< Farawa 31 >

1 Yaƙub ya ji cewa’ya’ya Laban mazan suna cewa, “Yaƙub ya kwashe dukan abin da mahaifinmu yake da shi, ya kuma sami dukan wannan arziki daga abin da yake na mahaifinmu.”
Or après que Jacob eut entendu les paroles des fils de Laban, qui disaient: Jacob a enlevé tout ce qui était à notre père, et enrichi de son bien, il est devenu un grand personnage,
2 Yaƙub kuma ya lura cewa halin Laban gare shi ya canja ba kamar yadda yake a dā ba.
Et qu’il eut aussi remarqué que le visage de Laban n’était pas pour lui comme hier et avant-hier,
3 Sai Ubangiji ya ce wa Yaƙub, “Koma ƙasar kakanninka da kuma danginka, zan kuwa kasance tare da kai.”
Surtout le Seigneur lui ayant dit: Retourne au pays de tes pères et vers ta famille, et je serai avec toi,
4 Saboda haka Yaƙub ya aika a ce wa Rahila da Liyatu su zo jeji inda garkunan suke.
Il envoya et appela Rachel et Lia dans le champ où il paissait les troupeaux,
5 Sai ya ce musu, “Na ga cewa halin mahaifinku gare ni ba kamar yadda dā yake ba, amma Allah na mahaifina yana tare da ni.
Et il leur dit: Je vois que le visage de votre père n’est pas pour moi comme hier et avant-hier; mais le Dieu de mon père a été avec moi;
6 Kun san cewa na yi aiki wa mahaifinku da dukan ƙarfina,
Et vous-mêmes vous savez que c’est de toutes mes forces que j’ai servi votre père.
7 duk da haka mahaifinku ya cuce ni ta wurin sauya albashina sau goma. Amma dai, Allah bai yardar masa yă yi mini lahani ba.
Mais votre père m’a trompé, et il a changé dix fois ma récompense; et cependant Dieu ne l’a pas laissé me nuire.
8 In ya ce, ‘Dabbare-dabbare ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi dabbare-dabbare, in kuma ya ce, ‘Masu zāne-zāne ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi ƙananan masu zāne-zāne.
Quand il a dit: Les petits mouchetés seront ta récompense; toutes les brebis avaient des petits mouchetés; quand au contraire il a dit: Tu recevras tous les blancs pour récompense, tous les troupeaux ont fait des petits blancs.
9 Ta haka Allah ya kwashe dabbobin mahaifinku ya ba ni.
C’est ainsi que Dieu a pris le bien de votre père, et me l’a donné.
10 “A lokacin ɗaukar cikin garken, na taɓa yin mafarki inda na ga bunsuran da suke barbara da garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne.
Car lorsque le temps de la conception des brebis fut venu, je levai mes yeux, et je vis en songe les mâles couvrant les femelles, mouchetés, tachetés, et de diverses couleurs.
11 Sai mala’ikan Allah ya ce mini a mafarkin, ‘Yaƙub.’ Sai na amsa na ce, ‘Ga ni.’
Et l’ange de Dieu me dit en songe: Jacob. Et moi je répondis: Me voici.
12 Ya ce, ‘Ɗaga idanunka ka gani, dukan bunsuran da suke hawan garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne, gama na ga dukan abin da Laban yake yin maka.
Il ajouta: Lève les yeux et vois: tous les mâles couvrant les femelles sont mouchetés, tachetés et parsemés de marques de diverses couleurs; car j’ai vu tout ce que t’a fait Laban.
13 Ni ne Allah na Betel, inda ka zuba wa al’amudi mai, da kuma inda ka yi mini alkawari. Yanzu ka bar wannan ƙasa nan take, ka koma ƙasarka ta ainihi.’”
Je suis le Dieu de Béthel, où tu as oint une pierre, et où tu m’as voué un vœu. Maintenant donc lève-toi, sors de cette terre, retournant dans le pays de ta naissance.
14 Sai Rahila da Liyatu suka amsa suka ce, “Muna da wani rabo a gādon kayan mahaifinmu ne?
Rachel et Lia répondirent: Nous reste-t-il quelque chose des biens et de l’héritage de la maison de notre père?
15 Ba kamar baƙi ne yake ɗaukarmu ba? Ba sayar da mu kaɗai ya yi ba, har ma ya yi amfani da abin da aka biya saboda mu.
N’est-ce pas comme des étrangères qu’il nous a considérées et vendues; et n’a-t-il pas mangé le prix de notre vente?
16 Tabbatacce dukan dukiyar da Allah ya kwashe daga mahaifinmu ya zama namu da’ya’yanmu. Saboda haka ka yi duk abin da Allah ya faɗa maka.”
Mais Dieu a pris les richesses de notre père, et nous les a données, à nous et à nos fils: ainsi, tout ce que Dieu t’a commandé, fais-le.
17 Sa’an nan Yaƙub ya sa’ya’yansa da matansa a kan raƙuma,
C’est pourquoi Jacob se leva, et ses enfants et ses femmes placés sur des chameaux, il s’en alla,
18 ya kuma kora dukan dabbobinsa, suka ja gabansa, tare da dukan abubuwan da ya samu a Faddan Aram, don su tafi wurin mahaifinsa Ishaku a ƙasar Kan’ana.
Et emporta toutes ses richesses, tous ses troupeaux et tout ce qu’il avait acquis en Mésopotamie, se dirigeant vers Isaac son père dans la terre de Chanaan.
19 Sa’ad da Laban ya tafi don askin tumakinsa, sai Rahila ta sace gumakan gidan mahaifinta.
En ce temps-là Laban était allé tondre ses brebis, et Rachel déroba les idoles de son père.
20 Yaƙub kuwa ya ruɗe Laban mutumin Aram da bai sanar da shi zai gudu ba.
Jacob ne voulut pas avouer à son beau-père qu’il fuyait.
21 Saboda haka ya gudu da dukan abin da ya mallaka, ya ƙetare Kogi, ya nufi yankin tuddan Gileyad.
Lors donc qu’il fut parti, et lui et tout ce qui était à lui de plein droit, et que, le fleuve traversé, il s’avançait vers la montagne de Galaad,
22 A rana ta uku, sai aka faɗa wa Laban cewa Yaƙub ya gudu.
On annonça à Laban, le troisième jour, que Jacob fuyait.
23 Sai Laban ya ɗauki danginsa tare da shi, ya bi bayan Yaƙub har kwana bakwai, ya kuma same shi a yankin tuddan Gileyad.
Laban ayant pris ses frères avec lui, le poursuivit durant sept jours, et l’atteignit à la montagne de Galaad.
24 Sai Allah ya bayyana ga Laban mutumin Aram a mafarki da dare, ya ce masa, “Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu, ko mai kyau ko marar kyau.”
Et il vit en songe Dieu qui lui dit: Garde-toi de rien dire à Jacob avec dureté.
25 Yaƙub ya riga ya kafa tentinsa a yankin tuddan Gileyad sa’ad da Laban ya same shi. Laban da danginsa suka kafa sansani a can su ma.
Or Jacob avait déjà tendu sa tente sur la montagne; et quand Laban l’eut atteint avec ses frères, c’est sur la même montagne de Galaad qu’il planta sa tente,
26 Sai Laban ya ce wa Yaƙub, “Me ke nan ka yi? Ka ruɗe ni, ka kuma ɗauki’ya’yana mata kamar kamammun yaƙi.
Et il dit à Jacob: Pourquoi as-tu agi ainsi, que d’emmener mes filles à mon insu, comme des captives du glaive?
27 Me ya sa ka gudu a ɓoye ka kuma ruɗe ni? Me ya sa ba ka faɗa mini don in sallame ka da farin ciki da waƙoƙi haɗe da kiɗin ganguna da garayu ba?
Pourquoi, moi l’ignorant, as-tu voulu fuir, et ne pas m’avertir, pour que je t’accompagnasse avec joie, avec des chants, des tambours et des harpes?
28 Ba ka ma bari in sumbaci jikokina da’ya’yana mata in yi musu bankwana ba. Ka yi wauta.
Tu ne m’as laissé embrasser ni mes fils ni mes filles; tu as agi en insensé: et maintenant certes,
29 Ina da iko in cuce ka; amma jiya da dare Allahn mahaifinka ya faɗa mini, ‘Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu ko mai kyau ko marar kyau.’
Ma main peut te rendre le mal; mais le Dieu de ton père m’a dit hier: Garde-toi de dire à Jacob rien de trop dur.
30 Yanzu ka gudu domin kana marmari komawa gidan mahaifinka. Amma don me ka sace mini gumakana?”
Eh bien, soit, tu désirais aller vers les tiens; et la maison de ton père était pour toi un objet de regret; pourquoi m’as-tu dérobé mes dieux?
31 Yaƙub ya amsa wa Laban, “Na ji tsoro ne, domin na yi tsammani za ka ƙwace’ya’yanka mata daga gare ni ƙarfi da yaji.
Jacob répondit: Si je suis parti à ton insu, c’est que j’ai craint que tu ne m’enlevasses violemment tes filles.
32 Amma in ka sami wani wanda yake da gumakanka, ba zai rayu ba. Kai da kanka ka duba a gaban danginmu, ko akwai wani abin da yake naka a nan tare da ni; in ka gani, ka ɗauka.” Yaƙub dai bai san cewa Rahila ta sace gumakan ba.
Mais quant au larcin que tu me reproches, que celui chez qui tu trouveras tes dieux soit mis à mort devant nos frères: fouille; tout ce que tu trouveras à toi chez moi, emporte-le. Disant cela, il ignorait que Rachel avait enlevé les idoles.
33 Saboda haka Laban ya shiga tentin Yaƙub, ya shiga tentin Liyatu da kuma tentuna matan nan biyu bayi, amma bai sami kome ba. Bayan ya fita daga tentin Liyatu, sai ya shiga tentin Rahila.
Laban étant donc entré dans la tente de Jacob, de Lia et des deux servantes, ne trouva rien. Mais quand il entra dans la tente de Rachel,
34 Rahila fa ta kwashe gumakan gidan ta sa su cikin sirdin raƙumi, ta kuma zauna a kansu. Laban ya bincika cikin kowane abu a tentin amma bai sami kome ba.
Celle-ci se hâtant, cacha les idoles sous le bât de son chameau, et elle s’assit dessus; et comme il fouillait toute la tente, et qu’il ne trouvait rien,
35 Sai Rahila ta ce wa mahaifinta, “Kada ka yi fushi, ranka yă daɗe da ban tashi tsaye a gabanka ba; gama ina al’adar mata ne.” Saboda haka ya bincika amma bai sami gumakan gidan ba.
Elle lui dit: Que mon seigneur ne se fâche point de ce que je ne puis me lever en sa présence; car ce qui est ordinaire aux femmes, m’arrive en ce moment. Ainsi elle dépista ces minutieuses perquisitions.
36 Yaƙub ya fusata, ya kuma yi wa Laban faɗa. Ya tambayi Laban, “Mene ne laifina? Wanda zunubi na yi da kake farautata?
Alors s’emportant, Jacob lui dit avec reproche: Pour quelle faute, et pour quel péché t’es-tu ainsi enflammé après moi,
37 Yanzu da ka bincika dukan kayayyakina, me ka samu da yake na gidanka? Kawo shi nan a gaban danginka da kuma dangina, bari su zama alƙali tsakaninmu biyu.
Et as-tu fouillé tous mes objets? Qu’as-tu trouvé de tout ce qui appartient à ta maison? Mets-le ici devant mes frères et tes frères, et qu’ils jugent entre moi et toi.
38 “Na kasance tare da kai shekaru ashirin. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuwa ci raguna daga garkunanka ba.
Est-ce pour cela que j’ai été vingt ans avec toi? tes brebis et tes chèvres n’ont pas été stériles; je n’ai pas mangé les béliers de ton troupeau:
39 Ban kawo dabbobinka da namun jeji suka yayyaga; na kuma ɗauki hasarar ba? Ka nemi in biya dukan abin da aka sace da rana ko da dare.
Et pour ce qui avait été pris par les bêtes sauvages, je ne t’en ai pas averti; c’est moi qui en réparais tout le dommage: tout ce qui avait été dérobé, c’est de moi que tu l’exigeais.
40 Yanayin da na kasance ke nan, da rana na sha zafin rana da dare kuma na sha sanyi, ga rashin barci.
Le jour et la nuit j’étais brûlé par la chaleur et glacé par le froid; et le sommeil fuyait de mes yeux.
41 Haka ya kasance shekaru ashirin da na yi a gidanka. Na yi maka aiki shekaru goma sha huɗu domin’ya’yanka mata biyu, na kuma yi shekaru shida domin garkunanka, ka kuma canja albashina sau goma.
C’est ainsi que pendant vingt ans je t’ai servi dans ta maison, quatorze pour tes filles, et six pour tes troupeaux: et tu as changé ma récompense dix fois.
42 Da ba don Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim da kuma Tsoron Ishaku ya kasance tare da ni ba, tabbatacce da ka sallame ni hannu wofi. Amma Allah ya ga wahalata da famar hannuwana, ya kuwa tsawata maka da dare jiya.”
Si le Dieu de mon père Abraham et la crainte d’Isaac ne m’avaient protégé, peut-être m’aurais-tu maintenant renvoyé nu; mais Dieu a regardé mon affliction et le travail de mes mains, et il t’a fait hier des reproches.
43 Laban ya amsa wa Yaƙub, “Matan,’ya’yana ne,’ya’yansu,’ya’yana ne, garkunan kuma garkunana ne. Dukan abin da kake gani, nawa ne. Duk da haka me zan yi a rana ta yau ga waɗannan’ya’yana mata, ko kuma ga’ya’yan da suka haifa?
Laban lui répondit: Mes filles et mes fils, tes troupeaux, et tout ce que tu vois, sont à moi, que puis-je faire à mes filles et à mes petits-fils?
44 Zo, bari mu ƙulla yarjejjeniya, da kai da ni, bari kuma ta kasance shaida a tsakaninmu.”
Viens donc et faisons une alliance, pour qu’elle soit en témoignage entre moi et toi.
45 Saboda haka Yaƙub ya ɗauki dutse ya kafa yă zama al’amudi.
C’est pourquoi Jacob mit une pierre, et l’érigea en monument.
46 Ya ce wa danginsa. “Ku tattara waɗansu duwatsu.” Sai suka kwashe duwatsu suka tsiba, suka kuwa ci abinci a can kusa da tsibin.
Et il dit à ses frères: Apportez des pierres. Ceux-ci en ayant rassemblé firent un grand tas. et mangèrent dessus;
47 Laban ya sa masa suna Yegar Sahaduta, Yaƙub kuwa ya kira shi Galeyed.
Laban l’appela Monceau du témoin, et Jacob, Monceau du témoignage, chacun selon la propriété de sa langue.
48 Laban ya ce, “Wannan tsibi, shi ne shaida tsakaninka da ni a yau.” Shi ya sa aka kira shi Galeyed.
Et Laban dit: Ce monceau sera témoin entre moi et toi aujourd’hui; et c’est pourquoi on l’a appelé du nom de Galaad, c’est-à-dire. Monceau du témoin.
49 Aka kuma kira shi Mizfa, domin ya ce, “Ubangiji yă sa ido tsakanin ni da kai sa’ad da muka rabu da juna.
Que le Seigneur considère et juge entre nous, quand nous serons éloignés l’un de l’autre.
50 Laban ya ce in ka wulaƙanta’ya’yana mata, ko ka auri waɗansu mata ban da’ya’yana mata, ko da yake babu wani da yake tare da mu, ka tuna cewa Allah shi ne shaida tsakaninka da ni.”
Si tu affliges mes filles, et si tu prends d’autres femmes avec elles, nul n’est témoin de nos paroles, excepté Dieu, qui présent, nous regarde.
51 Laban ya kuma ce wa Yaƙub, “Ga wannan tsibi, ga kuma wannan al’amudin da na kafa tsakaninka da ni.
Il dit de nouveau à Jacob: Voilà que ce monceau et la pierre que j’ai dressée entre moi et toi
52 Wannan tsibin shi ne shaida, wannan al’amudi kuma shaida ne, cewa ba zan tsallake wannan tsibi zuwa gefenka don in cuce ka ba, kai kuma ba za ka tsallake wannan tsibi da al’amudi zuwa gefena don ka cuce ni ba.
Sera témoin: que ce monceau, dis-je, et cette pierre soient en témoignage, si moi je les franchis, venant vers toi, ou si toi tu les dépasses, méditant le mal contre moi.
53 Bari Allah na Ibrahim da Allah na Nahor, Allah na iyayensu, yă zama alƙali tsakaninmu.” Saboda haka Yaƙub ya yi rantsuwa da sunan Tsoron mahaifinsa Ishaku.
Que le Dieu d’Abraham, le Dieu de Nachor, le Dieu de leur père juge entre nous. Jacob donc jura par la crainte de son père Isaac;
54 Ya miƙa hadaya a can a ƙasar tudu, ya kuma gayyaci danginsa zuwa wurin cin abinci. Bayan suka ci, sai suka kwana a can.
Puis, des victimes immolées sur la montagne, il invita ses frères à manger du pain. Lorsqu’ils eurent mangé, ils demeurèrent là.
55 Da sassafe kashegari sai Laban ya sumbaci jikokinsa da’ya’yansa mata, ya sa musu albarka. Sa’an nan ya yi bankwana da su, ya koma gida.
Mais Laban, se levant de nuit, embrassa ses fils et ses filles, et les bénit, et il s’en retourna dans sa demeure.

< Farawa 31 >