< Farawa 31 >
1 Yaƙub ya ji cewa’ya’ya Laban mazan suna cewa, “Yaƙub ya kwashe dukan abin da mahaifinmu yake da shi, ya kuma sami dukan wannan arziki daga abin da yake na mahaifinmu.”
Now Jacob heard the words of Laban's sons, that they said, “Jacob has taken away all that was our father's, and it is from our father's possessions that he has gotten all this wealth.”
2 Yaƙub kuma ya lura cewa halin Laban gare shi ya canja ba kamar yadda yake a dā ba.
Jacob saw the look on Laban's face. He saw that his attitude toward him had changed.
3 Sai Ubangiji ya ce wa Yaƙub, “Koma ƙasar kakanninka da kuma danginka, zan kuwa kasance tare da kai.”
Then Yahweh said to Jacob, “Return to the land of your fathers and to your relatives, and I will be with you.”
4 Saboda haka Yaƙub ya aika a ce wa Rahila da Liyatu su zo jeji inda garkunan suke.
Jacob sent and called Rachel and Leah to the field to his flock
5 Sai ya ce musu, “Na ga cewa halin mahaifinku gare ni ba kamar yadda dā yake ba, amma Allah na mahaifina yana tare da ni.
and said to them, “I see your father's attitude toward me has changed, but the God of my father has been with me.
6 Kun san cewa na yi aiki wa mahaifinku da dukan ƙarfina,
You know that it is with all my strength that I have served your father.
7 duk da haka mahaifinku ya cuce ni ta wurin sauya albashina sau goma. Amma dai, Allah bai yardar masa yă yi mini lahani ba.
Your father has deceived me and changed my wages ten times, but God has not permitted him to hurt me.
8 In ya ce, ‘Dabbare-dabbare ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi dabbare-dabbare, in kuma ya ce, ‘Masu zāne-zāne ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi ƙananan masu zāne-zāne.
If he said, 'The speckled animals will be your wages,' then all the flock bore speckled young. If he said, 'The striped will be your wages,' then the whole flock bore striped young.
9 Ta haka Allah ya kwashe dabbobin mahaifinku ya ba ni.
In this way God has taken away the livestock of your father and given them to me.
10 “A lokacin ɗaukar cikin garken, na taɓa yin mafarki inda na ga bunsuran da suke barbara da garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne.
Once at the time of breeding season, I saw in a dream the male goats that were mating with the flock. The male goats were striped, speckled, and spotted.
11 Sai mala’ikan Allah ya ce mini a mafarkin, ‘Yaƙub.’ Sai na amsa na ce, ‘Ga ni.’
The angel of God said to me in the dream, 'Jacob.' I said, 'Here I am.'
12 Ya ce, ‘Ɗaga idanunka ka gani, dukan bunsuran da suke hawan garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne, gama na ga dukan abin da Laban yake yin maka.
He said, 'Lift up your eyes and see all the male goats that are breeding with the flock. They are striped, speckled, and spotted, for I have seen everything that Laban is doing to you.
13 Ni ne Allah na Betel, inda ka zuba wa al’amudi mai, da kuma inda ka yi mini alkawari. Yanzu ka bar wannan ƙasa nan take, ka koma ƙasarka ta ainihi.’”
I am the God of Bethel, where you anointed a pillar, where you made a vow to me. Now rise up and leave this land and return to the land of your birth.'”
14 Sai Rahila da Liyatu suka amsa suka ce, “Muna da wani rabo a gādon kayan mahaifinmu ne?
Rachel and Leah answered and said to him, “Is there any portion or inheritance for us in our father's house?
15 Ba kamar baƙi ne yake ɗaukarmu ba? Ba sayar da mu kaɗai ya yi ba, har ma ya yi amfani da abin da aka biya saboda mu.
Are we not treated by him as foreigners? For he has sold us and has also completely devoured our money.
16 Tabbatacce dukan dukiyar da Allah ya kwashe daga mahaifinmu ya zama namu da’ya’yanmu. Saboda haka ka yi duk abin da Allah ya faɗa maka.”
For all the riches that God has taken away from our father are now ours and our children's. Now then, whatever God has said to you, do it.”
17 Sa’an nan Yaƙub ya sa’ya’yansa da matansa a kan raƙuma,
Then Jacob arose and placed his sons and his wives upon the camels.
18 ya kuma kora dukan dabbobinsa, suka ja gabansa, tare da dukan abubuwan da ya samu a Faddan Aram, don su tafi wurin mahaifinsa Ishaku a ƙasar Kan’ana.
He drove all his livestock ahead of him, along with all his property, including the livestock he had acquired in Paddan Aram. Then he set out to go to his father Isaac in the land of Canaan.
19 Sa’ad da Laban ya tafi don askin tumakinsa, sai Rahila ta sace gumakan gidan mahaifinta.
When Laban had gone to shear his sheep, Rachel stole her father's household gods.
20 Yaƙub kuwa ya ruɗe Laban mutumin Aram da bai sanar da shi zai gudu ba.
Jacob also deceived Laban the Aramean, by not telling him that he was leaving.
21 Saboda haka ya gudu da dukan abin da ya mallaka, ya ƙetare Kogi, ya nufi yankin tuddan Gileyad.
So he fled with all that he had and quickly passed over the River, and headed toward the hill country of Gilead.
22 A rana ta uku, sai aka faɗa wa Laban cewa Yaƙub ya gudu.
On the third day Laban was told that Jacob had fled.
23 Sai Laban ya ɗauki danginsa tare da shi, ya bi bayan Yaƙub har kwana bakwai, ya kuma same shi a yankin tuddan Gileyad.
So he took his relatives with him and pursued him for a seven days' journey. He overtook him in the hill country of Gilead.
24 Sai Allah ya bayyana ga Laban mutumin Aram a mafarki da dare, ya ce masa, “Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu, ko mai kyau ko marar kyau.”
Now God came to Laban the Aramean in a dream at night and said to him, “Be careful that you speak to Jacob neither good nor bad.”
25 Yaƙub ya riga ya kafa tentinsa a yankin tuddan Gileyad sa’ad da Laban ya same shi. Laban da danginsa suka kafa sansani a can su ma.
Laban overtook Jacob. Now Jacob had pitched his tent in the hill country. Laban also camped with his relatives in the hill country of Gilead.
26 Sai Laban ya ce wa Yaƙub, “Me ke nan ka yi? Ka ruɗe ni, ka kuma ɗauki’ya’yana mata kamar kamammun yaƙi.
Laban said to Jacob, “What have you done, that you deceived me and carried away my daughters like prisoners of war?
27 Me ya sa ka gudu a ɓoye ka kuma ruɗe ni? Me ya sa ba ka faɗa mini don in sallame ka da farin ciki da waƙoƙi haɗe da kiɗin ganguna da garayu ba?
Why did you flee secretly and trick me and did not tell me? I would have sent you away with celebration and with songs, with tambourine and with harps.
28 Ba ka ma bari in sumbaci jikokina da’ya’yana mata in yi musu bankwana ba. Ka yi wauta.
You did not allow me to kiss my grandsons and my daughters good bye. Now you have done foolishly.
29 Ina da iko in cuce ka; amma jiya da dare Allahn mahaifinka ya faɗa mini, ‘Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu ko mai kyau ko marar kyau.’
It is in my power to do you harm, but the God of your father spoke to me last night and said, 'Be careful that you speak to Jacob neither good nor bad.'
30 Yanzu ka gudu domin kana marmari komawa gidan mahaifinka. Amma don me ka sace mini gumakana?”
Now you have gone away because you longed to return to your father's house. But why did you steal my gods?”
31 Yaƙub ya amsa wa Laban, “Na ji tsoro ne, domin na yi tsammani za ka ƙwace’ya’yanka mata daga gare ni ƙarfi da yaji.
Jacob answered and said to Laban, “Because I was afraid and thought that you would take your daughters from me by force I left secretly.
32 Amma in ka sami wani wanda yake da gumakanka, ba zai rayu ba. Kai da kanka ka duba a gaban danginmu, ko akwai wani abin da yake naka a nan tare da ni; in ka gani, ka ɗauka.” Yaƙub dai bai san cewa Rahila ta sace gumakan ba.
Whoever has stolen your gods will not continue to live. In the presence of our relatives, identify whatever with me is yours and take it.” For Jacob did not know that Rachel had stolen them.
33 Saboda haka Laban ya shiga tentin Yaƙub, ya shiga tentin Liyatu da kuma tentuna matan nan biyu bayi, amma bai sami kome ba. Bayan ya fita daga tentin Liyatu, sai ya shiga tentin Rahila.
Laban went into Jacob's tent, into Leah's tent, and into the tent of the two female servants, but he did not find them. He went out of Leah's tent and entered into Rachel's tent.
34 Rahila fa ta kwashe gumakan gidan ta sa su cikin sirdin raƙumi, ta kuma zauna a kansu. Laban ya bincika cikin kowane abu a tentin amma bai sami kome ba.
Now Rachel had taken the household gods, put them in a camel's saddle, and sat upon them. Laban searched the whole tent, but did not find them.
35 Sai Rahila ta ce wa mahaifinta, “Kada ka yi fushi, ranka yă daɗe da ban tashi tsaye a gabanka ba; gama ina al’adar mata ne.” Saboda haka ya bincika amma bai sami gumakan gidan ba.
She said to her father, “Do not be angry, my master, that I cannot stand up before you, for I am having my period.” So he searched but did not find his household gods.
36 Yaƙub ya fusata, ya kuma yi wa Laban faɗa. Ya tambayi Laban, “Mene ne laifina? Wanda zunubi na yi da kake farautata?
Jacob was angry and argued with Laban. He said to him, “What is my offense? What is my sin, that you have hotly pursued after me?
37 Yanzu da ka bincika dukan kayayyakina, me ka samu da yake na gidanka? Kawo shi nan a gaban danginka da kuma dangina, bari su zama alƙali tsakaninmu biyu.
For you have searched all my possessions. What have you found of all your household goods? Set them here before our relatives, so that they may judge between us two.
38 “Na kasance tare da kai shekaru ashirin. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuwa ci raguna daga garkunanka ba.
For twenty years I have been with you. Your ewes and your female goats have not miscarried, nor have I eaten any rams from your flocks.
39 Ban kawo dabbobinka da namun jeji suka yayyaga; na kuma ɗauki hasarar ba? Ka nemi in biya dukan abin da aka sace da rana ko da dare.
What was torn by beasts I did not bring to you. Instead, I bore the loss of it. You always made me pay for every missing animal, whether stolen by day or stolen by night.
40 Yanayin da na kasance ke nan, da rana na sha zafin rana da dare kuma na sha sanyi, ga rashin barci.
There I was; in the day the heat consumed me, and the frost by night; and I went without sleep.
41 Haka ya kasance shekaru ashirin da na yi a gidanka. Na yi maka aiki shekaru goma sha huɗu domin’ya’yanka mata biyu, na kuma yi shekaru shida domin garkunanka, ka kuma canja albashina sau goma.
These twenty years I have been in your household. I worked for you fourteen years for your two daughters, and six years for your flock. You have changed my wages ten times.
42 Da ba don Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim da kuma Tsoron Ishaku ya kasance tare da ni ba, tabbatacce da ka sallame ni hannu wofi. Amma Allah ya ga wahalata da famar hannuwana, ya kuwa tsawata maka da dare jiya.”
Unless the God of my father, the God of Abraham, and the one Isaac fears, had been with me, surely now you would have sent me away empty-handed. God has seen my oppression and how hard I worked, and he rebuked you last night.”
43 Laban ya amsa wa Yaƙub, “Matan,’ya’yana ne,’ya’yansu,’ya’yana ne, garkunan kuma garkunana ne. Dukan abin da kake gani, nawa ne. Duk da haka me zan yi a rana ta yau ga waɗannan’ya’yana mata, ko kuma ga’ya’yan da suka haifa?
Laban answered and said to Jacob, “The daughters are my daughters, the grandchildren are my grandchildren, and the flocks are my flocks. All that you see is mine. But what can I do today to these my daughters, or to their children whom they have borne?
44 Zo, bari mu ƙulla yarjejjeniya, da kai da ni, bari kuma ta kasance shaida a tsakaninmu.”
So now, let us make a covenant, you and I, and let it be for a witness between you and me.”
45 Saboda haka Yaƙub ya ɗauki dutse ya kafa yă zama al’amudi.
So Jacob took a stone and set it up as a pillar.
46 Ya ce wa danginsa. “Ku tattara waɗansu duwatsu.” Sai suka kwashe duwatsu suka tsiba, suka kuwa ci abinci a can kusa da tsibin.
Jacob said to his relatives, “Gather stones.” So they took stones and made a pile. Then they ate there by the pile.
47 Laban ya sa masa suna Yegar Sahaduta, Yaƙub kuwa ya kira shi Galeyed.
Laban called it Jegar Saha Dutha, but Jacob called it Galeed.
48 Laban ya ce, “Wannan tsibi, shi ne shaida tsakaninka da ni a yau.” Shi ya sa aka kira shi Galeyed.
Laban said, “This pile is a witness between me and you today.” Therefore its name was called Galeed.
49 Aka kuma kira shi Mizfa, domin ya ce, “Ubangiji yă sa ido tsakanin ni da kai sa’ad da muka rabu da juna.
It is also called Mizpah, because Laban said, “May Yahweh watch between you and me, when we are out of sight one from another.
50 Laban ya ce in ka wulaƙanta’ya’yana mata, ko ka auri waɗansu mata ban da’ya’yana mata, ko da yake babu wani da yake tare da mu, ka tuna cewa Allah shi ne shaida tsakaninka da ni.”
If you mistreat my daughters, or if you take any wives besides my daughters, although no one else is with us, see, God is witness between you and me.”
51 Laban ya kuma ce wa Yaƙub, “Ga wannan tsibi, ga kuma wannan al’amudin da na kafa tsakaninka da ni.
Laban said to Jacob, “Look at this pile, and look at the pillar, which I have set between you and me.
52 Wannan tsibin shi ne shaida, wannan al’amudi kuma shaida ne, cewa ba zan tsallake wannan tsibi zuwa gefenka don in cuce ka ba, kai kuma ba za ka tsallake wannan tsibi da al’amudi zuwa gefena don ka cuce ni ba.
This pile is a witness, and the pillar is a witness, that I will not pass beyond this pile to you, and that you will not pass beyond this pile and this pillar to me, to do harm.
53 Bari Allah na Ibrahim da Allah na Nahor, Allah na iyayensu, yă zama alƙali tsakaninmu.” Saboda haka Yaƙub ya yi rantsuwa da sunan Tsoron mahaifinsa Ishaku.
May the God of Abraham, and the god of Nahor, the gods of their father, judge between us.” Jacob swore by the Fear of his father Isaac.
54 Ya miƙa hadaya a can a ƙasar tudu, ya kuma gayyaci danginsa zuwa wurin cin abinci. Bayan suka ci, sai suka kwana a can.
Jacob offered a sacrifice on the mountain and called his relatives to eat a meal. They ate and spent the entire night on the mountain.
55 Da sassafe kashegari sai Laban ya sumbaci jikokinsa da’ya’yansa mata, ya sa musu albarka. Sa’an nan ya yi bankwana da su, ya koma gida.
Early in the morning Laban got up, kissed his grandsons and his daughters and blessed them. Then Laban left and returned home.