< Farawa 30 >
1 Sa’ad da Rahila ta ga cewa ba tă haifa wa Yaƙub’ya’ya ba, sai ta fara kishin’yar’uwarta. Saboda haka ta ce wa Yaƙub, “Ka ba ni’ya’ya, ko kuwa in mutu!”
Kad nu Rahēle redzēja, ka tā Jēkabam nedzemdēja, tad tā apskauda savu māsu un sacīja uz Jēkabu: dabū man bērnus, bet ja ne, tad man jāmirst.
2 Yaƙub ya fusata da ita ya ce, “Ina a matsayin Allah ne wanda ya hana ke samun’ya’ya?”
Tad Jēkabs apskaitās uz Rahēli un sacīja: vai es esmu Dieva vietā, kas tev miesas augļus liedzis?
3 Sa’an nan ta ce, “Ga Bilha, mai baiwata, ka kwana da ita don tă haifa mini’ya’ya, ta gare ta kuwa ni ma in gina iyali.”
Un tā sacīja: redzi, še ir mana kalpone Bilha, ej pie tās, ka tā uz manu klēpi dzemdē, un es arīdzan caur viņu augļojos.
4 Saboda haka ta ba shi baranyarta Bilha tă zama matarsa. Yaƙub kuwa ya kwana da ita,
Un viņa tam deva Bilu, savu kalponi par sievu, un Jēkabs gāja pie tās.
5 ta kuwa yi ciki, ta kuma haifi ɗa.
Un Bilha tapa grūta un dzemdēja Jēkabam dēlu.
6 Sa’an nan Rahila ta ce, “Allah ya baratar da ni; ya saurari roƙona ya kuma ba ni ɗa.” Saboda wannan ta ba shi suna Dan.
Tad Rahēle sacīja: Dievs man tiesu ir iznesis un arī manu balsi paklausījis un man dēlu devis. Tādēļ tā viņa vārdu nosauca Danu.
7 Baranyar Rahila ta sāke yin ciki ta kuma haifi wa Yaƙub ɗa na biyu.
Un Bilha, Rahēles kalpone, tapa atkal grūta un dzemdēja Jēkabam otru dēlu.
8 Sai Rahila ta ce, “Na yi kokawa sosai da’yar’uwata, na kuwa yi nasara.” Saboda haka ta kira shi Naftali.
Tad Rahēle sacīja: Dieva cīnīšanos esmu cīnījusies ar savu māsu un arī uzvarējusi, - un nosauca viņa vārdu Naftali.
9 Sa’ad da Liyatu ta ga cewa ta daina haihuwa, sai ta ɗauki mai hidimarta Zilfa ta ba da ita ga Yaƙub tă zama matarsa.
Kad nu Lea redzēja, ka bija mitējusies dzemdēt, tad tā arīdzan ņēma savu kalponi Zilfu un to Jēkabam deva par sievu.
10 Baranyar Liyatu, Zilfa ta haifa wa Yaƙub ɗa.
Un Zilfa, Leas kalpone, dzemdēja Jēkabam dēlu.
11 Sai Liyatu ta ce, “Na yi sa’a!” Saboda haka ta ba shi suna Gad.
Tad Lea sacīja: laime, - un nosauca viņa vārdu Gadu.
12 Zilfa baranyar Liyatu ta haifa wa Yaƙub ɗa na biyu.
Un Zilfa, Leas kalpone, dzemdēja Jēkabam otru dēlu.
13 Sai Liyatu ta ce, “Ni mai farin ciki ce! Mata za su ce da ni mai farin ciki.” Saboda haka ta sa masa suna Asher.
Tad Lea sacīja: labi man, jo meitas mani teiks svētīgu, - un tā nosauca viņa vārdu Ašeru.
14 A lokacin girbin alkama, sai Ruben ya je jeji ya ɗebo manta-uwa ya kawo wa mahaifiyarsa Liyatu. Sai Rahila ta ce wa Liyatu, “Ina roƙonki ki ɗan sam mini manta-uwa ɗanki.”
Un Rūbens gāja kviešu pļaujamā laikā un atrada dudaīm (mīlestības ābols) laukā un atnesa tos Leai, savai mātei, un Rahēle sacīja uz Leū: dod man jel no tava dēla dudaīm.
15 Amma ta ce mata, “Bai ishe ki ba ne da kika ƙwace mijina? Yanzu kuma kina so ki ƙwace manta-uwa na yarona?” Sai Rahila ta ce “Shi ke nan, mijina zai iya kwana da ke yau saboda manta-uwa na ɗanki.”
Un viņa uz to sacīja: vai tā ir maza lieta, ka tu manu vīru esi atņēmusi, un tu arī mana dēla dudaīm gribi ņemt? Tad Rahēle sacīja: tam būs šo nakti pie tevis gulēt par tava dēla dudaīm.
16 Saboda haka sa’ad da Yaƙub ya dawo daga jeji a wannan yamma sai Liyatu ta fito ta tarye shi. Ta ce, “Dole ka kwana da ni, na yi hayarka da manta-uwa na ɗana.” Saboda haka ya kwana da ita a wannan dare.
Kad nu Jēkabs vakarā no lauka nāca, tad Lea tam izgāja pretī un sacīja: tev būs nākt pie manis, jo es tevi ar maksu esmu saderējusi par sava dēla dudaīm. Un viņš pie tās gulēja tanī naktī.
17 Allah ya saurari Liyatu, ta kuwa yi ciki ta kuma haifa wa Yaƙub ɗa na biyar.
Un Dievs paklausīja Leū, un tā tapa grūta un dzemdēja Jēkabam piekto dēlu.
18 Sai Liyatu ta ce, “Allah ya sāka mini saboda na ba da mai hidimata ga mijina.” Saboda haka ta ba shi suna Issakar.
Tad Lea sacīja: Dievs man to atmaksājis, ka es savam vīram esmu devusi savu kalponi, - un tā nosauca viņa vārdu Īsašaru.
19 Liyatu ta sāke yin ciki ta kuma haifa wa Yaƙub ɗa na shida.
Un Lea tapa atkal grūta un dzemdēja Jēkabam sesto dēlu.
20 Sai Liyatu ta ce, “Allah ya ba ni kyauta mai daraja. A wannan lokaci mijina zai darajarta ni, domin na haifa masa’ya’ya maza shida.” Saboda haka ta ba shi suna Zebulun.
Tad Lea sacīja: Dievs mani apdāvinājis ar labu dāvanu, nu mans vīrs pie manis dzīvos, tāpēc, ka es viņam esmu dzemdējusi sešus dēlus - un tā nosauca viņa vārdu Zebulonu.
21 Daga baya ta haifi’ya ta kuwa ba ta suna Dina.
Un pēc tam viņa dzemdēja meitu un nosauca viņas vārdu Dinu.
22 Sai Allah ya tuna da Rahila; ya saurare ta ya kuma buɗe mahaifarta.
Un Dievs pieminēja Rahēli un paklausīja viņu un darīja viņu auglīgu.
23 Sai ta yi ciki ta kuma haifi ɗa ta ce, “Allah ya ɗauke mini kunyata.”
Un viņa tapa grūta un dzemdēja dēlu un sacīja: Dievs manu apsmieklu no manis atņēmis.
24 Ta ba shi suna Yusuf, ta kuma ce, “Bari Ubangiji yă ƙara mini wani ɗa.”
Un tā nosauca viņa vārdu Jāzepu, sacīdama: lai Tas Kungs mani apdāvina vēl ar citu dēlu.
25 Bayan Rahila ta haifi Yusuf, sai Yaƙub ya ce wa Laban, “Ka sallame ni don in koma ƙasata.
Un notikās, kad Rahēle Jāzepu bija dzemdējusi, tad Jēkabs sacīja uz Lābanu: atlaid mani, ka es noeju uz savu vietu savā zemē,
26 Ba ni matana da’ya’yana, waɗanda na bauta maka dominsu, zan kuwa tafi. Ka dai san yadda na bauta maka.”
Dod man manas sievas un manus bērnus, kuru dēļ tev esmu kalpojis, tad es iešu, jo tu gan zini to kalpošanu, ko tev esmu kalpojis.
27 Amma Laban ya ce masa, “In na sami tagomashi daga gare ka, ina roƙonka ka zauna. Na gane ta wurin duba cewaUbangiji ya albarkace ni saboda kai.”
Un Lābans uz to sacīja: kaut es būtu atradis žēlastību tavās acīs! - es esmu nopratis, ka Tas Kungs mani tevis dēļ ir svētījis.
28 Ya ƙara da cewa, “Faɗa albashinka, zan kuwa biya shi.”
Un viņš sacīja: prasi savu algu no manis, tad es to došu.
29 Yaƙub ya ce masa, “Ka dai san yadda na yi maka aiki da kuma yadda dabbobinka suka yi yawa a hannuna.
Un tas uz viņu sacīja: tu zini, kā es tev esmu kalpojis, un kā tavi lopi pie manis ir izdevušies.
30 Kaɗan da kake da shi kafin zuwata ya ƙaru sosai, kuma Ubangiji ya albarkace ka a duk inda na tafi. Amma yanzu, yaushe zan yi wani abu domin gidana ni ma?”
Jo priekš manas atnākšanas tev bija mazums, un tas ir lielā pulkā vairojies, un Tas Kungs tevi svētījis caur maniem soļiem; un nu, kad tad man būs apgādāt savu namu?
31 Sai Laban ya yi tambaya, “Me zan ba ka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Kada ka ba ni wani abu. Amma in za ka yi mini abu guda ɗaya, zan ci gaba da kiwon garkunanka, ina kuma lura da su.
Un viņš sacīja: ko lai tev dodu? Tad Jēkabs sacīja: tev man nekā nav jādod; ja tu man šo darīsi, tad es atkal ganīšu un sargāšu tavas avis.
32 Bari in ratsa cikin dukan garkunanka yau in fid da masu dabbare-dabbare da tumaki babare-babare, da kowane ɗan rago baƙi, da dabbare-dabbare da babare-babare na awaki daga ciki, waɗannan ne za su zama ladana.
Es izstaigāšu šodien pa visu tavu ganāmo pulku un atšķiršu no turienes visus raibos un lāsainos un visus melnos starp jēriem un visus lāsainos un raibos starp kazām, - un tās būs man par algu.
33 Gaskiyata kuwa za tă zama mini shaida nan gaba, duk sa’ad da ka bincika a kan albashin da ka biya ni. Duk akuyar da take tawa da ba dabbare-dabbare ko babare-babare, ko ɗan ragon da ba baƙi ba, zai kasance sata na yi.”
Tad mana taisnība liecinās par mani nākamās dienās, kad tu nāksi, manu algu raudzīt: viss, kas nav raibs un lāsains starp kazām un melns starp jēriem, to es būšu zadzis.
34 Sai Laban ya ce, “Na yarda. Bari yă zama yadda ka faɗa.”
Tad Lābans sacīja: redzi, lai jel notiek pēc tava vārda.
35 A wannan rana ya ware dukan bunsurai da suke dabbare-dabbare da masu zāne-zāne, da dukan awakin da suke dabbare-dabbare (duka da suke da fari-fari a jikinsu), da dukan baƙaƙen tumaki, ya sa su a hannun’ya’yansa maza.
Un viņš atšķīra tanī dienā tos lāsainos un raibos āžus, un visas lāsainās un raibās kazas, visu, pie kā bija baltums, un visu, kas bija melns starp jēriem, un viņš tos iedeva savu bērnu rokā;
36 Sa’an nan ya sa nisan tafiya kwana uku tsakaninsa da Yaƙub, yayinda Yaƙub ya ci gaba da lura da sauran garkunan Laban Yaƙub.
Un lika starpu treju dienu gājumā starp sevi un Jēkabu. Un Jēkabs ganīja Lābana citas avis.
37 Yaƙub ya samo ɗanyen reshen itatuwan aduruku, da na katambiri, da na durumi, ya ɓare ya bar fararen cikin katakon rassan.
Tad Jēkabs ņēma rīkstes no zaļām apsēm un mandeļu kokiem un kļavām, un nodrāza tām baltas strīpas, atklādams to baltumu pie tām rīkstēm.
38 Sa’an nan ya zuba ɓararre rassan cikin dukan kwamame na banruwa saboda su kasance a gaban garkunan sa’ad da suka zo shan ruwa. A sa’ad da garkunan suke barbara suka kuma zo shan ruwa,
Un tos kociņus, ko bija nomizojis, viņš ielika ūdens silēs un dzeramos traukos avīm priekšā, ka tās nākdamas dzert apietos.
39 sai su yi barbara a gaban rassan. Sai kuwa su haifi ƙanana masu zāne dabbare-dabbare, ko babare-babare ko masu zāne-zāne.
Un tās avis apgājās pār tām rīkstēm, un vedās strīpainas, lāsainas un raibas.
40 Sai Yaƙub yă ware ƙananan garken dabam, amma sai yă sa sauran su fuskanci dabbobin da suke dabbare-dabbare da kuma baƙaƙe da suke na Laban. Ta haka ya ware garkuna dabam domin kansa bai kuwa haɗa su da dabbobin Laban ba.
Un Jēkabs šķīra tos jērus, un lika tām mātēm skatīties uz tām strīpainām un melnām starp Lābana avīm, un lika savus ganāmos pulkus atsevišķi, un nelika tos pie Lābana avīm.
41 A duk sa’ad da ƙarfafa dabbobi mata suke barbara, Yaƙub yakan zuba rassan a kwamame a gaban dabbobin saboda su yi barbara kusa da rassan,
Un notikās allažiņ, kad tās agrās avis apgājās, tad Jēkabs to avju priekšā tos kociņus ielika ūdens silēs, ka tās pār tiem kokiem apietos.
42 amma in dabbobin raunana ne, ba ya sa su a can. Saboda haka raunanan dabbobi suka zama na Laban, ƙarfafan kuma suka zama na Yaƙub.
Bet kad tās vēlās avis apgājās, tad Jēkabs tos kociņus nelika iekšā, tad tie atpīļi(vājie) kļuva Lābanam un tie agrējie(spēcīgie) Jēkabam.
43 Ta haka mutumin ya zama riƙaƙƙe mai arziki, ya kasance mai manya-manyan garkuna, da bayi mata da maza, da raƙuma da kuma jakuna.
Un tas vīrs auga ļoti varens, un tam bija daudz avju, kalpoņu un kalpu, kamieļu un ēzeļu.