< Farawa 32 >
1 Yaƙub shi ma ya kama hanyarsa, sai mala’ikun Allah suka sadu da shi.
Jakobo nodhi nyime gi wuodhe, kendo malaike mag Nyasaye noromo kode.
2 Sa’ad da Yaƙub ya gan su sai ya ce, “Wannan sansanin Allah ne!” Saboda haka ya kira wannan wuri Mahanayim.
Kane Jakobo onenogi, nowacho niya, “Ma en kambi mar Nyasaye!” Kuom mano nochako kanyo ni Mahanaim (tiende ni kembni ariyo).
3 Sai Yaƙub ya aiki manzanni su sha gabansa zuwa wurin ɗan’uwansa Isuwa a ƙasar Seyir, a ƙauyen Edom.
Jakobo nooro joote nyime ir owadgi Esau e piny Seir, gwengʼ mar Edom.
4 Ya umarce su, “Ga abin da za ku faɗa wa maigidana Isuwa, ‘Bawanka Yaƙub ya ce, na yi zama tare da Laban na kuwa kasance a can sai yanzu.
Jakobo nomiyogi chik niya, “Ma e gima onego udhi uwach ne ruodha Esau: Misumbani Jakobo wacho ni, ‘Asebedo ka adak gi Laban kendo asebedo kuno nyaka chil kawuono.
5 Ina da shanu da jakuna, tumaki da awaki, bayi maza da mata. Yanzu ina aika da wannan saƙo zuwa ga ranka yă daɗe, don in sami tagomashi a idanunka.’”
An kod dhok kod punde, rombe gi diek, jotich machwo kod jotich mamon. Omiyo koro aoro oteni ne ruodha, mondo ayud ngʼwono e wangʼe.’”
6 Sa’ad da manzannin suka komo wurin Yaƙub, suka ce, “Mun tafi wurin ɗan’uwanka Isuwa, yanzu kuwa yana zuwa ya sadu da kai, da kuma mutum ɗari huɗu tare da shi.”
Kane jootego odwogo ir Jakobo negiwachone niya, “Ne wadhi ir owadu Esau kendo koro obiro mondo orom kodi, to ji mia angʼwen bende ni kode.”
7 Da tsoro mai yawa da kuma damuwa, Yaƙub ya rarraba mutanen da suke tare da shi ƙungiyoyi biyu, haka ma garkunan tumaki da awaki, da garkunan shanu da raƙuma.
Kane Jakobo owinjo mano luoro kod kibaji nogoye mangʼeny mi nopogo jambe, gi dhoge kod ngamia e migepe ariyo.
8 Ya yi tunani, “In Isuwa ya zo ya fāɗa wa ƙungiya ɗaya, sai ƙungiya ɗayan da ta ragu ta tsira.”
Noparo e chunye niya, “Ka Esau omonjo migawo achiel, to migawo machielo modongʼ nyalo tony.”
9 Sa’an nan Yaƙub ya yi addu’a, “Ya Allah na mahaifina Ibrahim, Allah na mahaifina Ishaku. Ya Ubangiji kai da ka ce mini, ‘Koma ƙasarka zuwa wurin danginka, zan kuma sa ka yi albarka.’
Eka Jakobo nolamo kawacho niya, “Yaye Nyasach kwara Ibrahim, Nyasach wuora Isaka, Jehova Nyasaye mane owachona ni, ‘Dogi thuru ir jou, kendo abiro miyo inyaa,’
10 Ban cancanci dukan alheri da amincin da ka nuna wa bawanka ba. Da sanda kaɗai nake sa’ad da na ƙetare wannan Urdun, amma ga shi yanzu na zama ƙungiyoyi biyu.
ok awinjora gi kech kod adieragi duto misenyiso jatichni. Ne an mana gi ludha kende kane angʼado aora Jordan, to koro aseduogo gi ogendini ariyo.
11 Ka cece ni, ina roƙonka daga hannun ɗan’uwana Isuwa, gama ina tsoro zai zo yă fāɗa mini, yă karkashe mu duka,’ya’ya da iyaye.
Alamo ni mondo iresa e lwet owadwa Esau nikech aluor ni obiro biro ma omonja kaachiel gi mon kod nyithindgi.
12 Amma ka riga ka faɗa, ‘Tabbatacce zan sa ka yi albarka. Zan kuma sa zuriyarka su zama kamar yashin teku da ba a iya ƙirgawa.’”
To isewachona ni, ‘Adier abiro miyo inyaa kendo abiro miyo nyikwayi bedo mathoth ka kuoyo man e dho nam, ma ok nyal kwan.’”
13 Ya kwana a can, daga cikin abin da yake tare da shi kuwa, ya zaɓi kyauta domin ɗan’uwansa Isuwa,
Jakobo nonindo kanyo, kendo kuom gik mane en-go ne oyiero mich ne owadgi Esau kaka:
14 awaki ɗari biyu da bunsurai ashirin, tumaki ɗari biyu da raguna ashirin,
Diek mamon mia ariyo kod nywogi piero ariyo, rombe mamon mia ariyo gi imbe piero ariyo,
15 raƙuma mata talatin tare da ƙananansu, shanu arba’in da bijimai goma, jakuna mata ashirin da kuma jakuna maza goma.
ngamia mamon piero adek gi nyithindgi, dhok mamon piero angʼwen kod rwedhi apar, kod punde mamon piero ariyo kod punde machwo apar.
16 Ya sa su a ƙarƙashin kulawar bayinsa, kowane kashin garke ya kasance a ware. Ya ce wa bayinsa, “Ku sha gabana, ku kuma ba da rata tsakanin garke da garke.”
Noketogi e lwet jotichne ka moro ka moro otelone kweth ka kweth kendo nowachonegi niya, “Teluru nyima kuweyo thuolo e kind kweth ka kweth.”
17 Ya umarci wanda yake jagorar ya ce, “Sa’ad da ɗan’uwana Isuwa ya sadu da ku ya kuma yi tambaya, ‘Ku na wane ne, ina za ku, kuma wane ne mai dukan dabbobin nan da suke gabanku?’
Nomiyo ngʼat mane otelo chik niya, “Ka owadwa Esau oromo kodi mopenji ni, ‘In jatich ngʼa, to idhi kanye kendo ni jamni duto misembogi gin mag ngʼa?’
18 Sai ku ce, ‘Na bawanka Yaƙub ne. Kyauta ce wa maigidana Isuwa, yana kuma tafe a bayanmu.’”
Eka iwachne ni, ‘Magi gin mag jatichni Jakobo. Gin mich ma oor ne ruodha Esau, Jakobo bende biro bangʼwa.’”
19 Yaƙub ya kuma umarci na biyu da na uku da kuma dukan waɗansu da suka bi garkunan, “Sai ku faɗa irin abu guda ga Isuwa sa’ad da kuka sadu da shi.
Bende nomiyo ngʼat mar ariyo, gi ngʼat mar adek kod jogo duto mane luwo bangʼ kweth chik niya, “Un duto wachuru ne Esau mana gima chalre kuromo kode.
20 Ku kuma tabbata kun ce, ‘Bawanka Yaƙub yana tafe a bayanmu.’” Gama Yaƙub ya yi tunani cewa, “Zan kwantar da ran Isuwa da waɗannan kyautai, kafin mu sadu fuska da fuska, wataƙila yă karɓe shi.”
Kendo une ni uwacho ni, ‘Jatichni Jakobo biro bangʼwa.’” Nikech noparo niya, “Obiro hoye gi mich ma ooroneni kendo ka oneno to ponono obiro rwaka.”
21 Saboda haka kyautai Yaƙub suka sha gabansa, amma shi kansa ya kwana a sansani.
Kuom mano mich Jakobo noter motelo, ka en to nodongʼ ei kambi.
22 A wannan dare Yaƙub ya tashi ya ɗauki matansa biyu, da matan nan biyu masu hidima da’ya’yansa goma sha ɗaya ya haye rafin Yabbok.
Otienono Jakobo nochungʼ mokawo monde ariyo, jotichne mamon ariyo kod yawuote apar gachiel kendo negikadho aora mar Jabok.
23 Bayan ya sa suka haye rafin, haka ma ya tura dukan mallakarsa zuwa hayen.
Jakobo nokawo joge kaachiel gi gige mi nokowogi nyaka loka aora Jabok.
24 Saboda haka sai aka bar Yaƙub shi kaɗai. Sai ga wani mutum ya zo ya yi kokawa da shi har wayewar gari.
Bangʼ mano Jakobo nodongʼ kende, kendo ngʼato noi kode otieno duto nyaka okinyi.
25 Da mutumin ya ga cewa bai fi ƙarfin Yaƙub ba, sai ya bugi kwarin ƙashin cinyar Yaƙub, sai gaɓar ƙashin cinyarsa ya goce, a sa’ad da yake kokawa da mutumin.
Kane ngʼatno oneno ni ok onyal goye piny, nomulo fuoni mar bamne, kuom mano chieke nowil.
26 Sa’an nan mutumin ya ce, “Bar ni in tafi, gama gari ya waye.” Amma Yaƙub ya amsa ya ce, “Ba zan bar ka ka tafi ba, sai ka sa mini albarka.”
Ngʼatno nowacho niya, “We adhi, nikech en odiechiengʼ.” To Jakobo nodwoke niya, “Ok abi weyi idhi nyaka igwedha.”
27 Mutumin ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Yaƙub.”
Ngʼatno nopenje niya, “Nyingi ngʼa?” Nodwoke niya, “Jakobo.”
28 Sai mutumin ya ce, “Sunanka ba zai ƙara zama Yaƙub ba, amma Isra’ila, gama ka yi kokawa da Allah da mutane, ka kuwa yi rinjaye.”
Eka ngʼatno nowacho niya, “Nyingi ok nochak oluongi ni Jakobo, to noluongi ni Israel nikech ise ii gi Nyasaye kod ji mi iseloyo.”
29 Yaƙub ya ce, “Ina roƙonka, faɗa mini sunanka.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Me ya sa kake tambayata sunana?” Sa’an nan ya albarkace shi.
Jakobo nowachone niya, “Asayi nyisa nyingi.” To nodwoko Jakobo niya, “Angʼo momiyo ipenjo nyinga?” Eka nogwedho Jakobo kanyo.
30 Saboda haka Yaƙub ya kira wurin Feniyel, yana cewa, “Domin na ga Allah fuska da fuska, duk da haka aka bar ni da rai.”
Kuom mano Jakobo nochako kanyo ni Peniel (tiende ni wangʼ Nyasaye) kowacho niya, “Nikech aseneno Nyasaye wangʼ gi wangʼ kendo ngimana oresi.”
31 Rana ta yi sama a sa’ad da ya wuce Fenuwel yana kuma ɗingishi saboda ƙashin cinyarsa.
Chiengʼ notuchne ka okadho Peniel kendo nowuotho kolingʼo nikech bamne nowil.
32 Wannan ya sa har wa yau Isra’ilawa ba sa cin jijiyar ƙashin cinya wadda take a kwarin ƙashin cinya, domin an taɓa kwarin ƙashin cinyar Yaƙub kusa da jijiyar.
Mano emomiyo nyaka kawuono jo-Israel ok cham ringʼo moriwo fuond bam ka giparogo wil mar fuond bam Jakobo.