< Farawa 30 >
1 Sa’ad da Rahila ta ga cewa ba tă haifa wa Yaƙub’ya’ya ba, sai ta fara kishin’yar’uwarta. Saboda haka ta ce wa Yaƙub, “Ka ba ni’ya’ya, ko kuwa in mutu!”
Da Rakel så, at hun ikke fødte Jakob noget Barn, blev hun skinsyg på sin Søster og sagde til Jakob: "Skaf mig Børn, ellers dør jeg!"
2 Yaƙub ya fusata da ita ya ce, “Ina a matsayin Allah ne wanda ya hana ke samun’ya’ya?”
Men Jakob blev vred på Rakel og sagde: "Er jeg i Guds Sted? Det er jo ham, der har nægtet dig Livsfrugt!"
3 Sa’an nan ta ce, “Ga Bilha, mai baiwata, ka kwana da ita don tă haifa mini’ya’ya, ta gare ta kuwa ni ma in gina iyali.”
Så sagde hun: "Der er min Trælkvinde Bilha; gå ind til hende, så hun kan føde på mine Knæ og jeg få Sønner ved hende!"
4 Saboda haka ta ba shi baranyarta Bilha tă zama matarsa. Yaƙub kuwa ya kwana da ita,
Og hun gav ham sin Trælkvinde Bilha til Hustru, og Jakob gik ind til hende.
5 ta kuwa yi ciki, ta kuma haifi ɗa.
Så blev Bilha frugtsommelig og fødte Jakob en Søn,
6 Sa’an nan Rahila ta ce, “Allah ya baratar da ni; ya saurari roƙona ya kuma ba ni ɗa.” Saboda wannan ta ba shi suna Dan.
og Rakel sagde: "Gud har hjulpet mig til min Ret, han har hørt min Røst og givet mig en Søn." Derfor gav hun ham Navnet Dan.
7 Baranyar Rahila ta sāke yin ciki ta kuma haifi wa Yaƙub ɗa na biyu.
Siden blev Rakels Trælkvinde Bilha frugtsommelig igen og fødte Jakob en anden Søn;
8 Sai Rahila ta ce, “Na yi kokawa sosai da’yar’uwata, na kuwa yi nasara.” Saboda haka ta kira shi Naftali.
og Rakel sagde: "Gudskampe har jeg kæmpet med min Søster og sejret." Derfor gav hun ham Navnet Naftali.
9 Sa’ad da Liyatu ta ga cewa ta daina haihuwa, sai ta ɗauki mai hidimarta Zilfa ta ba da ita ga Yaƙub tă zama matarsa.
Men da Lea så, at hun ikke fik flere Børn, tog hun sin Trælkvinde Zilpa og gav Jakob hende til Hustru;
10 Baranyar Liyatu, Zilfa ta haifa wa Yaƙub ɗa.
og da Leas Trælkvinde Zilpa fødte Jakob en Søn,
11 Sai Liyatu ta ce, “Na yi sa’a!” Saboda haka ta ba shi suna Gad.
sagde Lea: "Hvilken Lykke!" Derfor gav hun ham Navnet Gad.
12 Zilfa baranyar Liyatu ta haifa wa Yaƙub ɗa na biyu.
Siden fødte Leas Trælkvinde Zilpa Jakob en anden Søn;
13 Sai Liyatu ta ce, “Ni mai farin ciki ce! Mata za su ce da ni mai farin ciki.” Saboda haka ta sa masa suna Asher.
og Lea sagde: "Held mig! Kvinderne vil prise mit Held!" Derfor gav hun ham Navnet Aser.
14 A lokacin girbin alkama, sai Ruben ya je jeji ya ɗebo manta-uwa ya kawo wa mahaifiyarsa Liyatu. Sai Rahila ta ce wa Liyatu, “Ina roƙonki ki ɗan sam mini manta-uwa ɗanki.”
Men da Ruben engang i Hvedehøstens Tid gik på Marken, fandt han nogle Kærlighedsæbler og bragte dem til sin Moder Lea. Da sagde Rakel til Lea: "Giv mig nogle af din Søns Kærlighedsæbler!"
15 Amma ta ce mata, “Bai ishe ki ba ne da kika ƙwace mijina? Yanzu kuma kina so ki ƙwace manta-uwa na yarona?” Sai Rahila ta ce “Shi ke nan, mijina zai iya kwana da ke yau saboda manta-uwa na ɗanki.”
Lea svarede: "Er det ikke nok, at du har taget min Mand fra mig? Vil du nu også tage min Søns Kærlighedsæbler?" Men Rakel sagde: "Til Gengæld for din Søns Kærlighedsæbler må han ligge hos dig i Nat!"
16 Saboda haka sa’ad da Yaƙub ya dawo daga jeji a wannan yamma sai Liyatu ta fito ta tarye shi. Ta ce, “Dole ka kwana da ni, na yi hayarka da manta-uwa na ɗana.” Saboda haka ya kwana da ita a wannan dare.
Da så Jakob kom fra Marken om Aftenen, gik Lea ham i Møde og sagde: "Kom ind til mig i Nat, thi jeg har købt dig for min Søns Kærlighedsæbler!" Og han lå hos hende den Nat.
17 Allah ya saurari Liyatu, ta kuwa yi ciki ta kuma haifa wa Yaƙub ɗa na biyar.
Så bønhørte Gud Lea, og hun blev frugtsommelig og fødte Jakob en femte Søn;
18 Sai Liyatu ta ce, “Allah ya sāka mini saboda na ba da mai hidimata ga mijina.” Saboda haka ta ba shi suna Issakar.
og Lea sagde: "Gud har lønnet mig, fordi jeg gav min Mand min Trælkvinde." Derfor gav hun ham Navnet Issakar.
19 Liyatu ta sāke yin ciki ta kuma haifa wa Yaƙub ɗa na shida.
Siden blev Lea frugtsommelig igen og fødte Jakob en sjette Søn;
20 Sai Liyatu ta ce, “Allah ya ba ni kyauta mai daraja. A wannan lokaci mijina zai darajarta ni, domin na haifa masa’ya’ya maza shida.” Saboda haka ta ba shi suna Zebulun.
og Lea sagde: "Gud har givet mig en god Gave, nu vil min Mand blive hos mig, fordi jeg har født ham seks Sønner." Derfor gav hun ham Navnet Zebulon.
21 Daga baya ta haifi’ya ta kuwa ba ta suna Dina.
Siden fødte hun en Datter, som hun gav Navnet Dina.
22 Sai Allah ya tuna da Rahila; ya saurare ta ya kuma buɗe mahaifarta.
Så kom Gud Rakel i Hu, og Gud bønhørte hende og åbnede hendes Moderliv,
23 Sai ta yi ciki ta kuma haifi ɗa ta ce, “Allah ya ɗauke mini kunyata.”
så hun blev frugtsommelig og fødte en Søn; og hun sagde: "Gud har borttaget min Skændsel."
24 Ta ba shi suna Yusuf, ta kuma ce, “Bari Ubangiji yă ƙara mini wani ɗa.”
Derfor gav hun ham Navnet Josef; thi hun sagde: "HERREN give mig endnu en Søn!"
25 Bayan Rahila ta haifi Yusuf, sai Yaƙub ya ce wa Laban, “Ka sallame ni don in koma ƙasata.
Da Rakel havde født Josef. sagde Jakob til Laban: "Lad mig fare, at jeg kan drage til min Hjemstavn og mit Land;
26 Ba ni matana da’ya’yana, waɗanda na bauta maka dominsu, zan kuwa tafi. Ka dai san yadda na bauta maka.”
giv mig mine Hustruer og mine Børn som jeg har tjent dig for, og lad mig drage bort; du ved jo selv, hvorledes jeg har tjent dig!"
27 Amma Laban ya ce masa, “In na sami tagomashi daga gare ka, ina roƙonka ka zauna. Na gane ta wurin duba cewaUbangiji ya albarkace ni saboda kai.”
Men Laban svarede: "Måtte jeg have fundet Nåde for dine Øjne! Jeg har udfundet, at HERREN bar velsignet mig for din Skyld."
28 Ya ƙara da cewa, “Faɗa albashinka, zan kuwa biya shi.”
Og han sagde: "Bestem, hvad du vil have i Løn af mig, så vil jeg give dig den!"
29 Yaƙub ya ce masa, “Ka dai san yadda na yi maka aiki da kuma yadda dabbobinka suka yi yawa a hannuna.
Så sagde Jakob: "Du ved jo selv, hvorledes jeg har tjent dig, og hvad din Ejendom er blevet til under mine Hænder;
30 Kaɗan da kake da shi kafin zuwata ya ƙaru sosai, kuma Ubangiji ya albarkace ka a duk inda na tafi. Amma yanzu, yaushe zan yi wani abu domin gidana ni ma?”
thi før jeg kom, ejede du kun lidet, men nu har du Overflod; HERREN har velsignet dig, hvor som helst jeg satte min Fod. Men når kan jeg komme til at gøre noget for mit eget Hus?"
31 Sai Laban ya yi tambaya, “Me zan ba ka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Kada ka ba ni wani abu. Amma in za ka yi mini abu guda ɗaya, zan ci gaba da kiwon garkunanka, ina kuma lura da su.
Laban svarede: "Hvad skal jeg da give dig?" Da sagde Jakob: "Du skal ikke give mig noget; men hvis du går ind på, hvad jeg nu foreslår dig, vedbliver jeg at være Hyrde for dine Hjorde og vogte dem.
32 Bari in ratsa cikin dukan garkunanka yau in fid da masu dabbare-dabbare da tumaki babare-babare, da kowane ɗan rago baƙi, da dabbare-dabbare da babare-babare na awaki daga ciki, waɗannan ne za su zama ladana.
Jeg vil i Dag gå hele din Hjord igennem og udskille alle spættede og blakkede Dyr alle de sorte Får og de blakkede eller spættede Geder skal være min Løn;
33 Gaskiyata kuwa za tă zama mini shaida nan gaba, duk sa’ad da ka bincika a kan albashin da ka biya ni. Duk akuyar da take tawa da ba dabbare-dabbare ko babare-babare, ko ɗan ragon da ba baƙi ba, zai kasance sata na yi.”
i Morgen den Dag skal min Retfærdighed vidne for mig: Når du kommer og syner den Hjord, der skal være min Løn, da er alle de" Geder, som ikke er spættede eller blakkede, og de Får, som ikke er sorte, stjålet af mig."
34 Sai Laban ya ce, “Na yarda. Bari yă zama yadda ka faɗa.”
Laban svarede: "Vel, lad det blive, som du siger!"
35 A wannan rana ya ware dukan bunsurai da suke dabbare-dabbare da masu zāne-zāne, da dukan awakin da suke dabbare-dabbare (duka da suke da fari-fari a jikinsu), da dukan baƙaƙen tumaki, ya sa su a hannun’ya’yansa maza.
Så udskilte han samme Dag de stribede og blakkede Bukke og de spættede og blakkede Geder, alle dem der havde hvide Pletter, og alle de sorte Får og overgav dem til sine Sønner,
36 Sa’an nan ya sa nisan tafiya kwana uku tsakaninsa da Yaƙub, yayinda Yaƙub ya ci gaba da lura da sauran garkunan Laban Yaƙub.
og han lod der være tre Dagsrejser mellem dem og Jakob; og Jakob vogtede Resten af Labans Hjord.
37 Yaƙub ya samo ɗanyen reshen itatuwan aduruku, da na katambiri, da na durumi, ya ɓare ya bar fararen cikin katakon rassan.
Men Jakob tog friske Grene af Hvidpopler, Mandeltræer og Plataner og afskrællede Barken således, at der kom hvide Striber på Grenene;
38 Sa’an nan ya zuba ɓararre rassan cikin dukan kwamame na banruwa saboda su kasance a gaban garkunan sa’ad da suka zo shan ruwa. A sa’ad da garkunan suke barbara suka kuma zo shan ruwa,
og de afskrællede Grene stillede han op i Trugene foran Dyrene, i Vandrenderne, hvor Dyrene kom hen og drak; og de parrede sig, når de kom for at drikke;
39 sai su yi barbara a gaban rassan. Sai kuwa su haifi ƙanana masu zāne dabbare-dabbare, ko babare-babare ko masu zāne-zāne.
Dyrene parrede sig foran Grenene og fødte så stribet, spættet og blakket Afkom.
40 Sai Yaƙub yă ware ƙananan garken dabam, amma sai yă sa sauran su fuskanci dabbobin da suke dabbare-dabbare da kuma baƙaƙe da suke na Laban. Ta haka ya ware garkuna dabam domin kansa bai kuwa haɗa su da dabbobin Laban ba.
Og Lammene udskilte Jakob. Og han lod Dyrene vende Hovedet mod de stribede og alle de sorte dyr i Labans Hjord. På den Måde fik han sine egne Hjorde, som han ikke bragte sammen med Labans.
41 A duk sa’ad da ƙarfafa dabbobi mata suke barbara, Yaƙub yakan zuba rassan a kwamame a gaban dabbobin saboda su yi barbara kusa da rassan,
Og hver Gang de kraftige Dyr parrede sig, stillede Jakob Grenene op foran dem i Vandrenderne, for at de skulde parre sig foran Grenene;
42 amma in dabbobin raunana ne, ba ya sa su a can. Saboda haka raunanan dabbobi suka zama na Laban, ƙarfafan kuma suka zama na Yaƙub.
men når det var de svage Dyr, stillede han dem ikke op; således kom de svage til at tilhøre Laban, de kraftige Jakob.
43 Ta haka mutumin ya zama riƙaƙƙe mai arziki, ya kasance mai manya-manyan garkuna, da bayi mata da maza, da raƙuma da kuma jakuna.
På den Måde blev Manden overmåde rig og fik Småkvæg i Mængde, Trælkvinder og Trælle, Kameler og Æsler.