< Farawa 32 >

1 Yaƙub shi ma ya kama hanyarsa, sai mala’ikun Allah suka sadu da shi.
UJakobe wasehamba indlela yakhe, lengilosi zikaNkulunkulu zamhlangabeza.
2 Sa’ad da Yaƙub ya gan su sai ya ce, “Wannan sansanin Allah ne!” Saboda haka ya kira wannan wuri Mahanayim.
UJakobe ezibona wasesithi: Leli libutho likaNkulunkulu. Wayitha ibizo laleyondawo iMahanayimi.
3 Sai Yaƙub ya aiki manzanni su sha gabansa zuwa wurin ɗan’uwansa Isuwa a ƙasar Seyir, a ƙauyen Edom.
UJakobe wasethuma izithunywa phambi kwakhe kuEsawu umnewabo, elizweni iSeyiri, ilizwe lakoEdoma.
4 Ya umarce su, “Ga abin da za ku faɗa wa maigidana Isuwa, ‘Bawanka Yaƙub ya ce, na yi zama tare da Laban na kuwa kasance a can sai yanzu.
Wasezilaya esithi: Likhulume kanje enkosini yami uEsawu lithi: Itsho njalo inceku yakho uJakobe ithi: KoLabani bengihlala njengowezizwe ngalibala kuze kube khathesi;
5 Ina da shanu da jakuna, tumaki da awaki, bayi maza da mata. Yanzu ina aika da wannan saƙo zuwa ga ranka yă daɗe, don in sami tagomashi a idanunka.’”
njalo ngilezinkabi labobabhemi, izimvu lezinceku lezincekukazi; sengithumele ukubika enkosini yami ukuthi ngithole umusa emehlweni akho.
6 Sa’ad da manzannin suka komo wurin Yaƙub, suka ce, “Mun tafi wurin ɗan’uwanka Isuwa, yanzu kuwa yana zuwa ya sadu da kai, da kuma mutum ɗari huɗu tare da shi.”
Izithunywa zasezibuyela kuJakobe zathi: Sifikile kumnewenu, kuEsawu, laye uyeza ukukuhlangabeza lamadoda angamakhulu amane laye.
7 Da tsoro mai yawa da kuma damuwa, Yaƙub ya rarraba mutanen da suke tare da shi ƙungiyoyi biyu, haka ma garkunan tumaki da awaki, da garkunan shanu da raƙuma.
UJakobe wasesesaba kakhulu, wakhathazeka. Wehlukanisa abantu ababelaye lezimvu lezinkomo lamakamela, kwaba ngamaqembu amabili;
8 Ya yi tunani, “In Isuwa ya zo ya fāɗa wa ƙungiya ɗaya, sai ƙungiya ɗayan da ta ragu ta tsira.”
ngoba wathi: Uba uEsawu efika kwelinye iqembu alitshaye, iqembu eliseleyo lizaphepha.
9 Sa’an nan Yaƙub ya yi addu’a, “Ya Allah na mahaifina Ibrahim, Allah na mahaifina Ishaku. Ya Ubangiji kai da ka ce mini, ‘Koma ƙasarka zuwa wurin danginka, zan kuma sa ka yi albarka.’
UJakobe wathi futhi: Nkulunkulu kababa uAbrahama, loNkulunkulu kababa uIsaka, Nkosi owathi kimi: Buyela elizweni lakini lezihlotsheni zakho, njalo ngizakwenzela okuhle;
10 Ban cancanci dukan alheri da amincin da ka nuna wa bawanka ba. Da sanda kaɗai nake sa’ad da na ƙetare wannan Urdun, amma ga shi yanzu na zama ƙungiyoyi biyu.
kangiwufanele wonke umusa lakho konke ukuthembeka okwenzele inceku yakho; ngoba ngilodondolo lwami ngachapha le iJordani, khathesi-ke sengingamaqembu amabili.
11 Ka cece ni, ina roƙonka daga hannun ɗan’uwana Isuwa, gama ina tsoro zai zo yă fāɗa mini, yă karkashe mu duka,’ya’ya da iyaye.
Ake ungophule esandleni somnewethu, esandleni sikaEsawu; ngoba ngiyamesaba, hlezi afike angitshaye, unina phezu kwabantwana.
12 Amma ka riga ka faɗa, ‘Tabbatacce zan sa ka yi albarka. Zan kuma sa zuriyarka su zama kamar yashin teku da ba a iya ƙirgawa.’”
Wena-ke wathi: Ukwenza okuhle ngizakwenzela okuhle, njalo ngizayenza inzalo yakho ibe njengetshebetshebe lolwandle elingelakubalwa ngenxa yobunengi.
13 Ya kwana a can, daga cikin abin da yake tare da shi kuwa, ya zaɓi kyauta domin ɗan’uwansa Isuwa,
Waselala lapho ngalobobusuku; wathatha kulokho okwafika esandleni sakhe, isipho sikaEsawu umfowabo,
14 awaki ɗari biyu da bunsurai ashirin, tumaki ɗari biyu da raguna ashirin,
izibhuzikazi ezingamakhulu amabili lempongo ezingamatshumi amabili, izimvukazi ezingamakhulu amabili lenqama ezingamatshumi amabili,
15 raƙuma mata talatin tare da ƙananansu, shanu arba’in da bijimai goma, jakuna mata ashirin da kuma jakuna maza goma.
amakamela enyisayo angamatshumi amathathu lamathole awo, amankomokazi angamatshumi amane, lamajongosi alitshumi, obabhemikazi abangamatshumi amabili lamathole abobabhemi alitshumi.
16 Ya sa su a ƙarƙashin kulawar bayinsa, kowane kashin garke ya kasance a ware. Ya ce wa bayinsa, “Ku sha gabana, ku kuma ba da rata tsakanin garke da garke.”
Wasezinikela esandleni senceku zakhe umhlambi ngomhlambi wodwa, wathi ezincekwini zakhe: Dlulani phambi kwami, libeke ibanga phakathi komhlambi lomhlambi.
17 Ya umarci wanda yake jagorar ya ce, “Sa’ad da ɗan’uwana Isuwa ya sadu da ku ya kuma yi tambaya, ‘Ku na wane ne, ina za ku, kuma wane ne mai dukan dabbobin nan da suke gabanku?’
Waselaya eyokuqala esithi: Nxa uEsawu umnewethu ehlangana lawe, ekubuza esithi: Ungokabani? Njalo uya ngaphi? Ngezikabani-ke lezi eziphambi kwakho?
18 Sai ku ce, ‘Na bawanka Yaƙub ne. Kyauta ce wa maigidana Isuwa, yana kuma tafe a bayanmu.’”
Ubususithi: Ngezenceku yakho ngezikaJakobe, yisipho esithunyelwa enkosini yami uEsawu; khangela-ke, laye uqobo ungemva kwethu.
19 Yaƙub ya kuma umarci na biyu da na uku da kuma dukan waɗansu da suka bi garkunan, “Sai ku faɗa irin abu guda ga Isuwa sa’ad da kuka sadu da shi.
Waselaya leyesibili leyesithathu labo bonke ababelandela imihlambi esithi: Njengalelilizwi lizakhuluma kuEsawu, lapho limthola;
20 Ku kuma tabbata kun ce, ‘Bawanka Yaƙub yana tafe a bayanmu.’” Gama Yaƙub ya yi tunani cewa, “Zan kwantar da ran Isuwa da waɗannan kyautai, kafin mu sadu fuska da fuska, wataƙila yă karɓe shi.”
lithi futhi: Khangela, inceku yakho uJakobe ingemva kwethu. Ngoba uthe: Ngizathoba ubuso bakhe ngesipho esihamba phambi kwami, langemva kwalokho ngizabona ubuso bakhe; mhlawumbe uzakwemukela ubuso bami.
21 Saboda haka kyautai Yaƙub suka sha gabansa, amma shi kansa ya kwana a sansani.
Lesipho sahamba phambi kwakhe; kodwa yena walala lobobusuku enkambeni.
22 A wannan dare Yaƙub ya tashi ya ɗauki matansa biyu, da matan nan biyu masu hidima da’ya’yansa goma sha ɗaya ya haye rafin Yabbok.
Wasesukuma ngalobobusuku, wathatha omkakhe bobabili lencekukazi ezimbili labantwana bakhe abalitshumi lanye, wachapha izibuko leJaboki.
23 Bayan ya sa suka haye rafin, haka ma ya tura dukan mallakarsa zuwa hayen.
Wabathatha, wabachaphisa isifudlana, wachaphisa lokho ayelakho.
24 Saboda haka sai aka bar Yaƙub shi kaɗai. Sai ga wani mutum ya zo ya yi kokawa da shi har wayewar gari.
UJakobe watshiywa yedwa; njalo indoda yabindana laye kwaze kwaba semadabukakusa.
25 Da mutumin ya ga cewa bai fi ƙarfin Yaƙub ba, sai ya bugi kwarin ƙashin cinyar Yaƙub, sai gaɓar ƙashin cinyarsa ya goce, a sa’ad da yake kokawa da mutumin.
Kodwa isibonile ukuthi kayimehluli, yathinta isikhoxo senyonga yakhe, isikhoxo senyonga kaJakobe saqhuzuka ebindana layo.
26 Sa’an nan mutumin ya ce, “Bar ni in tafi, gama gari ya waye.” Amma Yaƙub ya amsa ya ce, “Ba zan bar ka ka tafi ba, sai ka sa mini albarka.”
Yasisithi: Ngiyekela ngihambe ngoba sekusemadabukakusa. Kodwa wathi: Kangiyikukuyekela uhambe ngaphandle kokuthi ungibusise.
27 Mutumin ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Yaƙub.”
Yasisithi kuye: Ungubani ibizo lakho? Wasesithi: UJakobe.
28 Sai mutumin ya ce, “Sunanka ba zai ƙara zama Yaƙub ba, amma Isra’ila, gama ka yi kokawa da Allah da mutane, ka kuwa yi rinjaye.”
Yasisithi: Ibizo lakho kalisayikuthiwa nguJakobe, kodwa uIsrayeli, ngoba ulwile loNkulunkulu labantu, wanqoba.
29 Yaƙub ya ce, “Ina roƙonka, faɗa mini sunanka.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Me ya sa kake tambayata sunana?” Sa’an nan ya albarkace shi.
UJakobe wasebuza wathi: Ake utsho ibizo lakho. Yasisithi: Kungani ubuza ibizo lami? Yambusisa lapho.
30 Saboda haka Yaƙub ya kira wurin Feniyel, yana cewa, “Domin na ga Allah fuska da fuska, duk da haka aka bar ni da rai.”
UJakobe waseyitha ibizo lendawo iPeniyeli, ngoba ngibonile uNkulunkulu ubuso ngobuso, njalo impilo yami isindisiwe.
31 Rana ta yi sama a sa’ad da ya wuce Fenuwel yana kuma ɗingishi saboda ƙashin cinyarsa.
Njalo ilanga lamphumela esedlula iPenuyeli; wayeqhula enyongeni yakhe.
32 Wannan ya sa har wa yau Isra’ilawa ba sa cin jijiyar ƙashin cinya wadda take a kwarin ƙashin cinya, domin an taɓa kwarin ƙashin cinyar Yaƙub kusa da jijiyar.
Ngakho abantwana bakoIsrayeli kabawudli umsipha womthambo osesikhoxweni senyonga kuze kube lamuhla, ngoba wathinta isikhoxo senyonga kaJakobe esisemsipheni womthambo wenyonga.

< Farawa 32 >