< Farawa 31 >

1 Yaƙub ya ji cewa’ya’ya Laban mazan suna cewa, “Yaƙub ya kwashe dukan abin da mahaifinmu yake da shi, ya kuma sami dukan wannan arziki daga abin da yake na mahaifinmu.”
و سخنان پسران لابان را شنید که می گفتند: «یعقوب همه مایملک پدر مارا گرفته است، و از اموال پدر ما تمام این بزرگی رابهم رسانیده.»۱
2 Yaƙub kuma ya lura cewa halin Laban gare shi ya canja ba kamar yadda yake a dā ba.
و یعقوب روی لابان را دید که اینک مثل سابق با او نبود.۲
3 Sai Ubangiji ya ce wa Yaƙub, “Koma ƙasar kakanninka da kuma danginka, zan kuwa kasance tare da kai.”
و خداوند به یعقوب گفت: «به زمین پدرانت و به مولد خویش مراجعت کن و من با تو خواهم بود.»۳
4 Saboda haka Yaƙub ya aika a ce wa Rahila da Liyatu su zo jeji inda garkunan suke.
پس یعقوب فرستاده، راحیل و لیه را به صحرا نزد گله خودطلب نمود.۴
5 Sai ya ce musu, “Na ga cewa halin mahaifinku gare ni ba kamar yadda dā yake ba, amma Allah na mahaifina yana tare da ni.
و بدیشان گفت: «روی پدر شما رامی بینم که مثل سابق با من نیست، لیکن خدای پدرم با من بوده است.۵
6 Kun san cewa na yi aiki wa mahaifinku da dukan ƙarfina,
و شما می‌دانید که به تمام قوت خود پدر شما را خدمت کرده‌ام.۶
7 duk da haka mahaifinku ya cuce ni ta wurin sauya albashina sau goma. Amma dai, Allah bai yardar masa yă yi mini lahani ba.
و پدرشما مرا فریب داده، ده مرتبه اجرت مرا تبدیل نمود ولی خدا او را نگذاشت که ضرری به من رساند.۷
8 In ya ce, ‘Dabbare-dabbare ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi dabbare-dabbare, in kuma ya ce, ‘Masu zāne-zāne ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi ƙananan masu zāne-zāne.
هر گاه می‌گفت اجرت تو پیسه‌ها باشد، تمام گله‌ها پیسه می‌آوردند، و هر گاه گفتی اجرت تو مخطط باشد، همه گله‌ها مخطط می‌زاییدند.۸
9 Ta haka Allah ya kwashe dabbobin mahaifinku ya ba ni.
پس خدا اموال پدر شما را گرفته، به من داده است.»۹
10 “A lokacin ɗaukar cikin garken, na taɓa yin mafarki inda na ga bunsuran da suke barbara da garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne.
و واقع شد هنگامی که گله‌ها حمل می‌گرفتند که در خوابی چشم خود را باز کرده، دیدم اینک قوچهایی که با میشها جمع می‌شدند، مخطط و پیسه و ابلق بودند.۱۰
11 Sai mala’ikan Allah ya ce mini a mafarkin, ‘Yaƙub.’ Sai na amsa na ce, ‘Ga ni.’
و فرشته خدا درخواب به من گفت: «ای یعقوب!» گفتم: «لبیک.»۱۱
12 Ya ce, ‘Ɗaga idanunka ka gani, dukan bunsuran da suke hawan garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne, gama na ga dukan abin da Laban yake yin maka.
گفت: «اکنون چشمان خود را باز کن و بنگر که همه قوچهایی که با میشها جمع می‌شوند، مخططو پیسه و ابلق هستند زیرا که آنچه لابان به تو کرده است، دیده‌ام.۱۲
13 Ni ne Allah na Betel, inda ka zuba wa al’amudi mai, da kuma inda ka yi mini alkawari. Yanzu ka bar wannan ƙasa nan take, ka koma ƙasarka ta ainihi.’”
من هستم خدای بیت ئیل، جایی که ستون را مسح کردی و با من نذر نمودی. الان برخاسته، از این زمین روانه شده، به زمین مولد خویش مراجعت نما.»۱۳
14 Sai Rahila da Liyatu suka amsa suka ce, “Muna da wani rabo a gādon kayan mahaifinmu ne?
راحیل و لیه در جواب وی گفتند: «آیا در خانه پدر ما، برای ما بهره یامیراثی باقیست؟۱۴
15 Ba kamar baƙi ne yake ɗaukarmu ba? Ba sayar da mu kaɗai ya yi ba, har ma ya yi amfani da abin da aka biya saboda mu.
مگر نزد او چون بیگانگان محسوب نیستیم، زیرا که ما را فروخته است و نقدما را تمام خورده.۱۵
16 Tabbatacce dukan dukiyar da Allah ya kwashe daga mahaifinmu ya zama namu da’ya’yanmu. Saboda haka ka yi duk abin da Allah ya faɗa maka.”
زیرا تمام دولتی را که خدااز پدر ما گرفته است، از آن ما و فرزندان ماست، پس اکنون آنچه خدا به تو گفته است، بجا آور.»۱۶
17 Sa’an nan Yaƙub ya sa’ya’yansa da matansa a kan raƙuma,
آنگاه یعقوب برخاسته، فرزندان و زنان خود را بر شتران سوار کرد،۱۷
18 ya kuma kora dukan dabbobinsa, suka ja gabansa, tare da dukan abubuwan da ya samu a Faddan Aram, don su tafi wurin mahaifinsa Ishaku a ƙasar Kan’ana.
و تمام مواشی واموال خود را که اندوخته بود، یعنی مواشی حاصله خود را که در فدان ارام حاصل ساخته بود، برداشت تا نزد پدر خود اسحاق به زمین کنعان برود.۱۸
19 Sa’ad da Laban ya tafi don askin tumakinsa, sai Rahila ta sace gumakan gidan mahaifinta.
و اما لابان برای پشم بریدن گله خود رفته بود و راحیل، بتهای پدر خود را دزدید.۱۹
20 Yaƙub kuwa ya ruɗe Laban mutumin Aram da bai sanar da shi zai gudu ba.
و یعقوب لابان ارامی را فریب داد، چونکه او رااز فرار کردن خود آگاه نساخت.۲۰
21 Saboda haka ya gudu da dukan abin da ya mallaka, ya ƙetare Kogi, ya nufi yankin tuddan Gileyad.
پس با آنچه داشت، بگریخت و برخاسته، از نهر عبور کرد ومتوجه جبل جلعاد شد.۲۱
22 A rana ta uku, sai aka faɗa wa Laban cewa Yaƙub ya gudu.
در روز سوم، لابان را خبر دادند که یعقوب فرار کرده است.۲۲
23 Sai Laban ya ɗauki danginsa tare da shi, ya bi bayan Yaƙub har kwana bakwai, ya kuma same shi a yankin tuddan Gileyad.
پس برادران خویش را با خودبرداشته، هفت روز راه در عقب او شتافت، تا درجبل جلعاد بدو پیوست.۲۳
24 Sai Allah ya bayyana ga Laban mutumin Aram a mafarki da dare, ya ce masa, “Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu, ko mai kyau ko marar kyau.”
شبانگاه، خدا درخواب بر لابان ارامی ظاهر شده، به وی گفت: «باحذر باش که به یعقوب نیک یا بد نگویی.»۲۴
25 Yaƙub ya riga ya kafa tentinsa a yankin tuddan Gileyad sa’ad da Laban ya same shi. Laban da danginsa suka kafa sansani a can su ma.
پس لابان به یعقوب دررسید و یعقوب خیمه خود رادر جبل زده بود، و لابان با برادران خود نیز درجبل جلعاد فرود آمدند.۲۵
26 Sai Laban ya ce wa Yaƙub, “Me ke nan ka yi? Ka ruɗe ni, ka kuma ɗauki’ya’yana mata kamar kamammun yaƙi.
و لابان به یعقوب گفت: «چه کردی که مرا فریب دادی و دخترانم رامثل اسیران، شمشیر برداشته، رفتی؟۲۶
27 Me ya sa ka gudu a ɓoye ka kuma ruɗe ni? Me ya sa ba ka faɗa mini don in sallame ka da farin ciki da waƙoƙi haɗe da kiɗin ganguna da garayu ba?
چرامخفی فرار کرده، مرا فریب دادی و مرا آگاه نساختی تا تو را با شادی و نغمات و دف و بربطمشایعت نمایم؟۲۷
28 Ba ka ma bari in sumbaci jikokina da’ya’yana mata in yi musu bankwana ba. Ka yi wauta.
و مرا نگذاشتی که پسران ودختران خود ببوسم؛ الحال ابلهانه حرکتی نمودی.۲۸
29 Ina da iko in cuce ka; amma jiya da dare Allahn mahaifinka ya faɗa mini, ‘Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu ko mai kyau ko marar kyau.’
در قوت دست من است که به شمااذیت رسانم. لیکن خدای پدر شما دوش به من خطاب کرده، گفت: «با حذر باش که به یعقوب نیک یا بد نگویی.»۲۹
30 Yanzu ka gudu domin kana marmari komawa gidan mahaifinka. Amma don me ka sace mini gumakana?”
و الان چونکه به خانه پدرخود رغبتی تمام داشتی البته رفتنی بودی و لکن خدایان مرا چرا دزدیدی؟»۳۰
31 Yaƙub ya amsa wa Laban, “Na ji tsoro ne, domin na yi tsammani za ka ƙwace’ya’yanka mata daga gare ni ƙarfi da yaji.
یعقوب در جواب لابان گفت: «سبب این بود که ترسیدم و گفتم شایددختران خود را از من به زور بگیری،۳۱
32 Amma in ka sami wani wanda yake da gumakanka, ba zai rayu ba. Kai da kanka ka duba a gaban danginmu, ko akwai wani abin da yake naka a nan tare da ni; in ka gani, ka ɗauka.” Yaƙub dai bai san cewa Rahila ta sace gumakan ba.
و اما نزدهر‌که خدایانت را بیابی، او زنده نماند. در حضوربرادران ما، آنچه از اموال تو نزد ما باشد، مشخص کن و برای خود بگیر.» زیرا یعقوب ندانست که راحیل آنها را دزدیده است.۳۲
33 Saboda haka Laban ya shiga tentin Yaƙub, ya shiga tentin Liyatu da kuma tentuna matan nan biyu bayi, amma bai sami kome ba. Bayan ya fita daga tentin Liyatu, sai ya shiga tentin Rahila.
پس لابان به خیمه یعقوب و به خیمه لیه وبه خیمه دو کنیز رفت و نیافت، و از خیمه لیه بیرون آمده، به خیمه راحیل درآمد.۳۳
34 Rahila fa ta kwashe gumakan gidan ta sa su cikin sirdin raƙumi, ta kuma zauna a kansu. Laban ya bincika cikin kowane abu a tentin amma bai sami kome ba.
اما راحیل بتها را گرفته، زیر جهاز شتر نهاد و بر آن بنشست و لابان تمام خیمه را جست وجو کرده، چیزی نیافت.۳۴
35 Sai Rahila ta ce wa mahaifinta, “Kada ka yi fushi, ranka yă daɗe da ban tashi tsaye a gabanka ba; gama ina al’adar mata ne.” Saboda haka ya bincika amma bai sami gumakan gidan ba.
او به پدر خود گفت: «بنظر آقایم بدنیاید که در حضورت نمی توانم برخاست، زیرا که عادت زنان بر من است.» پس تجسس نموده، بتهارا نیافت.۳۵
36 Yaƙub ya fusata, ya kuma yi wa Laban faɗa. Ya tambayi Laban, “Mene ne laifina? Wanda zunubi na yi da kake farautata?
آنگاه یعقوب خشمگین شده، با لابان منازعت کرد. و یعقوب در جواب لابان گفت: «تقصیر و خطای من چیست که بدین گرمی مراتعاقب نمودی؟۳۶
37 Yanzu da ka bincika dukan kayayyakina, me ka samu da yake na gidanka? Kawo shi nan a gaban danginka da kuma dangina, bari su zama alƙali tsakaninmu biyu.
الان که تمامی اموال مراتفتیش کردی، از همه اسباب خانه خود چه یافته‌ای، اینجا نزد برادران من و برادران خودبگذار تا در میان من و تو انصاف دهند.۳۷
38 “Na kasance tare da kai shekaru ashirin. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuwa ci raguna daga garkunanka ba.
در این بیست سال که من با تو بودم، میشها و بزهایت حمل نینداختند و قوچهای گله تو را نخوردم.۳۸
39 Ban kawo dabbobinka da namun jeji suka yayyaga; na kuma ɗauki hasarar ba? Ka nemi in biya dukan abin da aka sace da rana ko da dare.
دریده شده‌ای را پیش تو نیاوردم؛ خود تاوان آن را می‌دادم و آن را از دست من می‌خواستی، خواه دزدیده شده در روز و خواه دزدیده شده درشب.۳۹
40 Yanayin da na kasance ke nan, da rana na sha zafin rana da dare kuma na sha sanyi, ga rashin barci.
چنین بودم که گرما در روز و سرما درشب، مرا تلف می‌کرد، و خواب از چشمانم می‌گریخت.۴۰
41 Haka ya kasance shekaru ashirin da na yi a gidanka. Na yi maka aiki shekaru goma sha huɗu domin’ya’yanka mata biyu, na kuma yi shekaru shida domin garkunanka, ka kuma canja albashina sau goma.
بدینطور بیست سال در خانه ات بودم، چهارده سال برای دو دخترت خدمت توکردم، و شش سال برای گله ات، و اجرت مرا ده مرتبه تغییر دادی.۴۱
42 Da ba don Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim da kuma Tsoron Ishaku ya kasance tare da ni ba, tabbatacce da ka sallame ni hannu wofi. Amma Allah ya ga wahalata da famar hannuwana, ya kuwa tsawata maka da dare jiya.”
و اگر خدای پدرم، خدای ابراهیم، و هیبت اسحاق با من نبودی، اکنون نیزمرا تهی‌دست روانه می‌نمودی. خدا مصیبت مراو مشقت دستهای مرا دید و دوش، تو را توبیخ نمود.»۴۲
43 Laban ya amsa wa Yaƙub, “Matan,’ya’yana ne,’ya’yansu,’ya’yana ne, garkunan kuma garkunana ne. Dukan abin da kake gani, nawa ne. Duk da haka me zan yi a rana ta yau ga waɗannan’ya’yana mata, ko kuma ga’ya’yan da suka haifa?
لابان در جواب یعقوب گفت: «این دختران، دختران منند و این پسران، پسران من واین گله، گله من و آنچه می‌بینی از آن من است. پس الیوم، به دختران خودم و به پسرانی که زاییده‌اند چه توانم کرد؟۴۳
44 Zo, bari mu ƙulla yarjejjeniya, da kai da ni, bari kuma ta kasance shaida a tsakaninmu.”
اکنون بیا تا من و توعهد ببندیم که در میان من و تو شهادتی باشد.»۴۴
45 Saboda haka Yaƙub ya ɗauki dutse ya kafa yă zama al’amudi.
پس یعقوب سنگی گرفته، آن را ستونی برپانمود.۴۵
46 Ya ce wa danginsa. “Ku tattara waɗansu duwatsu.” Sai suka kwashe duwatsu suka tsiba, suka kuwa ci abinci a can kusa da tsibin.
و یعقوب برادران خود را گفت: «سنگهاجمع کنید.» پس سنگها جمع کرده، توده‌ای ساختند و در آنجا بر توده غذا خوردند.۴۶
47 Laban ya sa masa suna Yegar Sahaduta, Yaƙub kuwa ya kira shi Galeyed.
ولابان آن را «یجرسهدوتا» نامید ولی یعقوب آن راجلعید خواند.۴۷
48 Laban ya ce, “Wannan tsibi, shi ne shaida tsakaninka da ni a yau.” Shi ya sa aka kira shi Galeyed.
و لابان گفت: «امروز این توده در میان من و تو شهادتی است.» از این سبب آن را «جلعید» نامید.۴۸
49 Aka kuma kira shi Mizfa, domin ya ce, “Ubangiji yă sa ido tsakanin ni da kai sa’ad da muka rabu da juna.
و مصفه نیز، زیرا گفت: «خداوند در میان من و تو دیده بانی کند وقتی که ازیکدیگر غایب شویم.۴۹
50 Laban ya ce in ka wulaƙanta’ya’yana mata, ko ka auri waɗansu mata ban da’ya’yana mata, ko da yake babu wani da yake tare da mu, ka tuna cewa Allah shi ne shaida tsakaninka da ni.”
اگر دختران مرا آزارکنی، و سوای دختران من، زنان دیگر بگیری، هیچکس در میان ما نخواهد بود. آگاه باش، خدادر میان من و تو شاهد است.»۵۰
51 Laban ya kuma ce wa Yaƙub, “Ga wannan tsibi, ga kuma wannan al’amudin da na kafa tsakaninka da ni.
و لابان به یعقوب گفت: «اینک این توده و اینک این ستونی که در میان خود و تو برپا نمودم.۵۱
52 Wannan tsibin shi ne shaida, wannan al’amudi kuma shaida ne, cewa ba zan tsallake wannan tsibi zuwa gefenka don in cuce ka ba, kai kuma ba za ka tsallake wannan tsibi da al’amudi zuwa gefena don ka cuce ni ba.
این توده شاهد است و این ستون شاهد است که من از این توده بسوی تو نگذرم و تو از این توده و از این ستون به قصدبدی بسوی من نگذری.۵۲
53 Bari Allah na Ibrahim da Allah na Nahor, Allah na iyayensu, yă zama alƙali tsakaninmu.” Saboda haka Yaƙub ya yi rantsuwa da sunan Tsoron mahaifinsa Ishaku.
خدای ابراهیم وخدای ناحور و خدای پدر ایشان در میان ماانصاف دهند.» و یعقوب قسم خورد به هیبت پدرخود اسحاق.۵۳
54 Ya miƙa hadaya a can a ƙasar tudu, ya kuma gayyaci danginsa zuwa wurin cin abinci. Bayan suka ci, sai suka kwana a can.
آنگاه یعقوب در آن کوه، قربانی گذرانید، و برادران خود را به نان خوردن دعوت نمود، و غذا خوردند و در کوه، شب را بسر بردند.۵۴
55 Da sassafe kashegari sai Laban ya sumbaci jikokinsa da’ya’yansa mata, ya sa musu albarka. Sa’an nan ya yi bankwana da su, ya koma gida.
بامدادان لابان برخاسته، پسران و دختران خودرا بوسید و ایشان را برکت داد و لابان روانه شده، به مکان خویش مراجعت نمود.۵۵

< Farawa 31 >