< Farawa 29 >
1 Sa’an nan Yaƙub ya ci gaba da tafiyarsa har ya kai ƙasar mutanen gabashi.
A LAILA, hele aku la o Iakoba i. kona hele ana, a hiki aku la i ka aina o na kanaka o ka hikina.
2 A can ya ga rijiya a jeji da garkuna uku na tumaki kwance kusa da ita, gama a wannan rijiya ce ake shayar da garkuna. Dutsen da ake rufe bakin rijiyar mai girma ne.
Nana aku la ia, aia hoi, he luawai ma ke kula, a me na ohana hipa ekolu e moe ana ilaila: no ka mea, ua hoohainuia na ohana holoholona i ka wai o ua luawai la: a aia maluna o ka waha o ka luawai he pohaku nui.
3 Sa’ad da dukan garkuna suka taru a can, sai makiyayan su gungurar da dutsen daga bakin rijiyar su shayar da tumaki. Sa’an nan su mai da dutsen a wurinsa a bakin rijiya.
Ilaila i hoakoakoaia'i na ohana holoholona a pau: olokaa ae la lakou i ka pohaku mai ka waha ae o ka luawai, a hoohainu iho la i na hipa; a kau hou iho la i ka pohaku maluna o ka waha o ka luawai, ma kona wahi.
4 Yaƙub ya tambayi makiyayan ya ce, “’Yan’uwa, ina kuka fito?” Suka amsa, “Mu daga Haran ne.”
I aku la o Iakoba ia lakou, E kuu mau hoahanau, nohea oukou? I mai la lakou, No Harana makou.
5 Sai ya ce musu, “Kun san Laban, jikan Nahor?” Suka amsa, “I, mun san shi.”
I aku la ia ia lakou, Ua ike anei oukou ia Labana, ka moopuna a Nahora? I mai la lakou, Ua ike no makou.
6 Sa’an nan Yaƙub ya tambaye su, “Yana nan lafiya?” Suka ce, “I, yana lafiya, ga ma’yarsa Rahila tafe da tumaki.”
I aku la ia ia lakou, E ola ana anei oia? I mai la lakou, E ola ana no, aia hoi, ke hele mai la o Rahela, o kana kaikamahine me ka pua hipa.
7 Ya ce, “Duba har yanzu da sauran rana da yawa, lokaci bai kai na tara garkuna ba. Ku shayar da tumaki ku mai da su wurin kiwo.”
I aku la ia, Aia hoi, he la okoa keia; aole i hiki ka manawa e houluulu ai i na bipi: e hoohainu oukou i na hipa, a hele e hanai.
8 Suka amsa suka ce, “Ba za mu iya ba, sai dukan garkunan sun taru, aka kuma gungurar da dutsen daga bakin rijiyar. Sa’an nan za mu shayar da tumakin.”
I mai la lakou, Aole makou e hiki, a pau na ohana hipa i ka houluuluia, a olokaa ae lakou i ka pohaku, mai ka waha mai o ka luawai; alaila makou e hoohainu i na hipa.
9 Tun yana cikin magana da su, sai ga Rahila ta zo da tumakin mahaifinta, gama ita makiyayyiya ce.
Ia ia i olelo ai me lakou, hiki mai la o Rahela me na hipa a kona makuakane: no ka mea, nana lakou i malama.
10 Sa’ad da Yaƙub ya ga Rahila’yar Laban, ɗan’uwan mahaifiyarsa, da tumakin Laban, sai ya tafi ya gungurar da dutsen daga bakin rijiyar, ya kuma shayar da tumakin kawunsa.
A ike aku la o Iakoba ia Rahela, ke kaikamahine a Labana, o ke kaikunane o kona makuwahine, a me ka poe hipa a Labana, o ke kaikunane o kona makuwahine, neenee aku la o Iakoba, olokaa ae la ia i ka pohaku mai ka waha ae o ka luawai, a hoohainu iho la i ka poe hipa a Labana, o ke kaikunane o kona makuwahine.
11 Sa’an nan Yaƙub ya sumbaci Rahila, ya kuma ɗaga murya ya yi kuka.
Honi aku la o Iakoba ia Rahela, hookiekie ae la ia i kona leo, a uwe iho la.
12 Ya riga ya faɗa wa Rahila cewa shi dangin mahaifinta ne kuma ɗan Rebeka. Saboda haka ta ruga da gudu ta faɗa wa mahaifinta.
Hai aku la o Iakoba ia Rahela, he hoahanau ia no kona makuakane, a he keiki na Rebeka: holo aku la kela, a hai aku la i kona makuakane.
13 Nan da nan, da Laban ya sami labari game da Yaƙub, ɗan’yar’uwarsa, ya gaggauta yă sadu da shi. Sai ya rungume shi ya sumbace shi, ya kuma kawo shi gidansa, a can kuwa Yaƙub ya faɗa masa dukan waɗannan abubuwa.
A lohe ae la o Labana i ka olelo no Iakoba no ke keikikane a kona kaikuwahine, holo mai la ia e halawai me ia, apo mai la ia ia, honi ae la, a kai aku la ia ia i kona hale. Hai aku la oia ia Labana ia mau mea a pau.
14 Sa’an nan Laban ya ce masa, “Kai nama da jinina ne.” Bayan Yaƙub ya zauna da shi na wata guda cif,
Olelo mai la o Labana ia ia, He oiaio, o oe no kuu iwi, a me kuu io. A noho pu iho la oia me ia, hookahi malama.
15 sai Laban ya ce masa, “Don kawai kai dangina ne na kusa, sai kawai ka yi mini aiki a banza? Faɗa mini abin da albashinka zai zama.”
Olelo mai la o Labana ia Iakoba, E hookauwa wale anei oe na'u, no kou pili hoahanau ana ia'u? e hai mai oe ia'u i kau uku.
16 Laban dai yana da’ya’ya mata biyu; sunan babbar Liyatu, sunan ƙaramar kuwa Rahila.
Elua mau kaikamahine a Labana, o Lea ka inoa o ka mua, a o Rahela ka inoa o ka muli iho.
17 Liyatu tana da raunannun idanu, amma Rahila dai tsarinta yana da kyau kuma kyakkyawa ce.
He makawai ko Lea; aka, ua maikai o Rahela ke nana aku, a ua maikai kona helehelena.
18 Yaƙub ya ƙaunaci Rahila, sai ya ce, “Zan yi maka aiki na shekaru bakwai domin ƙaramar’yarka Rahila.”
Aloha aku la o Iakoba ia Rahela: i aku la ia, E hooikaika aku no au i kau hana i na makahiki ehiku no Rahela, no kau kaikamahine muli iho.
19 Laban ya ce, “Ya fi kyau in ba ka ita, da in ba wani mutum dabam. Zauna tare da ni.”
I mai la o Labana, E aho no'u ke haawi aku ia ia nau, aole na ke kanaka e ae; e noho pu oe me au.
20 Saboda haka Yaƙub ya yi bauta shekaru bakwai domin a ba shi Rahila, amma shekarun suka zama kamar’yan kwanaki ne kawai gare shi saboda ƙaunar da yake mata.
Hooikaika aku la o Iakoba i na makahiki ehiku no Rahela; a he mau la uuku wale no ia i kona manao, no kona aloha ia ia.
21 Sa’an nan Yaƙub ya ce wa Laban, “Ba ni matata. Lokacina ya cika, ina kuma so in kwana da ita.”
I aku la o Iakoba ia Labana, E haawi mai oe i ka'u wahine, i komo ai au iloko io na la, no ka mea, ua hala ae nei ko'u mau la.
22 Saboda haka Laban ya tara dukan mutanen wurin, ya yi biki.
Houluulu ae la o Labana i na kanaka a pau o ia wahi, a hana iho la i ka ahaaina,
23 Amma da yamma ta yi, sai ya ɗauki’yarsa Liyatu ya ba da ita ga Yaƙub, sai Yaƙub ya kwana da ita.
A ahiahi iho la, lalau aku la ia i kana kaikamahine ia Lea, a lawe mai la ia ia io Iakoba la, a komo aku la ia io na la.
24 Laban kuma ya ba da baranyarsa Zilfa wa’yarsa tă zama mai hidimarta.
Haawi aku la o Labana ia Zilepa i kona kaikamahine i kauwawahine na kana kaikamahine na Lea.
25 Sa’ad da safiya ta yi, sai ga Liyatu! Saboda haka Yaƙub ya ce wa Laban, “Mene ne ke nan ka yi mini? Na yi maka bauta domin Rahila, ba haka na yi ba? Don me ka ruɗe ni?”
A ao ae la, aia hoi, o Lea ka ia: i aku la o Iakoba ia Labana, Heaha keia mea au i hana mai ai ia'u? aole anei o Rahela ka'u i hooikaika aku ai nau? No ke aha hoi oe i hoopunipuni mai ai ia'u?
26 Laban ya amsa, “Ba al’adarmu ba ce a nan a ba da’ya ƙarama aure kafin’yar fari.
I mai la o Labana, Aole pela e pono ke hana ma ko makou aina, ke haawi e aku i ka hanau hope mamua o ka hanau mua.
27 Ka gama makon amaryanci na’yar nan; sa’an nan za mu ba ka ƙaramar ita ma, don ƙarin waɗansu shekaru bakwai na aiki.”
E hoopau oe i ko ia nei hebedoma, alaila e haawi hoi makou ia Rahela nau, no ka hooikaika ana au e hooikaika ai me au, i na makahiki hou aku i ehiku.
28 Haka kuwa Yaƙub ya yi. Ya gama mako guda da Liyatu, sa’an nan Laban ya ba shi’yarsa Rahila tă zama matarsa.
Pela no o Iakoba i hana aku ai, a hoopau ae la i ko ia la hebedoma: a haawi aku la hoi oia ia Rahela i kana kaikamahine i wahine nana.
29 Laban ya ba da baranyarsa Bilha wa’yarsa Rahila ta zama mai hidimarta.
Haawi mai la o Labana ia Bileha i kona kaikamahine, i kauwawahine na Rahela, na kana kaikamahine.
30 Yaƙub ya kwana da Rahila ita ma, ya kuwa ƙaunaci Rahila fiye da Liyatu. Ya kuma yi wa Laban aiki na ƙarin waɗansu shekaru bakwai.
Komo aku la hoi oia io Rahela la, a oi aku la kona aloha ia Rahela mamua o kona aloha ia Lea; a hooikaika aku la ia me Labana i na makahiki hou aku i ehiku.
31 Sa’ad da Ubangiji ya ga ba a ƙaunar Liyatu, sai ya buɗe mahaifarta, amma Rahila ta zama bakararriya.
A ike iho la o Iehova, ua hoowahawahaia o Lea, hoohua iho la ia i kona opu: aka, ua pa o Rahela.
32 Sai Liyatu ta yi ciki ta haifi ɗa. Ta sa masa suna Ruben, gama ta ce, “Domin Ubangiji ya ga wahalata. Tabbatacce mijina zai ƙaunace ni yanzu.”
Hapai iho la o Lea, a hanau mai la he keikikane, a kapa iho la ia i kona inoa o I Reubena: no ka mea, i mai la ia, He oiaio, ua nana mai o Iehova i kuu popilikia; ano hoi, e aloha mai auanei ka'u kane ia'u.
33 Ta sāke yin ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Gama Ubangiji ya ji cewa ba a ƙaunata, ya ba ni wannan shi ma.” Saboda haka ta ba shi suna Simeyon.
Hapai hou iho la ia, a hanau mai la he keikikane; i mai la, No ka mea, ua lohe o Iehova i kuu hoowahawahaia, nolaila, ua haawi mai hoi oia i keia keikikane: kapa iho la ia i kona inoa, o I Simeona.
34 Har yanzu ta yi ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Yanzu, a ƙarshe mijina zai manne mini, gama na haifa masa’ya’ya maza uku.” Saboda haka ta ba shi suna Lawi.
Hapai hou iho la ia, a hanau mai la, he keikikane; i mai la, I keia manawa no, e hoopiliia mai auanei ka'u kane ia'u; no ka mea, ua hanau no wau i na keikikane ekolu nana: no ia mea i kapaia'i kona inoa, o I Levi.
35 Ta sāke yin ciki, sa’ad da ta haifi ɗa sai ta ce, “A wannan lokaci zan yabi Ubangiji.” Saboda haka ta ba shi suna Yahuda. Sa’an nan ta daina haihuwa.
Hapai hou iho la ia, a hanau mai la he keikikane: i mai la ia, Ano no, e hoolea aku wau ia Iehova; nolaila, kapa iho la ia i kona inoa, o I Iuda; a oki iho la kona hanau ana.