< Farawa 32 >

1 Yaƙub shi ma ya kama hanyarsa, sai mala’ikun Allah suka sadu da shi.
As Jacob and his family continued traveling, some angels, whom God sent, met him.
2 Sa’ad da Yaƙub ya gan su sai ya ce, “Wannan sansanin Allah ne!” Saboda haka ya kira wannan wuri Mahanayim.
When Jacob saw them, he said, “This is God’s army camp!” So he named that place Mahanaim, [which means ‘two camps’].
3 Sai Yaƙub ya aiki manzanni su sha gabansa zuwa wurin ɗan’uwansa Isuwa a ƙasar Seyir, a ƙauyen Edom.
Jacob told some of the men to go ahead of him to his older brother Esau, who was living in Seir, the land where the descendants of Edom lived.
4 Ya umarce su, “Ga abin da za ku faɗa wa maigidana Isuwa, ‘Bawanka Yaƙub ya ce, na yi zama tare da Laban na kuwa kasance a can sai yanzu.
He told them, “This is what I want you to say to Esau: 'I, Jacob, want to be your servant and I want you to be my master. I have been living with our uncle Laban, and I have stayed there until now.
5 Ina da shanu da jakuna, tumaki da awaki, bayi maza da mata. Yanzu ina aika da wannan saƙo zuwa ga ranka yă daɗe, don in sami tagomashi a idanunka.’”
I now own many cattle, donkeys, sheep, goats, and male and female slaves. Now I am sending this message to you, sir, hoping that you will (be friendly toward me/treat me kindly) when I arrive.’ “
6 Sa’ad da manzannin suka komo wurin Yaƙub, suka ce, “Mun tafi wurin ɗan’uwanka Isuwa, yanzu kuwa yana zuwa ya sadu da kai, da kuma mutum ɗari huɗu tare da shi.”
The messengers went and gave that message to Esau. When they returned to Jacob, they said, “We went to your older brother Esau. Now he is coming to you, and 400 men are coming with him.”
7 Da tsoro mai yawa da kuma damuwa, Yaƙub ya rarraba mutanen da suke tare da shi ƙungiyoyi biyu, haka ma garkunan tumaki da awaki, da garkunan shanu da raƙuma.
Jacob was very afraid and worried. So he divided the people who were with him into two groups. He also divided the sheep and goats, the cattle, and the camels, into two groups.
8 Ya yi tunani, “In Isuwa ya zo ya fāɗa wa ƙungiya ɗaya, sai ƙungiya ɗayan da ta ragu ta tsira.”
He was thinking, “If Esau and his men come and attack us, perhaps one of the groups will be left and will be able to escape.”
9 Sa’an nan Yaƙub ya yi addu’a, “Ya Allah na mahaifina Ibrahim, Allah na mahaifina Ishaku. Ya Ubangiji kai da ka ce mini, ‘Koma ƙasarka zuwa wurin danginka, zan kuma sa ka yi albarka.’
Then Jacob prayed, “O Yahweh God, whom my grandfather Abraham worshiped and my father Isaac worships, you said to me, ‘Go back to your own land and to your relatives, and I will (cause good things happen to/do good things for) you.’
10 Ban cancanci dukan alheri da amincin da ka nuna wa bawanka ba. Da sanda kaɗai nake sa’ad da na ƙetare wannan Urdun, amma ga shi yanzu na zama ƙungiyoyi biyu.
I am not worthy for you to have been so kind and faithful to me in so many ways, your servant. I had only this walking stick with me when I crossed the Jordan [River on my way to Haran], but now I am so wealthy that there are two large groups of my family and possessions.
11 Ka cece ni, ina roƙonka daga hannun ɗan’uwana Isuwa, gama ina tsoro zai zo yă fāɗa mini, yă karkashe mu duka,’ya’ya da iyaye.
So now I pray that you will rescue me from [MTY] my [older] brother Esau, because I am afraid that he and his men will come and attack and kill me and the children and their mothers.
12 Amma ka riga ka faɗa, ‘Tabbatacce zan sa ka yi albarka. Zan kuma sa zuriyarka su zama kamar yashin teku da ba a iya ƙirgawa.’”
But do not forget that you have said, ‘I will certainly enable you to prosper, and I will cause your descendants to be as numerous as the grains of sand on the seashore, which are so many that no one can count them.’”
13 Ya kwana a can, daga cikin abin da yake tare da shi kuwa, ya zaɓi kyauta domin ɗan’uwansa Isuwa,
Jacob slept there that night. The next morning he selected some animals to give to his brother Esau.
14 awaki ɗari biyu da bunsurai ashirin, tumaki ɗari biyu da raguna ashirin,
He selected 200 female goats and 20 male goats, 200 female sheep and 20 male sheep,
15 raƙuma mata talatin tare da ƙananansu, shanu arba’in da bijimai goma, jakuna mata ashirin da kuma jakuna maza goma.
30 female camels and their offspring, 40 cows and ten bulls, 20 female donkeys and 10 male donkeys.
16 Ya sa su a ƙarƙashin kulawar bayinsa, kowane kashin garke ya kasance a ware. Ya ce wa bayinsa, “Ku sha gabana, ku kuma ba da rata tsakanin garke da garke.”
He divided them into small herds, and put each herd into the care of one of his servants. He said to his servants, “Go ahead of me, one group at a time, and keep some space between each herd.”
17 Ya umarci wanda yake jagorar ya ce, “Sa’ad da ɗan’uwana Isuwa ya sadu da ku ya kuma yi tambaya, ‘Ku na wane ne, ina za ku, kuma wane ne mai dukan dabbobin nan da suke gabanku?’
He said to the servant who was going with the first group, “When my brother Esau meets you, and he asks you, ‘To whom do you belong, and where are you going, and to whom do these animals in front of you belong?’
18 Sai ku ce, ‘Na bawanka Yaƙub ne. Kyauta ce wa maigidana Isuwa, yana kuma tafe a bayanmu.’”
tell him, ‘They belong to your servant Jacob. He has sent them to you as a gift, sir. And he is coming behind us.’”
19 Yaƙub ya kuma umarci na biyu da na uku da kuma dukan waɗansu da suka bi garkunan, “Sai ku faɗa irin abu guda ga Isuwa sa’ad da kuka sadu da shi.
He also said the same thing to the servants who were taking care of the second and third groups, and to the other herdsmen. He said to them, “When you meet Esau, I want you to say to him the same thing that I told the first servant.
20 Ku kuma tabbata kun ce, ‘Bawanka Yaƙub yana tafe a bayanmu.’” Gama Yaƙub ya yi tunani cewa, “Zan kwantar da ran Isuwa da waɗannan kyautai, kafin mu sadu fuska da fuska, wataƙila yă karɓe shi.”
And be sure to say ‘Jacob, who wants to serve you, is coming behind us.’” Jacob told them to say that because he was thinking, “Perhaps these gifts that I am sending ahead of me will cause him to (act peacefully toward/stop being angry with) me. Then later, when I see him, perhaps he will be kind to me.”
21 Saboda haka kyautai Yaƙub suka sha gabansa, amma shi kansa ya kwana a sansani.
So the men taking the gifts [PRS] went ahead, but Jacob himself stayed in the camp that night.
22 A wannan dare Yaƙub ya tashi ya ɗauki matansa biyu, da matan nan biyu masu hidima da’ya’yansa goma sha ɗaya ya haye rafin Yabbok.
Some time during that night, Jacob got up and took his two wives, his two female slaves, and his eleven sons and his daughter, and he sent them across the ford at the Jabbok River.
23 Bayan ya sa suka haye rafin, haka ma ya tura dukan mallakarsa zuwa hayen.
After he had done that, he sent other slaves, carrying all his possessions, across the river.
24 Saboda haka sai aka bar Yaƙub shi kaɗai. Sai ga wani mutum ya zo ya yi kokawa da shi har wayewar gari.
So Jacob was left there alone. But a man came and wrestled with him until dawn.
25 Da mutumin ya ga cewa bai fi ƙarfin Yaƙub ba, sai ya bugi kwarin ƙashin cinyar Yaƙub, sai gaɓar ƙashin cinyarsa ya goce, a sa’ad da yake kokawa da mutumin.
When the man realized that he was not winning against Jacob, he struck Jacob’s hip and caused the thigh bone to pull away from the hip socket.
26 Sa’an nan mutumin ya ce, “Bar ni in tafi, gama gari ya waye.” Amma Yaƙub ya amsa ya ce, “Ba zan bar ka ka tafi ba, sai ka sa mini albarka.”
Then the man said, “Let me go, because it will soon be daylight.” [Then Jacob realized who he was really wrestling with]. So he replied, “No, if you will not bless me, I will not let you go!”
27 Mutumin ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Yaƙub.”
The man said to him, “What is your name?” He replied, “Jacob.”
28 Sai mutumin ya ce, “Sunanka ba zai ƙara zama Yaƙub ba, amma Isra’ila, gama ka yi kokawa da Allah da mutane, ka kuwa yi rinjaye.”
The man said, “Your name will no longer be Jacob. Your name will be Israel, [which means ‘he struggles with God’, ] because you have struggled with God and with people, and you have won.”
29 Yaƙub ya ce, “Ina roƙonka, faɗa mini sunanka.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Me ya sa kake tambayata sunana?” Sa’an nan ya albarkace shi.
Jacob said, “Now, please tell me your name!” The man replied, “(Why do you ask me what my name is?/You should not have to ask me what my name is!)” [RHQ] But he blessed Jacob there.
30 Saboda haka Yaƙub ya kira wurin Feniyel, yana cewa, “Domin na ga Allah fuska da fuska, duk da haka aka bar ni da rai.”
So Jacob named the place Peniel, [which means ‘God’s face’, ] saying “I looked directly at God, but I did not die because of doing that.”
31 Rana ta yi sama a sa’ad da ya wuce Fenuwel yana kuma ɗingishi saboda ƙashin cinyarsa.
The sun was rising as Jacob left Peniel, and he was limping because of what had happened to his hip.
32 Wannan ya sa har wa yau Isra’ilawa ba sa cin jijiyar ƙashin cinya wadda take a kwarin ƙashin cinya, domin an taɓa kwarin ƙashin cinyar Yaƙub kusa da jijiyar.
The muscle on his hip joint had been injured. So to this present time, because of what happened to Jacob, the Israeli people do not eat the muscle/tendon that is attached to the socket of the hips of animals.

< Farawa 32 >