< Farawa 31 >
1 Yaƙub ya ji cewa’ya’ya Laban mazan suna cewa, “Yaƙub ya kwashe dukan abin da mahaifinmu yake da shi, ya kuma sami dukan wannan arziki daga abin da yake na mahaifinmu.”
And he heard the words of Laban's sons, saying, Jacob hath taken away all that was our father's, and of that which was our father's hath he gotten all this wealth.
2 Yaƙub kuma ya lura cewa halin Laban gare shi ya canja ba kamar yadda yake a dā ba.
And Jacob beheld the countenance of Laban, and, behold, it was not toward him as before.
3 Sai Ubangiji ya ce wa Yaƙub, “Koma ƙasar kakanninka da kuma danginka, zan kuwa kasance tare da kai.”
And the Lord said unto Jacob, Return unto the land of thy fathers, and to thy birthplace; and I will be with thee.
4 Saboda haka Yaƙub ya aika a ce wa Rahila da Liyatu su zo jeji inda garkunan suke.
And Jacob sent and called Rachel and Leah to the field unto his flock.
5 Sai ya ce musu, “Na ga cewa halin mahaifinku gare ni ba kamar yadda dā yake ba, amma Allah na mahaifina yana tare da ni.
And he said unto them, I see your father's countenance, that it is not toward me as before; but the God of my father hath been with me.
6 Kun san cewa na yi aiki wa mahaifinku da dukan ƙarfina,
And ye know well that with all my power I have served your father.
7 duk da haka mahaifinku ya cuce ni ta wurin sauya albashina sau goma. Amma dai, Allah bai yardar masa yă yi mini lahani ba.
And your father hath deceived me, and changed my wages ten times: but God suffered him not to do me evil.
8 In ya ce, ‘Dabbare-dabbare ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi dabbare-dabbare, in kuma ya ce, ‘Masu zāne-zāne ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi ƙananan masu zāne-zāne.
If he said thus, The speckled shall be thy wages: then bore all the flocks speckled: and if he said thus, The ring-streaked shall be thy reward; then bore all the flocks ring-streaked.
9 Ta haka Allah ya kwashe dabbobin mahaifinku ya ba ni.
Thus God took away the cattle of your father, and gave them to me.
10 “A lokacin ɗaukar cikin garken, na taɓa yin mafarki inda na ga bunsuran da suke barbara da garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne.
And it came to pass at the time that the flocks conceived, that I lifted up my eyes, and saw in a dream, and, behold, the rams which leaped upon the flocks were ring-streaked, speckled, and grizzled.
11 Sai mala’ikan Allah ya ce mini a mafarkin, ‘Yaƙub.’ Sai na amsa na ce, ‘Ga ni.’
And an angel of God spoke unto me in the dream, Jacob: and I said, Here am I.
12 Ya ce, ‘Ɗaga idanunka ka gani, dukan bunsuran da suke hawan garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne, gama na ga dukan abin da Laban yake yin maka.
And he said, Lift up now thy eyes and see, all the rams which leap upon the flocks are ring-streaked, speckled, and grizzled; for I have seen all that Laban doth unto thee.
13 Ni ne Allah na Betel, inda ka zuba wa al’amudi mai, da kuma inda ka yi mini alkawari. Yanzu ka bar wannan ƙasa nan take, ka koma ƙasarka ta ainihi.’”
I am the God of Beth-el, where thou anointedst a pillar, where thou madest unto me a vow: now arise, get thee out from this land, and return unto the land of thy birth.
14 Sai Rahila da Liyatu suka amsa suka ce, “Muna da wani rabo a gādon kayan mahaifinmu ne?
And Rachel and Leah answered and said unto him, Is there yet any portion or inheritance for us in our father's house?
15 Ba kamar baƙi ne yake ɗaukarmu ba? Ba sayar da mu kaɗai ya yi ba, har ma ya yi amfani da abin da aka biya saboda mu.
Were we not counted of him as strangers? for he hath sold us; and he hath quite consumed also our money.
16 Tabbatacce dukan dukiyar da Allah ya kwashe daga mahaifinmu ya zama namu da’ya’yanmu. Saboda haka ka yi duk abin da Allah ya faɗa maka.”
For all the riches which God hath taken from our father, that is ours, and our children's; now then, whatsoever God hath said unto thee, do.
17 Sa’an nan Yaƙub ya sa’ya’yansa da matansa a kan raƙuma,
Then Jacob rose up, and set his sons and his wives upon camels;
18 ya kuma kora dukan dabbobinsa, suka ja gabansa, tare da dukan abubuwan da ya samu a Faddan Aram, don su tafi wurin mahaifinsa Ishaku a ƙasar Kan’ana.
And he led away all his cattle, and all his goods which he had gotten, the cattle of his acquiring, which he had gotten in Padan-aram, to go to Isaac his father into the land of Canaan.
19 Sa’ad da Laban ya tafi don askin tumakinsa, sai Rahila ta sace gumakan gidan mahaifinta.
And Laban was gone to shear his sheep; and Rachel stole the images that were her father's.
20 Yaƙub kuwa ya ruɗe Laban mutumin Aram da bai sanar da shi zai gudu ba.
And Jacob stole away unawares to Laban the Syrian, by not letting him know that he was going to flee.
21 Saboda haka ya gudu da dukan abin da ya mallaka, ya ƙetare Kogi, ya nufi yankin tuddan Gileyad.
And he fled with all that he had; and he rose up, and passed over the river, and set his face toward the mount Gilead.
22 A rana ta uku, sai aka faɗa wa Laban cewa Yaƙub ya gudu.
And it was told to Laban on the third day that Jacob was fled.
23 Sai Laban ya ɗauki danginsa tare da shi, ya bi bayan Yaƙub har kwana bakwai, ya kuma same shi a yankin tuddan Gileyad.
And he took his brethren with him, and pursued after him a seven days' journey; and he overtook him at the mount of Gilead.
24 Sai Allah ya bayyana ga Laban mutumin Aram a mafarki da dare, ya ce masa, “Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu, ko mai kyau ko marar kyau.”
And God came to Laban, the Syrian, in a dream of the night, and said unto him, Take thou heed that thou speak not to Jacob either good or bad.
25 Yaƙub ya riga ya kafa tentinsa a yankin tuddan Gileyad sa’ad da Laban ya same shi. Laban da danginsa suka kafa sansani a can su ma.
Then Laban overtook Jacob; now Jacob had pitched his tent on the mount, and Laban with his brethren pitched on the mount of Gilead.
26 Sai Laban ya ce wa Yaƙub, “Me ke nan ka yi? Ka ruɗe ni, ka kuma ɗauki’ya’yana mata kamar kamammun yaƙi.
And Laban said to Jacob, What hast thou done, that thou hast stolen away unawares to me, and led away my daughters, as captives taken with the sword.
27 Me ya sa ka gudu a ɓoye ka kuma ruɗe ni? Me ya sa ba ka faɗa mini don in sallame ka da farin ciki da waƙoƙi haɗe da kiɗin ganguna da garayu ba?
Wherefore didst thou flee away secretly, and steal away from me; and why didst thou not tell me, that I might have sent thee away with mirth, and with songs, with tabret, and with harp?
28 Ba ka ma bari in sumbaci jikokina da’ya’yana mata in yi musu bankwana ba. Ka yi wauta.
And [why] hast thou not suffered me to kiss my sons and my daughters? now thou hast acted foolishly in so doing.
29 Ina da iko in cuce ka; amma jiya da dare Allahn mahaifinka ya faɗa mini, ‘Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu ko mai kyau ko marar kyau.’
It is in the power of my hand to do you hurt; but the God of your father spoke unto me yesternight, saying, Take thou heed that thou speak not to Jacob either good or bad.
30 Yanzu ka gudu domin kana marmari komawa gidan mahaifinka. Amma don me ka sace mini gumakana?”
And now, thou wouldst needs be gone, because thou greatly longedst after thy father's house; [yet] wherefore hast thou stolen my gods.
31 Yaƙub ya amsa wa Laban, “Na ji tsoro ne, domin na yi tsammani za ka ƙwace’ya’yanka mata daga gare ni ƙarfi da yaji.
And Jacob answered and said to Laban, Because I was afraid, for I said, Peradventure thou wouldst take by force thy daughters from me.
32 Amma in ka sami wani wanda yake da gumakanka, ba zai rayu ba. Kai da kanka ka duba a gaban danginmu, ko akwai wani abin da yake naka a nan tare da ni; in ka gani, ka ɗauka.” Yaƙub dai bai san cewa Rahila ta sace gumakan ba.
With whomsoever thou findest thy gods, let him not live; before our brethren seek out thou what is thine with me, and take it to thee; but Jacob knew not that Rachel had stolen them.
33 Saboda haka Laban ya shiga tentin Yaƙub, ya shiga tentin Liyatu da kuma tentuna matan nan biyu bayi, amma bai sami kome ba. Bayan ya fita daga tentin Liyatu, sai ya shiga tentin Rahila.
And Laban went into the tent of Jacob, and into the tent of Leah, and into the tent of the two maid-servants; but he found nothing; he then went out of the tent of Leah, and entered into Rachel's tent.
34 Rahila fa ta kwashe gumakan gidan ta sa su cikin sirdin raƙumi, ta kuma zauna a kansu. Laban ya bincika cikin kowane abu a tentin amma bai sami kome ba.
Now Rachel had taken the images, and put them in the saddle-cushion of the camel, and sat upon them; and Laban searched all the tent, and found nothing.
35 Sai Rahila ta ce wa mahaifinta, “Kada ka yi fushi, ranka yă daɗe da ban tashi tsaye a gabanka ba; gama ina al’adar mata ne.” Saboda haka ya bincika amma bai sami gumakan gidan ba.
And she said to her father, Let it not displease my lord that I cannot rise up before thee; for the custom of women is upon me; and thus he searched, but found not the images.
36 Yaƙub ya fusata, ya kuma yi wa Laban faɗa. Ya tambayi Laban, “Mene ne laifina? Wanda zunubi na yi da kake farautata?
Now Jacob became wroth, and quarrelled with Laban; and Jacob answered and said to Laban, What is my trespass? what is my sin, that thou hast so hotly pursued after me?
37 Yanzu da ka bincika dukan kayayyakina, me ka samu da yake na gidanka? Kawo shi nan a gaban danginka da kuma dangina, bari su zama alƙali tsakaninmu biyu.
Although thou hast searched all my goods, what hast thou found of all the articles of thy household? set it here before my brethren and thy brethren, that they may judge between us both.
38 “Na kasance tare da kai shekaru ashirin. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuwa ci raguna daga garkunanka ba.
These twenty years have I been with thee: thy ewes and thy she-goats have not cast their young; and the rams of thy flock have I not eaten.
39 Ban kawo dabbobinka da namun jeji suka yayyaga; na kuma ɗauki hasarar ba? Ka nemi in biya dukan abin da aka sace da rana ko da dare.
That which was torn of beasts I brought not unto thee; I had to bear the loss of it, of my hand didst thou require it, whatever was stolen by day, or stolen by night.
40 Yanayin da na kasance ke nan, da rana na sha zafin rana da dare kuma na sha sanyi, ga rashin barci.
[Where] I was in the day the heat consumed me, and the frost by night; and my sleep departed from my eyes.
41 Haka ya kasance shekaru ashirin da na yi a gidanka. Na yi maka aiki shekaru goma sha huɗu domin’ya’yanka mata biyu, na kuma yi shekaru shida domin garkunanka, ka kuma canja albashina sau goma.
These twenty years have I been in thy house; I have served thee fourteen years for thy two daughters, and six years for thy flocks: and thou hast changed my wages ten times.
42 Da ba don Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim da kuma Tsoron Ishaku ya kasance tare da ni ba, tabbatacce da ka sallame ni hannu wofi. Amma Allah ya ga wahalata da famar hannuwana, ya kuwa tsawata maka da dare jiya.”
Except the God of my father, the God of Abraham, and the Fear of Isaac, had been with me, surely thou hadst now sent me away empty; my affliction and the labor of my hands God hath seen, and decided yesternight.
43 Laban ya amsa wa Yaƙub, “Matan,’ya’yana ne,’ya’yansu,’ya’yana ne, garkunan kuma garkunana ne. Dukan abin da kake gani, nawa ne. Duk da haka me zan yi a rana ta yau ga waɗannan’ya’yana mata, ko kuma ga’ya’yan da suka haifa?
And Laban answered and said unto Jacob, The daughters are my daughters, and the children are my children, and the flocks are my flocks, and all that thou seest is mine; but as to my daughters, what can I do unto them this day, or unto their children whom they have born?
44 Zo, bari mu ƙulla yarjejjeniya, da kai da ni, bari kuma ta kasance shaida a tsakaninmu.”
And now, come thou, let us make a covenant, I and thou; and let it be for a witness between me and thee.
45 Saboda haka Yaƙub ya ɗauki dutse ya kafa yă zama al’amudi.
And Jacob took a stone, and set it up for a pillar.
46 Ya ce wa danginsa. “Ku tattara waɗansu duwatsu.” Sai suka kwashe duwatsu suka tsiba, suka kuwa ci abinci a can kusa da tsibin.
And Jacob said unto his brethren, Gather stones; and they took stones, and made a heap; and they ate there upon the heap.
47 Laban ya sa masa suna Yegar Sahaduta, Yaƙub kuwa ya kira shi Galeyed.
And Laban called it Yegar-sahadutha; but Jacob called it Galed.
48 Laban ya ce, “Wannan tsibi, shi ne shaida tsakaninka da ni a yau.” Shi ya sa aka kira shi Galeyed.
And Laban said, This heap is a witness between me and thee this day; therefore called he its name Galed;
49 Aka kuma kira shi Mizfa, domin ya ce, “Ubangiji yă sa ido tsakanin ni da kai sa’ad da muka rabu da juna.
And Mitzpah; for he said, The Lord shall watch between me and thee, when we are absent one from the other;
50 Laban ya ce in ka wulaƙanta’ya’yana mata, ko ka auri waɗansu mata ban da’ya’yana mata, ko da yake babu wani da yake tare da mu, ka tuna cewa Allah shi ne shaida tsakaninka da ni.”
If thou shouldst afflict my daughters, or if thou shouldst take other wives besides my daughters, when there is no man with us: see, God is witness between me and thee.
51 Laban ya kuma ce wa Yaƙub, “Ga wannan tsibi, ga kuma wannan al’amudin da na kafa tsakaninka da ni.
And Laban said to Jacob, Behold this heap, and behold this pillar, which I have cast up between me and thee;
52 Wannan tsibin shi ne shaida, wannan al’amudi kuma shaida ne, cewa ba zan tsallake wannan tsibi zuwa gefenka don in cuce ka ba, kai kuma ba za ka tsallake wannan tsibi da al’amudi zuwa gefena don ka cuce ni ba.
Witness be this heap and witness be this pillar, that I will not pass by this heap, and that thou shalt not pass unto me by this heap and this pillar, for evil.
53 Bari Allah na Ibrahim da Allah na Nahor, Allah na iyayensu, yă zama alƙali tsakaninmu.” Saboda haka Yaƙub ya yi rantsuwa da sunan Tsoron mahaifinsa Ishaku.
The God of Abraham and the God of Nachor shall judge between us, the God of their father; but Jacob swore by the Fear of his father Isaac.
54 Ya miƙa hadaya a can a ƙasar tudu, ya kuma gayyaci danginsa zuwa wurin cin abinci. Bayan suka ci, sai suka kwana a can.
Then Jacob slew some cattle upon the mount, and called his brethren to eat bread; and they did eat bread, and tarried all night on the mount.
55 Da sassafe kashegari sai Laban ya sumbaci jikokinsa da’ya’yansa mata, ya sa musu albarka. Sa’an nan ya yi bankwana da su, ya koma gida.
And early in the morning Laban rose up, and kissed his sons and his daughters and blessed them; and Laban departed, and returned unto his own place.