< Farawa 31 >
1 Yaƙub ya ji cewa’ya’ya Laban mazan suna cewa, “Yaƙub ya kwashe dukan abin da mahaifinmu yake da shi, ya kuma sami dukan wannan arziki daga abin da yake na mahaifinmu.”
Then heard he the words of the sons of Laban, saying, Jacob hath taken away all that belonged to our father; Yea out of what belonged to our father, hath he made all this wealth.
2 Yaƙub kuma ya lura cewa halin Laban gare shi ya canja ba kamar yadda yake a dā ba.
And Jacob looked upon the face of Laban, —and lo! it was not with him as afore-time.
3 Sai Ubangiji ya ce wa Yaƙub, “Koma ƙasar kakanninka da kuma danginka, zan kuwa kasance tare da kai.”
Then said Yahweh unto Jacob, Return unto the land of thy fathers and to thy kindred, —that I may be with thee.
4 Saboda haka Yaƙub ya aika a ce wa Rahila da Liyatu su zo jeji inda garkunan suke.
So Jacob sent, and called for Rachel and for Leah, to the field unto his flock;
5 Sai ya ce musu, “Na ga cewa halin mahaifinku gare ni ba kamar yadda dā yake ba, amma Allah na mahaifina yana tare da ni.
and said to them, Beholding, am I the face of your father, that it is not towards me as aforetime, —nevertheless, the God of my father, hath been with me;
6 Kun san cewa na yi aiki wa mahaifinku da dukan ƙarfina,
and, ye, know that with all my vigour, have I served your father.
7 duk da haka mahaifinku ya cuce ni ta wurin sauya albashina sau goma. Amma dai, Allah bai yardar masa yă yi mini lahani ba.
But, your father, hath deceived me, and hath changed my wages ten times, —yet God hath not suffered him to deal harmfully with me.
8 In ya ce, ‘Dabbare-dabbare ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi dabbare-dabbare, in kuma ya ce, ‘Masu zāne-zāne ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi ƙananan masu zāne-zāne.
If thus he saith, The speckled, shall be thy wages, then do all the flock bring forth speckled, —But if thus he saith, The ring-straked, shall be thy wages, then do all the flock bring forth ring-straked.
9 Ta haka Allah ya kwashe dabbobin mahaifinku ya ba ni.
So hath God stripped away the herds of your father, and given them to me.
10 “A lokacin ɗaukar cikin garken, na taɓa yin mafarki inda na ga bunsuran da suke barbara da garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne.
And it came to pass in the season when the flock were in heat, then lifted I mine eyes and beheld in a dream, —and lo! the he-goats that were leaping upon the flock, were ring-straked speckled and dappled.
11 Sai mala’ikan Allah ya ce mini a mafarkin, ‘Yaƙub.’ Sai na amsa na ce, ‘Ga ni.’
And the messenger of God said unto me in a dream, Jacob! and I said, Behold me!
12 Ya ce, ‘Ɗaga idanunka ka gani, dukan bunsuran da suke hawan garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne, gama na ga dukan abin da Laban yake yin maka.
Then he said Lift, I pray thee, thine eyes and behold All, the he-goats that are leaping upon the flock are ring-straked, speckled, and dappled, —for I have seen all that Laban, has been doing to thee.
13 Ni ne Allah na Betel, inda ka zuba wa al’amudi mai, da kuma inda ka yi mini alkawari. Yanzu ka bar wannan ƙasa nan take, ka koma ƙasarka ta ainihi.’”
I, am the GOD of Beth-el, where thou didst anoint a pillar, where thou didst vow to me a vow, —Now, rise, go forth out of this land, and return unto the land of thy kindred.
14 Sai Rahila da Liyatu suka amsa suka ce, “Muna da wani rabo a gādon kayan mahaifinmu ne?
Then responded Rachel and Leah, and said to him, —Have we any longer a portion or an inheritance in the house of our father?
15 Ba kamar baƙi ne yake ɗaukarmu ba? Ba sayar da mu kaɗai ya yi ba, har ma ya yi amfani da abin da aka biya saboda mu.
Are we not accounted, aliens, to him seeing that having sold us, he hath then gone on devouring, our silver?
16 Tabbatacce dukan dukiyar da Allah ya kwashe daga mahaifinmu ya zama namu da’ya’yanmu. Saboda haka ka yi duk abin da Allah ya faɗa maka.”
Surely all the riches which God hath stripped off from our father, unto us, it belongeth, and unto our sons, —Now, therefore, whatsoever God hath said unto thee, do.
17 Sa’an nan Yaƙub ya sa’ya’yansa da matansa a kan raƙuma,
So Jacob arose, —and mounted his sons and his wives on the camels;
18 ya kuma kora dukan dabbobinsa, suka ja gabansa, tare da dukan abubuwan da ya samu a Faddan Aram, don su tafi wurin mahaifinsa Ishaku a ƙasar Kan’ana.
and drave away all his herds and all his goods which he had gathered, the gains he had gained, which he had gathered in Padan-aram; that he might go in unto Isaac his father unto the land of Canaan.
19 Sa’ad da Laban ya tafi don askin tumakinsa, sai Rahila ta sace gumakan gidan mahaifinta.
Now, Laban, had gone, to shear his sheep, —so Rachel stole the household gods that belonged to her father,
20 Yaƙub kuwa ya ruɗe Laban mutumin Aram da bai sanar da shi zai gudu ba.
Thus Jacob stole away unawares to Laban, the Syrian, —in that he had not told him that he was about to flee.
21 Saboda haka ya gudu da dukan abin da ya mallaka, ya ƙetare Kogi, ya nufi yankin tuddan Gileyad.
So he fled, he—and all that he had, and he arose, and passed over the River, —and set his face towards the mountain of Gilead.
22 A rana ta uku, sai aka faɗa wa Laban cewa Yaƙub ya gudu.
And it was told Laban, on the third day, —that Jacob had fled.
23 Sai Laban ya ɗauki danginsa tare da shi, ya bi bayan Yaƙub har kwana bakwai, ya kuma same shi a yankin tuddan Gileyad.
So he took his brethren with him, and pursued after him a journey of seven days—and overtook him in the mountain of Gilead.
24 Sai Allah ya bayyana ga Laban mutumin Aram a mafarki da dare, ya ce masa, “Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu, ko mai kyau ko marar kyau.”
And God went in unto Laban the Syrian in a dream of the night, —and said to him Take heed to thyself that thou speak not with Jacob either good or bad.
25 Yaƙub ya riga ya kafa tentinsa a yankin tuddan Gileyad sa’ad da Laban ya same shi. Laban da danginsa suka kafa sansani a can su ma.
So then Laban came up with Jacob, —Jacob, having pitched his tent in the mountain, Laban, also, with his brethren pitched in the mountain of Gilead.
26 Sai Laban ya ce wa Yaƙub, “Me ke nan ka yi? Ka ruɗe ni, ka kuma ɗauki’ya’yana mata kamar kamammun yaƙi.
Then said Laban to Jacob, What hadst thou done, that thou shouldst steal away unawares to me, —and shouldst carry off my daughters, as captives of the sword?
27 Me ya sa ka gudu a ɓoye ka kuma ruɗe ni? Me ya sa ba ka faɗa mini don in sallame ka da farin ciki da waƙoƙi haɗe da kiɗin ganguna da garayu ba?
Wherefore didst thou secretly flee, and rob me, —and didst not tell me, that I might send thee away with rejoicing and with songs, with timbrel and with lyre;
28 Ba ka ma bari in sumbaci jikokina da’ya’yana mata in yi musu bankwana ba. Ka yi wauta.
and didst not suffer me to kiss my sons and my daughters? Now, hast thou done, foolishly.
29 Ina da iko in cuce ka; amma jiya da dare Allahn mahaifinka ya faɗa mini, ‘Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu ko mai kyau ko marar kyau.’
It is in the power of my hand, to deal with thee for harm, —but the God of your father, last night, spake unto me, saying, Take heed to thyself that thou speak not with Jacob, either good or bad.
30 Yanzu ka gudu domin kana marmari komawa gidan mahaifinka. Amma don me ka sace mini gumakana?”
But, now, though thou, didst even take thy journey, because thou, didst sorely long, for the house of thy father, wherefore didst thou steal away my gods?
31 Yaƙub ya amsa wa Laban, “Na ji tsoro ne, domin na yi tsammani za ka ƙwace’ya’yanka mata daga gare ni ƙarfi da yaji.
And Jacob answered and said unto Laban, —Because I was afraid, for I said, Lest thou take by force thy daughters from me!
32 Amma in ka sami wani wanda yake da gumakanka, ba zai rayu ba. Kai da kanka ka duba a gaban danginmu, ko akwai wani abin da yake naka a nan tare da ni; in ka gani, ka ɗauka.” Yaƙub dai bai san cewa Rahila ta sace gumakan ba.
He with whom thou find thy gods, shall not live! Before our brethren, note thou for thyself what is with me and take what is thine. Neither did Jacob know that, Rachel, had stolen them.
33 Saboda haka Laban ya shiga tentin Yaƙub, ya shiga tentin Liyatu da kuma tentuna matan nan biyu bayi, amma bai sami kome ba. Bayan ya fita daga tentin Liyatu, sai ya shiga tentin Rahila.
Then entered Laban into the tent of Jacob and into the tent of Leah and into the tent of the two handmaids, and found nothing, —then went he forth out of the tent of Leah, and entered into the tent of Rachel.
34 Rahila fa ta kwashe gumakan gidan ta sa su cikin sirdin raƙumi, ta kuma zauna a kansu. Laban ya bincika cikin kowane abu a tentin amma bai sami kome ba.
Now Rachel, had taken the household gods and put them in the basket-saddle of the camel, and taken her seat upon them. And Laban felt about throughout all the tent, and found them not.
35 Sai Rahila ta ce wa mahaifinta, “Kada ka yi fushi, ranka yă daɗe da ban tashi tsaye a gabanka ba; gama ina al’adar mata ne.” Saboda haka ya bincika amma bai sami gumakan gidan ba.
And she said unto her father, Let it not be vexing in the eyes of my lord that I cannot rise up at thy presence, for, the way of women, is upon me. So he made search, but found not the household gods,
36 Yaƙub ya fusata, ya kuma yi wa Laban faɗa. Ya tambayi Laban, “Mene ne laifina? Wanda zunubi na yi da kake farautata?
And it was vexing to Jacob and he contended with Laban, —and Jacob responded and said to Laban, What was my trespass, what my sin, that thou shouldst have come burning after me?
37 Yanzu da ka bincika dukan kayayyakina, me ka samu da yake na gidanka? Kawo shi nan a gaban danginka da kuma dangina, bari su zama alƙali tsakaninmu biyu.
Now that thou hast felt about among all my goods, what hast thou found of the goods of thine own house? Set it out here, right before my brethren and thy brethren, —that they may give sentence betwixt us two.
38 “Na kasance tare da kai shekaru ashirin. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuwa ci raguna daga garkunanka ba.
This twenty years’ time, have, I, been with thee—Thy ewes and thy she-goats, have not cast their young, —And the rams of thy flock, have I not eaten,
39 Ban kawo dabbobinka da namun jeji suka yayyaga; na kuma ɗauki hasarar ba? Ka nemi in biya dukan abin da aka sace da rana ko da dare.
The torn, have I not brought in unto thee—I bare the loss, At my hand, didst thou require it, —Stolen by day, or stolen by night.
40 Yanayin da na kasance ke nan, da rana na sha zafin rana da dare kuma na sha sanyi, ga rashin barci.
Thus have I been—By day, drought hath consumed me, And, frost, by, night, —So that my sleep fled away from mine eyes.
41 Haka ya kasance shekaru ashirin da na yi a gidanka. Na yi maka aiki shekaru goma sha huɗu domin’ya’yanka mata biyu, na kuma yi shekaru shida domin garkunanka, ka kuma canja albashina sau goma.
This, hath been my lot twenty years in thy house, —I served thee fourteen years for thy two daughters, And six years for thy sheep—And thou didst change my wages ten times: —
42 Da ba don Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim da kuma Tsoron Ishaku ya kasance tare da ni ba, tabbatacce da ka sallame ni hannu wofi. Amma Allah ya ga wahalata da famar hannuwana, ya kuwa tsawata maka da dare jiya.”
But that the God of my father—The God of Abraham, and the Dread of Isaac—Proved to be mine, Surely even now, empty, hadst thou let me go? My humiliation and the wearying toil of my hands, God had seen, And therefore gave sentence last night!
43 Laban ya amsa wa Yaƙub, “Matan,’ya’yana ne,’ya’yansu,’ya’yana ne, garkunan kuma garkunana ne. Dukan abin da kake gani, nawa ne. Duk da haka me zan yi a rana ta yau ga waɗannan’ya’yana mata, ko kuma ga’ya’yan da suka haifa?
Then responded Laban and said unto Jacob—the daughters, are my daughters, And the sons, are my sons, And the sheep are my sheep, And, all that, thou, beholdest, To me doth it belong! But to my daughters, what can I do to these this day, Or to their sons whom they have borne?
44 Zo, bari mu ƙulla yarjejjeniya, da kai da ni, bari kuma ta kasance shaida a tsakaninmu.”
Now, therefore, come on! Let us solemnise a covenant, I and thou, —So shall it be a witness betwixt me and thee.
45 Saboda haka Yaƙub ya ɗauki dutse ya kafa yă zama al’amudi.
So Jacob took a stone, —and set it up as a pillar.
46 Ya ce wa danginsa. “Ku tattara waɗansu duwatsu.” Sai suka kwashe duwatsu suka tsiba, suka kuwa ci abinci a can kusa da tsibin.
Then said Jacob to his brethren—Gather stones. And they took stones and made a heap, —and they did eat there, by the heap.
47 Laban ya sa masa suna Yegar Sahaduta, Yaƙub kuwa ya kira shi Galeyed.
And Laban called it, Jegar-sahadutha, —but, Jacob, called it, Galeed.
48 Laban ya ce, “Wannan tsibi, shi ne shaida tsakaninka da ni a yau.” Shi ya sa aka kira shi Galeyed.
Then said Laban: This heap, be witness betwixt me, and thee, to-day. For this cause, is the name thereof called Galeed;
49 Aka kuma kira shi Mizfa, domin ya ce, “Ubangiji yă sa ido tsakanin ni da kai sa’ad da muka rabu da juna.
also, The Watch Tower, as to which it is said, Yahweh watch betwixt me and thee, when we are parted one from another.
50 Laban ya ce in ka wulaƙanta’ya’yana mata, ko ka auri waɗansu mata ban da’ya’yana mata, ko da yake babu wani da yake tare da mu, ka tuna cewa Allah shi ne shaida tsakaninka da ni.”
If thou oppress my daughters, or if thou take wives besides my daughters, —there may be no man with us—see! God, be witness betwixt me, and thee!
51 Laban ya kuma ce wa Yaƙub, “Ga wannan tsibi, ga kuma wannan al’amudin da na kafa tsakaninka da ni.
And Laban said to Jacob—Behold this heap, and behold this pillar, which I have set betwixt me, and thee:
52 Wannan tsibin shi ne shaida, wannan al’amudi kuma shaida ne, cewa ba zan tsallake wannan tsibi zuwa gefenka don in cuce ka ba, kai kuma ba za ka tsallake wannan tsibi da al’amudi zuwa gefena don ka cuce ni ba.
A witness, be this heap, and, a witness, the pillar, —That, I, am not to pass, unto thee, over this heap, And, thou, art not to pass, unto me, over this heap and this pillar for harm.
53 Bari Allah na Ibrahim da Allah na Nahor, Allah na iyayensu, yă zama alƙali tsakaninmu.” Saboda haka Yaƙub ya yi rantsuwa da sunan Tsoron mahaifinsa Ishaku.
The Gods of Abraham and the Gods of Nahor judge betwixt us—the Gods of their fathers. And Jacob sware by the Dread of his father Isaac:
54 Ya miƙa hadaya a can a ƙasar tudu, ya kuma gayyaci danginsa zuwa wurin cin abinci. Bayan suka ci, sai suka kwana a can.
and Jacob offered sacrifice in the mountain, and called on his brethren to eat bread. So they did eat bread, and tarried the night in the mountain.
55 Da sassafe kashegari sai Laban ya sumbaci jikokinsa da’ya’yansa mata, ya sa musu albarka. Sa’an nan ya yi bankwana da su, ya koma gida.
And Laban rose up early in the morning, and kissed his sons and his daughters, and blessed them: and Laban went his way and returned to his place.