< Farawa 29 >

1 Sa’an nan Yaƙub ya ci gaba da tafiyarsa har ya kai ƙasar mutanen gabashi.
Ja Jaakob lähti matkaan ja tuli Idän miesten maalle.
2 A can ya ga rijiya a jeji da garkuna uku na tumaki kwance kusa da ita, gama a wannan rijiya ce ake shayar da garkuna. Dutsen da ake rufe bakin rijiyar mai girma ne.
Ja katso, hän huomasi kedolla kaivon, ja katso, sen ääressä makasi kolme lammaslaumaa, sillä siitä kaivosta oli tapana juottaa laumoja. Ja kaivon suulla oli suuri kivi.
3 Sa’ad da dukan garkuna suka taru a can, sai makiyayan su gungurar da dutsen daga bakin rijiyar su shayar da tumaki. Sa’an nan su mai da dutsen a wurinsa a bakin rijiya.
Sentähden annettiin kaikkien laumojen kokoontua sinne ja sitten vieritettiin kivi kaivon suulta ja juotettiin lampaat, jonka jälkeen kivi taas pantiin paikoilleen kaivon suulle.
4 Yaƙub ya tambayi makiyayan ya ce, “’Yan’uwa, ina kuka fito?” Suka amsa, “Mu daga Haran ne.”
Ja Jaakob sanoi heille: "Veljeni, mistä te olette?" He vastasivat: "Harranista olemme".
5 Sai ya ce musu, “Kun san Laban, jikan Nahor?” Suka amsa, “I, mun san shi.”
Hän kysyi heiltä: "Tunnetteko Laabanin, Naahorin pojan?" He vastasivat: "Tunnemme".
6 Sa’an nan Yaƙub ya tambaye su, “Yana nan lafiya?” Suka ce, “I, yana lafiya, ga ma’yarsa Rahila tafe da tumaki.”
Ja hän kysyi heiltä: "Voiko hän hyvin?" He vastasivat: "Hyvin hän voi; ja katso, Raakel, hänen tyttärensä, tulee tuolla lammasten kanssa".
7 Ya ce, “Duba har yanzu da sauran rana da yawa, lokaci bai kai na tara garkuna ba. Ku shayar da tumaki ku mai da su wurin kiwo.”
Hän sanoi: "Vielä on täysi päivä ja liian aikaista koota lauma; juottakaa lampaat ja viekää ne takaisin laitumelle".
8 Suka amsa suka ce, “Ba za mu iya ba, sai dukan garkunan sun taru, aka kuma gungurar da dutsen daga bakin rijiyar. Sa’an nan za mu shayar da tumakin.”
He vastasivat: "Emme voi, ennenkuin kaikki laumat ovat koolla ja kivi on vieritetty kaivon suulta; sitten juotamme lampaat".
9 Tun yana cikin magana da su, sai ga Rahila ta zo da tumakin mahaifinta, gama ita makiyayyiya ce.
Hänen vielä puhuessaan heidän kanssaan tuli Raakel isänsä lammasten kanssa, sillä hänen oli tapana olla paimenessa.
10 Sa’ad da Yaƙub ya ga Rahila’yar Laban, ɗan’uwan mahaifiyarsa, da tumakin Laban, sai ya tafi ya gungurar da dutsen daga bakin rijiyar, ya kuma shayar da tumakin kawunsa.
Kun Jaakob näki Raakelin, enonsa Laabanin tyttären, ja enonsa Laabanin lampaat, astui hän esiin ja vieritti kiven kaivon suulta ja juotti enonsa Laabanin lampaat.
11 Sa’an nan Yaƙub ya sumbaci Rahila, ya kuma ɗaga murya ya yi kuka.
Ja Jaakob suuteli Raakelia ja korotti äänensä ja itki.
12 Ya riga ya faɗa wa Rahila cewa shi dangin mahaifinta ne kuma ɗan Rebeka. Saboda haka ta ruga da gudu ta faɗa wa mahaifinta.
Niin Jaakob ilmoitti Raakelille, että hän oli hänen isänsä sukulainen ja Rebekan poika; ja Raakel riensi pois ja ilmoitti sen isällensä.
13 Nan da nan, da Laban ya sami labari game da Yaƙub, ɗan’yar’uwarsa, ya gaggauta yă sadu da shi. Sai ya rungume shi ya sumbace shi, ya kuma kawo shi gidansa, a can kuwa Yaƙub ya faɗa masa dukan waɗannan abubuwa.
Kun Laaban kuuli kerrottavan Jaakobista, sisarensa pojasta, riensi hän häntä vastaan, syleili ja suuteli häntä ja toi hänet kotiinsa; ja hän kertoi Laabanille kaikki, mitä oli tapahtunut.
14 Sa’an nan Laban ya ce masa, “Kai nama da jinina ne.” Bayan Yaƙub ya zauna da shi na wata guda cif,
Ja Laaban sanoi hänelle: "Niin, sinä olet minun luutani ja lihaani". Ja hän asui hänen luonaan kuukauden päivät.
15 sai Laban ya ce masa, “Don kawai kai dangina ne na kusa, sai kawai ka yi mini aiki a banza? Faɗa mini abin da albashinka zai zama.”
Ja Laaban sanoi Jaakobille: "Olet tosin sukulaiseni, mutta palvelisitko silti minua palkatta? Sano minulle, mikä on palkkasi oleva."
16 Laban dai yana da’ya’ya mata biyu; sunan babbar Liyatu, sunan ƙaramar kuwa Rahila.
Mutta Laabanilla oli kaksi tytärtä; vanhemman nimi oli Leea, nuoremman nimi oli Raakel.
17 Liyatu tana da raunannun idanu, amma Rahila dai tsarinta yana da kyau kuma kyakkyawa ce.
Ja Leealla oli sameat silmät, mutta Raakelilla oli kaunis vartalo ja kauniit kasvot.
18 Yaƙub ya ƙaunaci Rahila, sai ya ce, “Zan yi maka aiki na shekaru bakwai domin ƙaramar’yarka Rahila.”
Ja Jaakob rakasti Raakelia; niin hän sanoi: "Minä palvelen sinua seitsemän vuotta saadakseni Raakelin, nuoremman tyttäresi".
19 Laban ya ce, “Ya fi kyau in ba ka ita, da in ba wani mutum dabam. Zauna tare da ni.”
Laaban vastasi: "Parempi on, että annan hänet sinulle, kuin että antaisin hänet jollekin toiselle; jää luokseni".
20 Saboda haka Yaƙub ya yi bauta shekaru bakwai domin a ba shi Rahila, amma shekarun suka zama kamar’yan kwanaki ne kawai gare shi saboda ƙaunar da yake mata.
Jaakob palveli siis seitsemän vuotta saadakseen Raakelin, ja ne tuntuivat hänestä muutamilta päiviltä; niin hän rakasti häntä.
21 Sa’an nan Yaƙub ya ce wa Laban, “Ba ni matata. Lokacina ya cika, ina kuma so in kwana da ita.”
Senjälkeen Jaakob sanoi Laabanille: "Anna minulle vaimoni, sillä aikani on nyt kulunut umpeen, mennäkseni hänen tykönsä".
22 Saboda haka Laban ya tara dukan mutanen wurin, ya yi biki.
Silloin Laaban kutsui kokoon kaikki sen paikkakunnan asukkaat ja laittoi pidot;
23 Amma da yamma ta yi, sai ya ɗauki’yarsa Liyatu ya ba da ita ga Yaƙub, sai Yaƙub ya kwana da ita.
mutta illalla hän otti tyttärensä Leean ja vei hänet hänen luokseen; ja hän yhtyi häneen.
24 Laban kuma ya ba da baranyarsa Zilfa wa’yarsa tă zama mai hidimarta.
Ja Laaban antoi orjattarensa Silpan tyttärellensä Leealle orjattareksi.
25 Sa’ad da safiya ta yi, sai ga Liyatu! Saboda haka Yaƙub ya ce wa Laban, “Mene ne ke nan ka yi mini? Na yi maka bauta domin Rahila, ba haka na yi ba? Don me ka ruɗe ni?”
Aamulla hän näki, että se oli Leea. Ja hän sanoi Laabanille: "Mitä oletkaan minulle tehnyt? Olenhan palvellut sinua saadakseni Raakelin! Miksi petit minut?"
26 Laban ya amsa, “Ba al’adarmu ba ce a nan a ba da’ya ƙarama aure kafin’yar fari.
Laaban vastasi: "Ei ole meidän maassamme tapana antaa nuorempaa ennen vanhempaa.
27 Ka gama makon amaryanci na’yar nan; sa’an nan za mu ba ka ƙaramar ita ma, don ƙarin waɗansu shekaru bakwai na aiki.”
Vietä nyt vain tämä hääviikko loppuun, niin annetaan sinulle toinenkin, kunhan olet palveluksessani vielä toiset seitsemän vuotta."
28 Haka kuwa Yaƙub ya yi. Ya gama mako guda da Liyatu, sa’an nan Laban ya ba shi’yarsa Rahila tă zama matarsa.
Ja Jaakob suostui siihen, ja kun hän oli viettänyt sen viikon loppuun, antoi Laaban myöskin tyttärensä Raakelin hänelle vaimoksi.
29 Laban ya ba da baranyarsa Bilha wa’yarsa Rahila ta zama mai hidimarta.
Ja Laaban antoi orjattarensa Bilhan tyttärellensä Raakelille orjattareksi.
30 Yaƙub ya kwana da Rahila ita ma, ya kuwa ƙaunaci Rahila fiye da Liyatu. Ya kuma yi wa Laban aiki na ƙarin waɗansu shekaru bakwai.
Ja hän yhtyi myös Raakeliin, ja Raakel oli hänelle rakkaampi kuin Leea; ja hän palveli Laabanin luona vielä toiset seitsemän vuotta.
31 Sa’ad da Ubangiji ya ga ba a ƙaunar Liyatu, sai ya buɗe mahaifarta, amma Rahila ta zama bakararriya.
Ja kun Herra näki, että Leeaa hyljittiin, avasi hän hänen kohtunsa; mutta Raakel oli hedelmätön.
32 Sai Liyatu ta yi ciki ta haifi ɗa. Ta sa masa suna Ruben, gama ta ce, “Domin Ubangiji ya ga wahalata. Tabbatacce mijina zai ƙaunace ni yanzu.”
Niin Leea tuli raskaaksi ja synnytti pojan ja antoi hänelle nimen Ruuben, sanoen: "Herra on nähnyt minun kurjuuteni; nyt on mieheni rakastava minua".
33 Ta sāke yin ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Gama Ubangiji ya ji cewa ba a ƙaunata, ya ba ni wannan shi ma.” Saboda haka ta ba shi suna Simeyon.
Ja hän tuli jälleen raskaaksi ja synnytti pojan ja sanoi: "Herra on kuullut, että minua hyljitään, ja on antanut minulle myös tämän". Niin hän antoi hänelle nimen Simeon.
34 Har yanzu ta yi ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Yanzu, a ƙarshe mijina zai manne mini, gama na haifa masa’ya’ya maza uku.” Saboda haka ta ba shi suna Lawi.
Ja hän tuli jälleen raskaaksi ja synnytti pojan ja sanoi: "Nyt kai mieheni vihdoinkin kiintyy minuun, sillä olenhan synnyttänyt hänelle kolme poikaa". Sentähden hän antoi hänelle nimen Leevi.
35 Ta sāke yin ciki, sa’ad da ta haifi ɗa sai ta ce, “A wannan lokaci zan yabi Ubangiji.” Saboda haka ta ba shi suna Yahuda. Sa’an nan ta daina haihuwa.
Ja hän tuli vieläkin raskaaksi ja synnytti pojan ja sanoi: "Nyt minä kiitän Herraa". Sentähden hän antoi hänelle nimen Juuda. Sitten hän lakkasi synnyttämästä.

< Farawa 29 >