< Farawa 31 >
1 Yaƙub ya ji cewa’ya’ya Laban mazan suna cewa, “Yaƙub ya kwashe dukan abin da mahaifinmu yake da shi, ya kuma sami dukan wannan arziki daga abin da yake na mahaifinmu.”
Jacob entendit les propos des fils de Laban, qui disaient: « Jacob a pris tout ce qui était à notre père, et c’est avec le bien de notre père qu’il s’est fait toute cette richesse. »
2 Yaƙub kuma ya lura cewa halin Laban gare shi ya canja ba kamar yadda yake a dā ba.
Jacob remarqua aussi le visage de Laban, et voici, il n’était plus à son égard comme auparavant.
3 Sai Ubangiji ya ce wa Yaƙub, “Koma ƙasar kakanninka da kuma danginka, zan kuwa kasance tare da kai.”
Et Yahweh dit à Jacob: « Retourne au pays de tes pères et au lieu de ta naissance, et je serai avec toi. »
4 Saboda haka Yaƙub ya aika a ce wa Rahila da Liyatu su zo jeji inda garkunan suke.
Alors Jacob fit dire à Rachel et à Lia de venir le trouver aux champs, où il faisait paître son troupeau.
5 Sai ya ce musu, “Na ga cewa halin mahaifinku gare ni ba kamar yadda dā yake ba, amma Allah na mahaifina yana tare da ni.
Il leur dit: « Je vois que le visage de votre père n’est plus le même envers moi qu’auparavant; or le Dieu de mon père a été avec moi.
6 Kun san cewa na yi aiki wa mahaifinku da dukan ƙarfina,
Vous savez vous-mêmes que j’ai servi votre père de tout mon pouvoir;
7 duk da haka mahaifinku ya cuce ni ta wurin sauya albashina sau goma. Amma dai, Allah bai yardar masa yă yi mini lahani ba.
et votre père s’est joué de moi, changeant dix fois mon salaire; mais Dieu ne lui a pas permis de me causer du préjudice.
8 In ya ce, ‘Dabbare-dabbare ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi dabbare-dabbare, in kuma ya ce, ‘Masu zāne-zāne ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi ƙananan masu zāne-zāne.
Quand il disait: Les bêtes tachetées seront ton salaire, toutes les brebis faisaient des agneaux tachetés. Et s’il disait: Les bêtes rayées seront ton salaire, toutes les brebis faisaient des agneaux rayés.
9 Ta haka Allah ya kwashe dabbobin mahaifinku ya ba ni.
Dieu a donc pris le bétail de votre père et me l’a donné.
10 “A lokacin ɗaukar cikin garken, na taɓa yin mafarki inda na ga bunsuran da suke barbara da garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne.
Au temps où les brebis entrent en chaleur, je levai les yeux et je vis en songe que les béliers qui couvraient les brebis étaient rayés, tachetés et marquetés.
11 Sai mala’ikan Allah ya ce mini a mafarkin, ‘Yaƙub.’ Sai na amsa na ce, ‘Ga ni.’
Et un ange de Dieu me dit en songe: Jacob! Je répondis: Me voici.
12 Ya ce, ‘Ɗaga idanunka ka gani, dukan bunsuran da suke hawan garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne, gama na ga dukan abin da Laban yake yin maka.
Et il dit: Lève les yeux et regarde: tous les béliers qui couvrent les brebis sont rayés, tachetés et marquetés; car j’ai vu tout ce que t’a fait Laban.
13 Ni ne Allah na Betel, inda ka zuba wa al’amudi mai, da kuma inda ka yi mini alkawari. Yanzu ka bar wannan ƙasa nan take, ka koma ƙasarka ta ainihi.’”
Je suis le Dieu de Béthel, où tu as oint un monument, où tu m’as fait un vœu. Maintenant lève-toi, sors de ce pays et retourne au pays de ta naissance. »
14 Sai Rahila da Liyatu suka amsa suka ce, “Muna da wani rabo a gādon kayan mahaifinmu ne?
Rachel et Lia répondirent en disant: « Est-ce que nous avons encore une part et un héritage dans la maison de notre père?
15 Ba kamar baƙi ne yake ɗaukarmu ba? Ba sayar da mu kaɗai ya yi ba, har ma ya yi amfani da abin da aka biya saboda mu.
Ne sommes-nous pas regardées par lui comme des étrangères, puisqu’il nous a vendues et qu’il mange notre argent?
16 Tabbatacce dukan dukiyar da Allah ya kwashe daga mahaifinmu ya zama namu da’ya’yanmu. Saboda haka ka yi duk abin da Allah ya faɗa maka.”
D’ailleurs tout le bien que Dieu a enlevé à notre père, nous l’avons, nous et nos enfants. Fais donc maintenant ce que Dieu t’a ordonné. »
17 Sa’an nan Yaƙub ya sa’ya’yansa da matansa a kan raƙuma,
Jacob se leva et fit monter ses enfants et ses femmes sur les chameaux.
18 ya kuma kora dukan dabbobinsa, suka ja gabansa, tare da dukan abubuwan da ya samu a Faddan Aram, don su tafi wurin mahaifinsa Ishaku a ƙasar Kan’ana.
Il emmena tout son troupeau et tout le bien qu’il avait acquis, le troupeau qu’il possédait, qu’il avait acquis à Paddan-Aram; et il s’en alla vers Isaac, son père, au pays de Canaan.
19 Sa’ad da Laban ya tafi don askin tumakinsa, sai Rahila ta sace gumakan gidan mahaifinta.
Comme Laban était allé tondre ses brebis, Rachel déroba les théraphim de son père.
20 Yaƙub kuwa ya ruɗe Laban mutumin Aram da bai sanar da shi zai gudu ba.
Et Jacob trompa Laban, l’Araméen, en ne l’informant pas de sa fuite.
21 Saboda haka ya gudu da dukan abin da ya mallaka, ya ƙetare Kogi, ya nufi yankin tuddan Gileyad.
Il s’enfuit, lui et tout ce qui lui appartenait et, s’étant levé, il traversa le fleuve et se dirigea vers la montagne de Galaad.
22 A rana ta uku, sai aka faɗa wa Laban cewa Yaƙub ya gudu.
Le troisième jour, on annonça à Laban que Jacob s’était enfui.
23 Sai Laban ya ɗauki danginsa tare da shi, ya bi bayan Yaƙub har kwana bakwai, ya kuma same shi a yankin tuddan Gileyad.
Il prit avec lui ses frères et le poursuivit pendant sept journées de chemin; il l’atteignit à la montagne de Galaad.
24 Sai Allah ya bayyana ga Laban mutumin Aram a mafarki da dare, ya ce masa, “Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu, ko mai kyau ko marar kyau.”
Et Dieu vint en songe, de nuit, vers Laban l’Araméen, et il lui dit: « Garde-toi de rien dire à Jacob, ni en bien ni en mal. »
25 Yaƙub ya riga ya kafa tentinsa a yankin tuddan Gileyad sa’ad da Laban ya same shi. Laban da danginsa suka kafa sansani a can su ma.
Laban atteignit donc Jacob. — Jacob avait dressé sa tente sur la montagne, et Laban avait aussi dressé la sienne, avec ses frères, sur la montagne de Galaad.
26 Sai Laban ya ce wa Yaƙub, “Me ke nan ka yi? Ka ruɗe ni, ka kuma ɗauki’ya’yana mata kamar kamammun yaƙi.
Laban dit à Jacob: « Qu’as-tu fait? tu as abusé mon esprit et tu as emmené mes filles comme des captives prises par l’épée?
27 Me ya sa ka gudu a ɓoye ka kuma ruɗe ni? Me ya sa ba ka faɗa mini don in sallame ka da farin ciki da waƙoƙi haɗe da kiɗin ganguna da garayu ba?
Pourquoi as-tu pris secrètement la fuite et m’as-tu trompé, au lieu de m’avertir, moi qui t’aurais laissé aller dans l’allégresse des chants, au son du tambourin et de la harpe?
28 Ba ka ma bari in sumbaci jikokina da’ya’yana mata in yi musu bankwana ba. Ka yi wauta.
Tu ne m’as pas laissé embrasser mes fils et mes filles! Vraiment tu as agi en insensé.
29 Ina da iko in cuce ka; amma jiya da dare Allahn mahaifinka ya faɗa mini, ‘Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu ko mai kyau ko marar kyau.’
Ma main est assez forte pour vous faire du mal; mais le Dieu de votre père m’a parlé cette nuit en disant: Garde-toi de rien dire à Jacob, ni en bien ni en mal.
30 Yanzu ka gudu domin kana marmari komawa gidan mahaifinka. Amma don me ka sace mini gumakana?”
Et maintenant, tu es parti parce que tu languissais après la maison de ton père; mais, pourquoi as-tu dérobé mes dieux? »
31 Yaƙub ya amsa wa Laban, “Na ji tsoro ne, domin na yi tsammani za ka ƙwace’ya’yanka mata daga gare ni ƙarfi da yaji.
Jacob répondit et dit à Laban: « C’est que j’avais de la crainte, en me disant que peut-être tu m’enlèverais tes filles.
32 Amma in ka sami wani wanda yake da gumakanka, ba zai rayu ba. Kai da kanka ka duba a gaban danginmu, ko akwai wani abin da yake naka a nan tare da ni; in ka gani, ka ɗauka.” Yaƙub dai bai san cewa Rahila ta sace gumakan ba.
Quant à celui chez qui tu trouveras tes dieux, il ne vivra pas! En présence de nos frères, reconnais ce qui t’appartient chez moi et prends-le. » — Or Jacob ignorait que Rachel les eût dérobés. —
33 Saboda haka Laban ya shiga tentin Yaƙub, ya shiga tentin Liyatu da kuma tentuna matan nan biyu bayi, amma bai sami kome ba. Bayan ya fita daga tentin Liyatu, sai ya shiga tentin Rahila.
Laban entra dans la tente de Jacob, dans la tente de Lia et dans la tente des deux servantes, et il ne trouva rien. Puis il sortit de la tente de Lia et entra dans la tente de Rachel.
34 Rahila fa ta kwashe gumakan gidan ta sa su cikin sirdin raƙumi, ta kuma zauna a kansu. Laban ya bincika cikin kowane abu a tentin amma bai sami kome ba.
Rachel avait pris les théraphim, les avait mis dans la selle du chameau et s’était assise dessus. Laban fouilla toute la tente, sans rien trouver.
35 Sai Rahila ta ce wa mahaifinta, “Kada ka yi fushi, ranka yă daɗe da ban tashi tsaye a gabanka ba; gama ina al’adar mata ne.” Saboda haka ya bincika amma bai sami gumakan gidan ba.
Et Rachel dit à son père: « Que mon seigneur ne s’irrite pas de ce que je ne puis me lever devant toi, car j’ai ce qui est ordinaire aux femmes. » Il chercha, mais ne trouva pas les théraphim.
36 Yaƙub ya fusata, ya kuma yi wa Laban faɗa. Ya tambayi Laban, “Mene ne laifina? Wanda zunubi na yi da kake farautata?
Jacob se mit en colère et adressa des reproches à Laban; et Jacob prit la parole et dit à Laban: « Quel est mon crime, quelle est ma faute, que tu t’acharnes après moi?
37 Yanzu da ka bincika dukan kayayyakina, me ka samu da yake na gidanka? Kawo shi nan a gaban danginka da kuma dangina, bari su zama alƙali tsakaninmu biyu.
Quand tu as fouillé tous mes effets, qu’as-tu trouvé des effets de ta maison? Produis-le ici devant mes frères et tes frères, et qu’ils soient juges entre nous deux.
38 “Na kasance tare da kai shekaru ashirin. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuwa ci raguna daga garkunanka ba.
Voilà vingt ans que j’ai passés chez toi; tes brebis et tes chèvres n’ont pas avorté, et je n’ai pas mangé les béliers de ton troupeau.
39 Ban kawo dabbobinka da namun jeji suka yayyaga; na kuma ɗauki hasarar ba? Ka nemi in biya dukan abin da aka sace da rana ko da dare.
Ce qui était déchiré par les bêtes sauvages, je ne te l’ai pas rapporté; c’est moi qui en ai supporté la perte. Tu me réclamais ce qui avait été dérobé de jour et ce qui avait été dérobé de nuit.
40 Yanayin da na kasance ke nan, da rana na sha zafin rana da dare kuma na sha sanyi, ga rashin barci.
J’étais dévoré le jour par la chaleur, et la nuit par le froid, et mon sommeil fuyait de mes yeux.
41 Haka ya kasance shekaru ashirin da na yi a gidanka. Na yi maka aiki shekaru goma sha huɗu domin’ya’yanka mata biyu, na kuma yi shekaru shida domin garkunanka, ka kuma canja albashina sau goma.
Voilà vingt ans que je suis dans ta maison; je t’ai servi quatorze ans pour tes deux filles et six ans pour ton bétail, et tu as changé mon salaire dix fois.
42 Da ba don Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim da kuma Tsoron Ishaku ya kasance tare da ni ba, tabbatacce da ka sallame ni hannu wofi. Amma Allah ya ga wahalata da famar hannuwana, ya kuwa tsawata maka da dare jiya.”
Si le Dieu de mon père, le Dieu d’Abraham et la Terreur d’Isaac n’eût pas été pour moi, tu m’aurais maintenant laissé partir à vide. Dieu a vu ma souffrance et le travail de mes mains, et cette nuit il a jugé entre nous. »
43 Laban ya amsa wa Yaƙub, “Matan,’ya’yana ne,’ya’yansu,’ya’yana ne, garkunan kuma garkunana ne. Dukan abin da kake gani, nawa ne. Duk da haka me zan yi a rana ta yau ga waɗannan’ya’yana mata, ko kuma ga’ya’yan da suka haifa?
Laban répondit et dit à Jacob: « Ces filles sont mes filles, ces enfants mes enfants, ces troupeaux mes troupeaux, et tout ce que tu vois est à moi. Que ferais-je aujourd’hui à mes filles, à elles et aux fils qu’elles ont enfantés?
44 Zo, bari mu ƙulla yarjejjeniya, da kai da ni, bari kuma ta kasance shaida a tsakaninmu.”
Maintenant donc, viens, faisons alliance, moi et toi, et qu’il y ait un témoin entre moi et toi.
45 Saboda haka Yaƙub ya ɗauki dutse ya kafa yă zama al’amudi.
Jacob prit une pierre et la dressa pour monument.
46 Ya ce wa danginsa. “Ku tattara waɗansu duwatsu.” Sai suka kwashe duwatsu suka tsiba, suka kuwa ci abinci a can kusa da tsibin.
Et Jacob dit à ses frères: « Amassez des pierres. » Ils prirent des pierres et en firent un monceau, et ils mangèrent là sur le monceau.
47 Laban ya sa masa suna Yegar Sahaduta, Yaƙub kuwa ya kira shi Galeyed.
Laban l’appela Yegar-Sahadutha, et Jacob l’appela Galaad.
48 Laban ya ce, “Wannan tsibi, shi ne shaida tsakaninka da ni a yau.” Shi ya sa aka kira shi Galeyed.
Et Laban dit: « Ce monceau est témoin entre moi et toi aujourd’hui. » C’est pourquoi on lui donna le nom de Galaad,
49 Aka kuma kira shi Mizfa, domin ya ce, “Ubangiji yă sa ido tsakanin ni da kai sa’ad da muka rabu da juna.
et aussi celui de Mitspa, parce que Laban dit: « Que Yahweh nous surveille, moi et toi, quand nous serons séparés l’un de l’autre.
50 Laban ya ce in ka wulaƙanta’ya’yana mata, ko ka auri waɗansu mata ban da’ya’yana mata, ko da yake babu wani da yake tare da mu, ka tuna cewa Allah shi ne shaida tsakaninka da ni.”
Si tu maltraites mes filles et si tu prends d’autres femmes à côté de mes filles, ce n’est pas un homme qui sera avec nous; mais, prends-y garde, c’est Dieu qui sera témoin entre moi et toi. »
51 Laban ya kuma ce wa Yaƙub, “Ga wannan tsibi, ga kuma wannan al’amudin da na kafa tsakaninka da ni.
Laban dit encore à Jacob: « Voici ce monceau et voici le monument que j’ai dressé entre moi et toi.
52 Wannan tsibin shi ne shaida, wannan al’amudi kuma shaida ne, cewa ba zan tsallake wannan tsibi zuwa gefenka don in cuce ka ba, kai kuma ba za ka tsallake wannan tsibi da al’amudi zuwa gefena don ka cuce ni ba.
Ce monceau est témoin et ce monument est témoin que je n’avancerai pas vers toi au delà de ce monceau, et que tu n’avanceras pas vers moi au delà de ce monceau et de ce monument, pour faire du mal.
53 Bari Allah na Ibrahim da Allah na Nahor, Allah na iyayensu, yă zama alƙali tsakaninmu.” Saboda haka Yaƙub ya yi rantsuwa da sunan Tsoron mahaifinsa Ishaku.
Que le Dieu d’Abraham, le Dieu de Nachor et le Dieu de leurs pères soient juges entre nous! » Et Jacob jura par la Terreur d’Isaac.
54 Ya miƙa hadaya a can a ƙasar tudu, ya kuma gayyaci danginsa zuwa wurin cin abinci. Bayan suka ci, sai suka kwana a can.
Et Jacob offrit un sacrifice sur la montagne, et il invita ses frères au repas. Ils mangèrent donc et passèrent la nuit sur la montagne.
55 Da sassafe kashegari sai Laban ya sumbaci jikokinsa da’ya’yansa mata, ya sa musu albarka. Sa’an nan ya yi bankwana da su, ya koma gida.
Laban se leva de bon matin; il baisa ses fils et ses filles et les bénit; puis il partit, pour retourner dans sa maison.