< Farawa 30 >
1 Sa’ad da Rahila ta ga cewa ba tă haifa wa Yaƙub’ya’ya ba, sai ta fara kishin’yar’uwarta. Saboda haka ta ce wa Yaƙub, “Ka ba ni’ya’ya, ko kuwa in mutu!”
Et Rachel vit qu’elle ne donnait pas d’enfants à Jacob, et Rachel fut jalouse de sa sœur, et dit à Jacob: Donne-moi des fils, sinon je meurs.
2 Yaƙub ya fusata da ita ya ce, “Ina a matsayin Allah ne wanda ya hana ke samun’ya’ya?”
Et la colère de Jacob s’enflamma contre Rachel, et il dit: Suis-je à la place de Dieu, qui t’a refusé le fruit du ventre?
3 Sa’an nan ta ce, “Ga Bilha, mai baiwata, ka kwana da ita don tă haifa mini’ya’ya, ta gare ta kuwa ni ma in gina iyali.”
Et elle dit: Voici ma servante Bilha: va vers elle; et elle enfantera sur mes genoux, et moi aussi j’aurai des enfants par elle.
4 Saboda haka ta ba shi baranyarta Bilha tă zama matarsa. Yaƙub kuwa ya kwana da ita,
Et elle lui donna Bilha, sa servante, pour femme; et Jacob vint vers elle.
5 ta kuwa yi ciki, ta kuma haifi ɗa.
Et Bilha conçut, et enfanta un fils à Jacob.
6 Sa’an nan Rahila ta ce, “Allah ya baratar da ni; ya saurari roƙona ya kuma ba ni ɗa.” Saboda wannan ta ba shi suna Dan.
Et Rachel dit: Dieu m’a fait justice, et il a aussi entendu ma voix, et m’a donné un fils; c’est pourquoi elle appela son nom Dan.
7 Baranyar Rahila ta sāke yin ciki ta kuma haifi wa Yaƙub ɗa na biyu.
Et Bilha, servante de Rachel, conçut encore, et enfanta un second fils à Jacob.
8 Sai Rahila ta ce, “Na yi kokawa sosai da’yar’uwata, na kuwa yi nasara.” Saboda haka ta kira shi Naftali.
Et Rachel dit: J’ai soutenu des luttes de Dieu avec ma sœur, aussi je l’ai emporté. Et elle appela son nom Nephthali.
9 Sa’ad da Liyatu ta ga cewa ta daina haihuwa, sai ta ɗauki mai hidimarta Zilfa ta ba da ita ga Yaƙub tă zama matarsa.
Et Léa vit qu’elle avait cessé d’enfanter, et elle prit Zilpa, sa servante, et la donna pour femme à Jacob.
10 Baranyar Liyatu, Zilfa ta haifa wa Yaƙub ɗa.
Et Zilpa, servante de Léa, enfanta un fils à Jacob.
11 Sai Liyatu ta ce, “Na yi sa’a!” Saboda haka ta ba shi suna Gad.
Et Léa dit: La bonne fortune vient. Et elle appela son nom Gad.
12 Zilfa baranyar Liyatu ta haifa wa Yaƙub ɗa na biyu.
Et Zilpa, servante de Léa, enfanta un second fils à Jacob.
13 Sai Liyatu ta ce, “Ni mai farin ciki ce! Mata za su ce da ni mai farin ciki.” Saboda haka ta sa masa suna Asher.
Et Léa dit: Pour mon bonheur! car les filles me diront bienheureuse. Et elle appela son nom Aser.
14 A lokacin girbin alkama, sai Ruben ya je jeji ya ɗebo manta-uwa ya kawo wa mahaifiyarsa Liyatu. Sai Rahila ta ce wa Liyatu, “Ina roƙonki ki ɗan sam mini manta-uwa ɗanki.”
Et Ruben sortit aux jours de la moisson du froment, et il trouva des mandragores dans les champs, et les apporta à Léa, sa mère. Et Rachel dit à Léa: Donne-moi, je te prie, des mandragores de ton fils.
15 Amma ta ce mata, “Bai ishe ki ba ne da kika ƙwace mijina? Yanzu kuma kina so ki ƙwace manta-uwa na yarona?” Sai Rahila ta ce “Shi ke nan, mijina zai iya kwana da ke yau saboda manta-uwa na ɗanki.”
Et elle lui dit: Est-ce peu de chose que tu m’aies pris mon mari, et tu prends aussi les mandragores de mon fils! Et Rachel dit: Eh bien, il couchera avec toi cette nuit pour les mandragores de ton fils.
16 Saboda haka sa’ad da Yaƙub ya dawo daga jeji a wannan yamma sai Liyatu ta fito ta tarye shi. Ta ce, “Dole ka kwana da ni, na yi hayarka da manta-uwa na ɗana.” Saboda haka ya kwana da ita a wannan dare.
Et Jacob vint des champs sur le soir, et Léa sortit à sa rencontre, et dit: C’est vers moi que tu viendras, car je t’ai loué pour les mandragores de mon fils. Et il coucha avec elle cette nuit-là.
17 Allah ya saurari Liyatu, ta kuwa yi ciki ta kuma haifa wa Yaƙub ɗa na biyar.
Et Dieu entendit Léa, et elle conçut, et enfanta à Jacob un cinquième fils.
18 Sai Liyatu ta ce, “Allah ya sāka mini saboda na ba da mai hidimata ga mijina.” Saboda haka ta ba shi suna Issakar.
Et Léa dit: Dieu m’a donné mon salaire, parce que j’ai donné ma servante à mon mari. Et elle appela son nom Issacar.
19 Liyatu ta sāke yin ciki ta kuma haifa wa Yaƙub ɗa na shida.
Et Léa conçut encore, et enfanta à Jacob un sixième fils.
20 Sai Liyatu ta ce, “Allah ya ba ni kyauta mai daraja. A wannan lokaci mijina zai darajarta ni, domin na haifa masa’ya’ya maza shida.” Saboda haka ta ba shi suna Zebulun.
Et Léa dit: Dieu m’a fait un beau don; cette fois mon mari habitera avec moi, car je lui ai enfanté six fils. Et elle appela son nom Zabulon.
21 Daga baya ta haifi’ya ta kuwa ba ta suna Dina.
Et après, elle enfanta une fille, et appela son nom Dina.
22 Sai Allah ya tuna da Rahila; ya saurare ta ya kuma buɗe mahaifarta.
Et Dieu se souvint de Rachel; et Dieu l’écouta et ouvrit sa matrice.
23 Sai ta yi ciki ta kuma haifi ɗa ta ce, “Allah ya ɗauke mini kunyata.”
Et elle conçut, et enfanta un fils, et dit: Dieu a ôté mon opprobre.
24 Ta ba shi suna Yusuf, ta kuma ce, “Bari Ubangiji yă ƙara mini wani ɗa.”
Et elle appela son nom Joseph, en disant: Que l’Éternel m’ajoute un autre fils!
25 Bayan Rahila ta haifi Yusuf, sai Yaƙub ya ce wa Laban, “Ka sallame ni don in koma ƙasata.
Et il arriva, quand Rachel eut enfanté Joseph, que Jacob dit à Laban: Renvoie-moi, et j’irai dans mon lieu et dans mon pays.
26 Ba ni matana da’ya’yana, waɗanda na bauta maka dominsu, zan kuwa tafi. Ka dai san yadda na bauta maka.”
Donne-moi mes femmes pour lesquelles je t’ai servi, et mes enfants, et je m’en irai; car tu sais quel a été le service que je t’ai rendu.
27 Amma Laban ya ce masa, “In na sami tagomashi daga gare ka, ina roƙonka ka zauna. Na gane ta wurin duba cewaUbangiji ya albarkace ni saboda kai.”
Et Laban lui dit: [Écoute], si au moins j’ai trouvé grâce à tes yeux! J’ai aperçu que l’Éternel m’a béni à cause de toi.
28 Ya ƙara da cewa, “Faɗa albashinka, zan kuwa biya shi.”
Et il dit: Fixe-moi ton salaire, et je te le donnerai.
29 Yaƙub ya ce masa, “Ka dai san yadda na yi maka aiki da kuma yadda dabbobinka suka yi yawa a hannuna.
Et il lui dit: Tu sais comment je t’ai servi, et ce qu’est devenu ton troupeau avec moi;
30 Kaɗan da kake da shi kafin zuwata ya ƙaru sosai, kuma Ubangiji ya albarkace ka a duk inda na tafi. Amma yanzu, yaushe zan yi wani abu domin gidana ni ma?”
car ce que tu avais avant moi était peu de chose, et s’est accru et est devenu une multitude; et l’Éternel t’a béni depuis que je suis venu. Et maintenant, quand travaillerai-je, moi aussi, pour ma maison?
31 Sai Laban ya yi tambaya, “Me zan ba ka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Kada ka ba ni wani abu. Amma in za ka yi mini abu guda ɗaya, zan ci gaba da kiwon garkunanka, ina kuma lura da su.
Et [Laban] dit: Que te donnerai-je? Et Jacob dit: Tu ne me donneras rien. Si tu veux faire ceci pour moi, je paîtrai encore ton bétail, [et] je le garderai:
32 Bari in ratsa cikin dukan garkunanka yau in fid da masu dabbare-dabbare da tumaki babare-babare, da kowane ɗan rago baƙi, da dabbare-dabbare da babare-babare na awaki daga ciki, waɗannan ne za su zama ladana.
je passerai aujourd’hui par tout ton bétail, j’en ôterai toute bête marquetée et tachetée, et tous les agneaux foncés, et ce qui est tacheté et marqueté parmi les chèvres; et ce sera là mon salaire.
33 Gaskiyata kuwa za tă zama mini shaida nan gaba, duk sa’ad da ka bincika a kan albashin da ka biya ni. Duk akuyar da take tawa da ba dabbare-dabbare ko babare-babare, ko ɗan ragon da ba baƙi ba, zai kasance sata na yi.”
Et ma justice répondra pour moi désormais, quand elle viendra devant toi pour mon salaire; tout ce qui ne sera pas marqueté et tacheté parmi les chèvres, et foncé parmi les agneaux, auprès de moi, sera tenu pour volé.
34 Sai Laban ya ce, “Na yarda. Bari yă zama yadda ka faɗa.”
Et Laban dit: Voici, qu’il en soit selon ta parole.
35 A wannan rana ya ware dukan bunsurai da suke dabbare-dabbare da masu zāne-zāne, da dukan awakin da suke dabbare-dabbare (duka da suke da fari-fari a jikinsu), da dukan baƙaƙen tumaki, ya sa su a hannun’ya’yansa maza.
Et il ôta ce jour-là les boucs rayés et tachetés, et toutes les chèvres marquetées et tachetées, toutes celles qui avaient du blanc, et tout ce qui était foncé parmi les agneaux, et il les remit entre les mains de ses fils.
36 Sa’an nan ya sa nisan tafiya kwana uku tsakaninsa da Yaƙub, yayinda Yaƙub ya ci gaba da lura da sauran garkunan Laban Yaƙub.
Et il mit trois journées de chemin entre lui et Jacob; et Jacob paissait le reste du bétail de Laban.
37 Yaƙub ya samo ɗanyen reshen itatuwan aduruku, da na katambiri, da na durumi, ya ɓare ya bar fararen cikin katakon rassan.
– Et Jacob prit des branches fraîches de peuplier blanc, de coudrier, et d’érable, et y pela des raies blanches, mettant à nu le blanc qui était aux branches.
38 Sa’an nan ya zuba ɓararre rassan cikin dukan kwamame na banruwa saboda su kasance a gaban garkunan sa’ad da suka zo shan ruwa. A sa’ad da garkunan suke barbara suka kuma zo shan ruwa,
Et il plaça les branches, qu’il avait pelées, devant le bétail dans les auges, dans les abreuvoirs où le bétail venait boire; et le bétail entrait en chaleur lorsqu’il venait boire;
39 sai su yi barbara a gaban rassan. Sai kuwa su haifi ƙanana masu zāne dabbare-dabbare, ko babare-babare ko masu zāne-zāne.
le bétail entrait en chaleur devant les branches, et il faisait des petits, rayés, marquetés, et tachetés.
40 Sai Yaƙub yă ware ƙananan garken dabam, amma sai yă sa sauran su fuskanci dabbobin da suke dabbare-dabbare da kuma baƙaƙe da suke na Laban. Ta haka ya ware garkuna dabam domin kansa bai kuwa haɗa su da dabbobin Laban ba.
Et Jacob sépara les agneaux, et tourna la face du troupeau vers ce qui était rayé et tout ce qui était foncé dans le bétail de Laban; et il mit ses troupeaux à part, et ne les mit pas auprès du bétail de Laban.
41 A duk sa’ad da ƙarfafa dabbobi mata suke barbara, Yaƙub yakan zuba rassan a kwamame a gaban dabbobin saboda su yi barbara kusa da rassan,
Et il arrivait que toutes les fois que les bêtes vigoureuses entraient en chaleur, Jacob mettait les branches dans les auges, devant les yeux du bétail, afin qu’elles entrent en chaleur en face des branches.
42 amma in dabbobin raunana ne, ba ya sa su a can. Saboda haka raunanan dabbobi suka zama na Laban, ƙarfafan kuma suka zama na Yaƙub.
Mais quand les bêtes étaient chétives, il ne les mettait pas; et les chétives étaient à Laban, et les vigoureuses à Jacob.
43 Ta haka mutumin ya zama riƙaƙƙe mai arziki, ya kasance mai manya-manyan garkuna, da bayi mata da maza, da raƙuma da kuma jakuna.
Et l’homme s’accrut extrêmement, et eut un bétail nombreux, et des servantes et des serviteurs, et des chameaux et des ânes.