuwa,
یعقوب شب را در آنجا به سر برد و از آنچه با خود داشت این هدایا را برای تقدیم به برادرش عیسو انتخاب کرد:
14 awaki ɗari biyu da bunsurai ashirin, tumaki ɗari biyu da raguna ashirin,
دویست بز ماده، بیست بز نر، دویست میش، بیست قوچ،
15 raƙuma mata talatin tare da ƙananansu, shanu arba’in da bijimai goma, jakuna mata ashirin da kuma jakuna maza goma.
سی شتر شیرده با بچه‌هایشان، چهل گاو ماده، ده گاو نر، بیست الاغ ماده و ده الاغ نر.
16 Ya sa su a ƙarƙashin kulawar bayinsa, kowane kashin garke ya kasance a ware. Ya ce wa bayinsa, “Ku sha gabana, ku kuma ba da rata tsakanin garke da garke.”
او آنها را دسته‌دسته جدا کرده، به خادمانش سپرد و گفت: «از هم فاصله بگیرید و جلوتر از من حرکت کنید.»
17 Ya umarci wanda yake jagorar ya ce, “Sa’ad da ɗan’uwana Isuwa ya sadu da ku ya kuma yi tambaya, ‘Ku na wane ne, ina za ku, kuma wane ne mai dukan dabbobin nan da suke gabanku?’
به مردانی که دستهٔ اول را رهبری می‌کردند گفت که موقع برخورد با عیسو اگر عیسو از ایشان بپرسد: «کجا می‌روید؟ برای چه کسی کار می‌کنید؟ و این حیوانات مال کیست؟»
18 Sai ku ce, ‘Na bawanka Yaƙub ne. Kyauta ce wa maigidana Isuwa, yana kuma tafe a bayanmu.’”
باید بگویند: «اینها متعلق به بنده‌ات یعقوب می‌باشند و هدایایی است که برای سَروَر خود عیسو فرستاده است. خودش هم پشت سر ما می‌آید.»
19 Yaƙub ya kuma umarci na biyu da na uku da kuma dukan waɗansu da suka bi garkunan, “Sai ku faɗa irin abu guda ga Isuwa sa’ad da kuka sadu da shi.
یعقوب همین دستورها را به افراد دستۀ دوم و سوم و به همۀ کسانی که بدنبال گله‌ها می‌آمدند داده، گفت: «وقتی به عیسو رسیدید، همین سخنان را به او بگویید.
20 Ku kuma tabbata kun ce, ‘Bawanka Yaƙub yana tafe a bayanmu.’” Gama Yaƙub ya yi tunani cewa, “Zan kwantar da ran Isuwa da waɗannan kyautai, kafin mu sadu fuska da fuska, wataƙila yă karɓe shi.”
و نیز بگویید:”بنده‌ات یعقوب نیز پشت سر ما می‌آید.“» یعقوب با خود فکر کرد: «با این هدایایی که جلوتر از خودم می‌فرستم او را نرم خواهم کرد. پس از آن وقتی او را ببینم شاید مرا بپذیرد.»
21 Saboda haka kyautai Yaƙub suka sha gabansa, amma shi kansa ya kwana a sansani.
پس او هدایا را جلوتر فرستاد اما خودش شب را در اردوگاه به سر برد.
22 A wannan dare Yaƙub ya tashi ya ɗauki matansa biyu, da matan nan biyu masu hidima da’ya’yansa goma sha ɗaya ya haye rafin Yabbok.
شبانگاه یعقوب برخاست و دو همسر و کنیزان و یازده پسر و تمام اموال خود را برداشته، به کنار رود اردن آمد و آنها را از گذرگاه یبوق به آن طرف رود فرستاد و خود در همان جا تنها ماند. سپس مردی به سراغ او آمده، تا سپیدهٔ صبح با او کشتی گرفت.
23 Bayan ya sa suka haye rafin, haka ma ya tura dukan mallakarsa zuwa hayen.
24 Saboda haka sai aka bar Yaƙub shi kaɗai. Sai ga wani mutum ya zo ya yi kokawa da shi har wayewar gari.
25 Da mutumin ya ga cewa bai fi ƙarfin Yaƙub ba, sai ya bugi kwarin ƙashin cinyar Yaƙub, sai gaɓar ƙashin cinyarsa ya goce, a sa’ad da yake kokawa da mutumin.
وقتی آن مرد دید که نمی‌تواند بر یعقوب غالب شود، مفصل لگن ران او را محکم گرفت، به طوری که لگن او از جا در رفت.
26 Sa’an nan mutumin ya ce, “Bar ni in tafi, gama gari ya waye.” Amma Yaƙub ya amsa ya ce, “Ba zan bar ka ka tafi ba, sai ka sa mini albarka.”
سپس آن مرد گفت: «بگذار بروم، چون سپیده دمیده است.» اما یعقوب گفت: «تا مرا برکت ندهی نمی‌گذارم از اینجا بروی.»
27 Mutumin ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Yaƙub.”
آن مرد پرسید: «نام تو چیست؟» جواب داد: «یعقوب.»
28 Sai mutumin ya ce, “Sunanka ba zai ƙara zama Yaƙub ba, amma Isra’ila, gama ka yi kokawa da Allah da mutane, ka kuwa yi rinjaye.”
به او گفت: «پس از این نام تو دیگر یعقوب نخواهد بود، بلکه اسرائیل، زیرا نزد خدا و مردم مقاوم بوده و پیروز شده‌ای.»
29 Yaƙub ya ce, “Ina roƙonka, faɗa mini sunanka.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Me ya sa kake tambayata sunana?” Sa’an nan ya albarkace shi.
یعقوب از او پرسید: «نام تو چیست؟» آن مرد گفت: «چرا نام مرا می‌پرسی؟» آنگاه یعقوب را در آنجا برکت داد.
30 Saboda haka Yaƙub ya kira wurin Feniyel, yana cewa, “Domin na ga Allah fuska da fuska, duk da haka aka bar ni da rai.”
یعقوب گفت: «در اینجا من خدا را رو به رو دیدم و با وجود این هنوز زنده هستم.» پس آن مکان را فنی‌ئیل (یعنی «چهرهٔ خدا») نامید.
31 Rana ta yi sama a sa’ad da ya wuce Fenuwel yana kuma ɗingishi saboda ƙashin cinyarsa.
یعقوب هنگام طلوع آفتاب به راه افتاد. او به خاطر صدمه‌ای که به رانش وارد شده بود، می‌لنگید.
32 Wannan ya sa har wa yau Isra’ilawa ba sa cin jijiyar ƙashin cinya wadda take a kwarin ƙashin cinya, domin an taɓa kwarin ƙashin cinyar Yaƙub kusa da jijiyar.
(بنی‌اسرائیل تا به امروز ماهیچهٔ عِرق النِساء را که در ران است نمی‌خورند، زیرا این قسمت از رانِ یعقوب بود که در آن شب صدمه دید.)

< Farawa 32 >