< Farawa 32 >

1 Yaƙub shi ma ya kama hanyarsa, sai mala’ikun Allah suka sadu da shi.
HELE aku la o Iakoba i kona hele ana, a halawai mai la na anela o ke Akua me ia.
2 Sa’ad da Yaƙub ya gan su sai ya ce, “Wannan sansanin Allah ne!” Saboda haka ya kira wannan wuri Mahanayim.
A ike aku la o Iakoba ia lakou, i aku la ia, O ka puali kaua keia o ke Akua: a kapa iho la ia i ka inoa o ia wahi, o I Mahanaima.
3 Sai Yaƙub ya aiki manzanni su sha gabansa zuwa wurin ɗan’uwansa Isuwa a ƙasar Seyir, a ƙauyen Edom.
Hoouna aku la o Iakoba i na elele imua ona io Esau la i kona kaikuaana, ma ka aina o Seira, oia ka aina o Edoma.
4 Ya umarce su, “Ga abin da za ku faɗa wa maigidana Isuwa, ‘Bawanka Yaƙub ya ce, na yi zama tare da Laban na kuwa kasance a can sai yanzu.
Kauoha aku la ia ia lakou, i aku la, Penei ka oukou e olelo aku ai i kuu haku, ia Esau; Ke i mai nei o kau kauwa o Iakoba penei, Ua noho pu au me Labana, ua kali aku no wau ilaila a hiki i neia manawa.
5 Ina da shanu da jakuna, tumaki da awaki, bayi maza da mata. Yanzu ina aika da wannan saƙo zuwa ga ranka yă daɗe, don in sami tagomashi a idanunka.’”
Ia'u no na bipi, na hoki, na holoholona, me na kauwakane a me na kauwawahine; a ua hoouna aku no wau e hai aku i kuu haku, i loaa ia'u ke alohaia imua o kou maka.
6 Sa’ad da manzannin suka komo wurin Yaƙub, suka ce, “Mun tafi wurin ɗan’uwanka Isuwa, yanzu kuwa yana zuwa ya sadu da kai, da kuma mutum ɗari huɗu tare da shi.”
Hoi hou mai la na elele io Iakoba la, i mai la, Hele aku la makou i kou kaikuaana io Esau la; a ke hele mai nei hoi oia e halawai me oe, a me ia na haneri kanaka eha.
7 Da tsoro mai yawa da kuma damuwa, Yaƙub ya rarraba mutanen da suke tare da shi ƙungiyoyi biyu, haka ma garkunan tumaki da awaki, da garkunan shanu da raƙuma.
Alaila, makau nui iho la o Iakoba, a ua pilikia loa: mahele ae la oia i na kanaka me ia, i na holoholona, i na bipi a me na kamelo, elua poe;
8 Ya yi tunani, “In Isuwa ya zo ya fāɗa wa ƙungiya ɗaya, sai ƙungiya ɗayan da ta ragu ta tsira.”
I aku la, Ina e hele mai o Esau, a pepehi mai i kekahi poe, alaila e pakele ka poe i koe.
9 Sa’an nan Yaƙub ya yi addu’a, “Ya Allah na mahaifina Ibrahim, Allah na mahaifina Ishaku. Ya Ubangiji kai da ka ce mini, ‘Koma ƙasarka zuwa wurin danginka, zan kuma sa ka yi albarka.’
I aku la o Iakoba, E ke Akua o kun kupunakane o Aberahama, ke Akua o kuu makuakane o Isaaka, e Iehova, ka mea nana i olelo mai ia'u, E hoi hou aku oe i kou aina, a i kou poe hoahanau, a e lokomaikai aku no au ia oe:
10 Ban cancanci dukan alheri da amincin da ka nuna wa bawanka ba. Da sanda kaɗai nake sa’ad da na ƙetare wannan Urdun, amma ga shi yanzu na zama ƙungiyoyi biyu.
Aole au e pono no na lokomaikai a pau a me ka oiaio a pau au i hoike mai ai, i kau kauwa nei; no ka mea, me kuu kookoo iho i hele mai ai au ma keia kapa o loredane; a ua lilo no wau ano i elua poe.
11 Ka cece ni, ina roƙonka daga hannun ɗan’uwana Isuwa, gama ina tsoro zai zo yă fāɗa mini, yă karkashe mu duka,’ya’ya da iyaye.
Ke pule aku nei au ia oe, e hoopakele ae ae ia'u mai ka lima aku o kuu kaikuaana, mai ka lima o Esau: no ka mea, ke makau nei au ia ia, o hele mai nei oia e pepehi mai ia'u me ka makuwahine a me na kamalii.
12 Amma ka riga ka faɗa, ‘Tabbatacce zan sa ka yi albarka. Zan kuma sa zuriyarka su zama kamar yashin teku da ba a iya ƙirgawa.’”
Ua olelo mai oe, E lokomaikai io no wau ia oe, a e hoonui au i kau poe mamo e like me ke one o ke kai, aole e pau lakou i ka heluia no ka lehulehu.
13 Ya kwana a can, daga cikin abin da yake tare da shi kuwa, ya zaɓi kyauta domin ɗan’uwansa Isuwa,
Moe iho la ia malaila ia po; lalau aku la ia i na mea i loaa i kona lima, i makana na kona kaikuaana, na Esau,
14 awaki ɗari biyu da bunsurai ashirin, tumaki ɗari biyu da raguna ashirin,
I elua haneri kao wahine, me na kao kane he iwakalua; elua haneri hipa wahine, me na hipa kane he iwakalua,
15 raƙuma mata talatin tare da ƙananansu, shanu arba’in da bijimai goma, jakuna mata ashirin da kuma jakuna maza goma.
He kanakolu kamelo waiu, me ka lakou mau keiki; he kanaha bipi wahine, me na bipi kane he umi; he iwakalua hoki wahine a me na hokikeiki he umi.
16 Ya sa su a ƙarƙashin kulawar bayinsa, kowane kashin garke ya kasance a ware. Ya ce wa bayinsa, “Ku sha gabana, ku kuma ba da rata tsakanin garke da garke.”
Haawi aku la oia ia mau mea i ka lima o kana poe kauwa, a kaawale kekahi poe me kahi poe; i aku la ia i kana poe kauwa, E hele e aku oukou mamua o'u, a e hookaawale i kahi poe me kahi poe.
17 Ya umarci wanda yake jagorar ya ce, “Sa’ad da ɗan’uwana Isuwa ya sadu da ku ya kuma yi tambaya, ‘Ku na wane ne, ina za ku, kuma wane ne mai dukan dabbobin nan da suke gabanku?’
Kauoha aku la ia i ka mea i hele mamua, i aku la, A halawai mai ko'u kaikuaana o Esau me oe, a ninau mai ia oe, i ka i ana mai, Nowai oe? Mahea oe e hele nei? Nawai hoi keia poe mamua ou?
18 Sai ku ce, ‘Na bawanka Yaƙub ne. Kyauta ce wa maigidana Isuwa, yana kuma tafe a bayanmu.’”
Alaila, e olelo aku oe, Na kau kauwa, na Iakoba lakou nei, ua hoounaia mai, i makana na ko'u haku na Esau: eia ae hoi oia mahope o makou.
19 Yaƙub ya kuma umarci na biyu da na uku da kuma dukan waɗansu da suka bi garkunan, “Sai ku faɗa irin abu guda ga Isuwa sa’ad da kuka sadu da shi.
Pela hoi oia i kauoha aku ai i ka lua a me ke kolu, a me ka poe a pau i hahai mahope o na pua holoholona, i ka i ana, Pela hoi oukou e olelo aku ai ia Esau, i ka wa e loaa'i ia oukou ia.
20 Ku kuma tabbata kun ce, ‘Bawanka Yaƙub yana tafe a bayanmu.’” Gama Yaƙub ya yi tunani cewa, “Zan kwantar da ran Isuwa da waɗannan kyautai, kafin mu sadu fuska da fuska, wataƙila yă karɓe shi.”
E i aku hoi oukou, Eia ae kau kauwa o Iakoba mahope o makou. No ka mea, i iho la ia, E hoolaulea aku au ia ia i ka makana e hele la mamua o'u, a mahope iho e ike aku au i kona maka; a e maliu mai paha ia ia'u.
21 Saboda haka kyautai Yaƙub suka sha gabansa, amma shi kansa ya kwana a sansani.
Pela i hele aku ai ka makana ma kela kapa imua ona: a moe pu iho la oia ia po me ka huakai.
22 A wannan dare Yaƙub ya tashi ya ɗauki matansa biyu, da matan nan biyu masu hidima da’ya’yansa goma sha ɗaya ya haye rafin Yabbok.
Ala ae la oia ia po, lalau aku la ia i kana mau wahine elua, me kana mau kauwawahine elua, a me kana mau keiki kane he umikumamakahi, a hele aku la ma kahi papau o Iaboka ma kela kapa.
23 Bayan ya sa suka haye rafin, haka ma ya tura dukan mallakarsa zuwa hayen.
Lalau aku la ia ia lakou, hoouna aku la ia lakou ma kela kapa o ke kahawai, a hoouka aku la hoi i kana mau mea a pau.
24 Saboda haka sai aka bar Yaƙub shi kaɗai. Sai ga wani mutum ya zo ya yi kokawa da shi har wayewar gari.
O Iakoba wale no i koe: a hakoko mai la kekahi kanaka me ia, a wehe ae la ke alaula o ke ao.
25 Da mutumin ya ga cewa bai fi ƙarfin Yaƙub ba, sai ya bugi kwarin ƙashin cinyar Yaƙub, sai gaɓar ƙashin cinyarsa ya goce, a sa’ad da yake kokawa da mutumin.
A ike iho la kela, aole ia i lanakila maluna ona, papai mai la ia i ka hena o kona uha, a ua kapeke ae la ka huamoa o ko Iakoba uha, i kona hakoko ana me ia.
26 Sa’an nan mutumin ya ce, “Bar ni in tafi, gama gari ya waye.” Amma Yaƙub ya amsa ya ce, “Ba zan bar ka ka tafi ba, sai ka sa mini albarka.”
I mai la kela, E kuu ae oe ia'u, no ka mea, ke wehe mai la ke alaula. I aku la oia, Aole au e kuu aku ia oe, a hoomaikai mai oe ia'u.
27 Mutumin ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Yaƙub.”
Ninau mai la kela ia ia, Owai kou inoa? I aku la oia, O Iakoba.
28 Sai mutumin ya ce, “Sunanka ba zai ƙara zama Yaƙub ba, amma Isra’ila, gama ka yi kokawa da Allah da mutane, ka kuwa yi rinjaye.”
I mai la kela, Aole e hea hou ia kou inoa, o Iakoba; aka, o Iseraela: no ka mea, he ikaika kou imua o ke Akua; a e lanakila hoi oe maluna o na kanaka.
29 Yaƙub ya ce, “Ina roƙonka, faɗa mini sunanka.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Me ya sa kake tambayata sunana?” Sa’an nan ya albarkace shi.
Ninau aku la o Iakoba, i aku la, Ke noi aku nei au ia oe, e hai mai oe ia'u i kou inoa. I mai la kela, Heaha kau i ninau mai ai i ko'u inoa? A hoomaikai mai la kela ia ia ilaila.
30 Saboda haka Yaƙub ya kira wurin Feniyel, yana cewa, “Domin na ga Allah fuska da fuska, duk da haka aka bar ni da rai.”
Kapa aku la o Iakoba i ka inoa o ia wahi o i Peniela: No ka mea, ua ike iho nei au i ke Akua, he maka no he maka, a ua malamaia kuu ola.
31 Rana ta yi sama a sa’ad da ya wuce Fenuwel yana kuma ɗingishi saboda ƙashin cinyarsa.
Puka mai la ka la maluna ona i kona hele ana ae maluna o Penuela, kapeke ae la oia maluna o kona uha.
32 Wannan ya sa har wa yau Isra’ilawa ba sa cin jijiyar ƙashin cinya wadda take a kwarin ƙashin cinya, domin an taɓa kwarin ƙashin cinyar Yaƙub kusa da jijiyar.
No ia mea, aole e ai na mamo a Iseraela i ke olona i eeke, ka mea ma ka uha, a hiki i keia la: no ka mea, papai mai la kela i ka hena o ko Iakoba uha ma ke olona i eeke.

< Farawa 32 >