< Farawa 29 >

1 Sa’an nan Yaƙub ya ci gaba da tafiyarsa har ya kai ƙasar mutanen gabashi.
Jacob continued on the road [MTY], and he arrived at the land that was east of Canaan.
2 A can ya ga rijiya a jeji da garkuna uku na tumaki kwance kusa da ita, gama a wannan rijiya ce ake shayar da garkuna. Dutsen da ake rufe bakin rijiyar mai girma ne.
There he [was surprised to] see a well in a field, and three flocks of sheep were lying near the well. It was the well from which shepherds habitually got water for their sheep. There was a large stone covering the top of the well.
3 Sa’ad da dukan garkuna suka taru a can, sai makiyayan su gungurar da dutsen daga bakin rijiyar su shayar da tumaki. Sa’an nan su mai da dutsen a wurinsa a bakin rijiya.
When all the flocks were gathered there, the shepherds would work together to roll the stone away from the top of the well and get water for the sheep. When they finished doing that, they would put the stone back in its place over the top of the well.
4 Yaƙub ya tambayi makiyayan ya ce, “’Yan’uwa, ina kuka fito?” Suka amsa, “Mu daga Haran ne.”
[On that day], Jacob asked the shepherds who were sitting there, “Where are you from?” They replied, “We are from Haran.”
5 Sai ya ce musu, “Kun san Laban, jikan Nahor?” Suka amsa, “I, mun san shi.”
He asked them, “Do you know Laban, the grandson of Nahor?” They replied, “Yes, we know him.”
6 Sa’an nan Yaƙub ya tambaye su, “Yana nan lafiya?” Suka ce, “I, yana lafiya, ga ma’yarsa Rahila tafe da tumaki.”
Jacob asked them, “Is Laban well?” They replied, “Yes, he is well. Look! Here comes his daughter Rachel with the sheep!”
7 Ya ce, “Duba har yanzu da sauran rana da yawa, lokaci bai kai na tara garkuna ba. Ku shayar da tumaki ku mai da su wurin kiwo.”
Jacob said, “Hey! The sun is still high in the sky. It is not time for the flocks to be gathered for nighttime. Give the sheep some water and then take them back to (graze/eat grass) in the pastures!”
8 Suka amsa suka ce, “Ba za mu iya ba, sai dukan garkunan sun taru, aka kuma gungurar da dutsen daga bakin rijiyar. Sa’an nan za mu shayar da tumakin.”
They replied, “No, we cannot do that until all the flocks are gathered here and the stone is removed from the top of the well. After that, we will give water to the sheep.”
9 Tun yana cikin magana da su, sai ga Rahila ta zo da tumakin mahaifinta, gama ita makiyayyiya ce.
While he was still talking with them, Rachel came with her father’s sheep. She was the one who took care of her father’s sheep.
10 Sa’ad da Yaƙub ya ga Rahila’yar Laban, ɗan’uwan mahaifiyarsa, da tumakin Laban, sai ya tafi ya gungurar da dutsen daga bakin rijiyar, ya kuma shayar da tumakin kawunsa.
When Jacob saw Rachel, the daughter of Laban, who was his mother’s brother, [Jacob was so excited that] he went over and [by himself] rolled away the stone that covered the top of the well, and he got water for his uncle’s sheep.
11 Sa’an nan Yaƙub ya sumbaci Rahila, ya kuma ɗaga murya ya yi kuka.
Then Jacob kissed Rachel [on the cheek], and he cried loudly [because he was so happy].
12 Ya riga ya faɗa wa Rahila cewa shi dangin mahaifinta ne kuma ɗan Rebeka. Saboda haka ta ruga da gudu ta faɗa wa mahaifinta.
Jacob told Rachel that he was one of her father’s relatives, the son of her aunt Rebekah. So she ran and told that to her father.
13 Nan da nan, da Laban ya sami labari game da Yaƙub, ɗan’yar’uwarsa, ya gaggauta yă sadu da shi. Sai ya rungume shi ya sumbace shi, ya kuma kawo shi gidansa, a can kuwa Yaƙub ya faɗa masa dukan waɗannan abubuwa.
As soon as Laban heard that Jacob, his sister’s son, was there, he ran to meet him. He embraced him and kissed him [on the cheek]. Then he brought him to his home, and Jacob told him all that had happened to him.
14 Sa’an nan Laban ya ce masa, “Kai nama da jinina ne.” Bayan Yaƙub ya zauna da shi na wata guda cif,
Then Laban said to him, “Truly, you are part of my family!” After Jacob had stayed there and worked for Laban for a month,
15 sai Laban ya ce masa, “Don kawai kai dangina ne na kusa, sai kawai ka yi mini aiki a banza? Faɗa mini abin da albashinka zai zama.”
Laban said to him “(You should not work for me for nothing just because you are a relative of mine!/Why should you work for me for nothing just because you are a relative of mine?) [RHQ] Tell me how much you want me to pay you.”
16 Laban dai yana da’ya’ya mata biyu; sunan babbar Liyatu, sunan ƙaramar kuwa Rahila.
Well, Laban had two daughters. The older one was named Leah, and the younger one was named Rachel.
17 Liyatu tana da raunannun idanu, amma Rahila dai tsarinta yana da kyau kuma kyakkyawa ce.
Leah had pretty eyes, but Rachel had a very attractive figure and was beautiful.
18 Yaƙub ya ƙaunaci Rahila, sai ya ce, “Zan yi maka aiki na shekaru bakwai domin ƙaramar’yarka Rahila.”
Jacob (was in love with/wanted very much to be married to) Rachel, and he said, “I will work for you for seven years. That will be my payment for your letting me marry your younger daughter, Rachel.”
19 Laban ya ce, “Ya fi kyau in ba ka ita, da in ba wani mutum dabam. Zauna tare da ni.”
Laban replied, “It is better for me to let you marry her than for her to marry some other man!”
20 Saboda haka Yaƙub ya yi bauta shekaru bakwai domin a ba shi Rahila, amma shekarun suka zama kamar’yan kwanaki ne kawai gare shi saboda ƙaunar da yake mata.
So Jacob worked for Laban for seven years to get Rachel, but to him it seemed like it was only a few days, because he loved her so much.
21 Sa’an nan Yaƙub ya ce wa Laban, “Ba ni matata. Lokacina ya cika, ina kuma so in kwana da ita.”
After the seven years were ended, Jacob said to Laban, “Let me marry Rachel now, because the time we agreed upon for me to work for you is ended, and I want to marry her. [EUP]”
22 Saboda haka Laban ya tara dukan mutanen wurin, ya yi biki.
So Laban gathered together all the people who lived in that area and made a feast.
23 Amma da yamma ta yi, sai ya ɗauki’yarsa Liyatu ya ba da ita ga Yaƙub, sai Yaƙub ya kwana da ita.
But that evening, instead of taking Rachel to Jacob, Laban took his older daughter, Leah, to him. But because it was already dark, he could not see that it was Leah and not Rachel, and he had sex [EUP] with her.
24 Laban kuma ya ba da baranyarsa Zilfa wa’yarsa tă zama mai hidimarta.
(Laban had already given his slave girl Zilpah to his daughter Leah to be her maid/servant.)
25 Sa’ad da safiya ta yi, sai ga Liyatu! Saboda haka Yaƙub ya ce wa Laban, “Mene ne ke nan ka yi mini? Na yi maka bauta domin Rahila, ba haka na yi ba? Don me ka ruɗe ni?”
The next morning, Jacob was shocked to see that it was Leah who was with him! So he went to Laban [and told him] very angrily, “(What you have done to me is disgusting!/What is this that you have done to me?) [RHQ] I worked for you to get Rachel, did I not? So why did you deceive me?”
26 Laban ya amsa, “Ba al’adarmu ba ce a nan a ba da’ya ƙarama aure kafin’yar fari.
Laban replied, “In this land, it is not our custom to give a younger daughter to be married before we let someone marry our firstborn daughter.
27 Ka gama makon amaryanci na’yar nan; sa’an nan za mu ba ka ƙaramar ita ma, don ƙarin waɗansu shekaru bakwai na aiki.”
After we finish this week of celebration, we will let you marry the younger one also. But in return, you must pay for Rachel by working for me for another seven years.”
28 Haka kuwa Yaƙub ya yi. Ya gama mako guda da Liyatu, sa’an nan Laban ya ba shi’yarsa Rahila tă zama matarsa.
So that is what Jacob did. After the week of celebration was ended, Laban gave him his daughter, Rachel, to be his wife.
29 Laban ya ba da baranyarsa Bilha wa’yarsa Rahila ta zama mai hidimarta.
Laban gave his slave girl, Bilhah, to Rachel to be her maid/servant.
30 Yaƙub ya kwana da Rahila ita ma, ya kuwa ƙaunaci Rahila fiye da Liyatu. Ya kuma yi wa Laban aiki na ƙarin waɗansu shekaru bakwai.
Jacob had sex [EUP] with Rachel also, and he loved Rachel more than he loved Leah. And Jacob worked for Laban for another seven years.
31 Sa’ad da Ubangiji ya ga ba a ƙaunar Liyatu, sai ya buɗe mahaifarta, amma Rahila ta zama bakararriya.
When Yahweh saw that Jacob did not love Leah [very much], he enabled her to become pregnant. But Rachel was not able to become pregnant.
32 Sai Liyatu ta yi ciki ta haifi ɗa. Ta sa masa suna Ruben, gama ta ce, “Domin Ubangiji ya ga wahalata. Tabbatacce mijina zai ƙaunace ni yanzu.”
Leah gave birth to a son, whom she named Reuben, [which sounds like the Hebrew words that mean ‘Look, a son]!’ She said, “Yahweh has seen that I was miserable, and because of that he has given me a son. Now, surely my husband will love me for giving birth to a son for him.”
33 Ta sāke yin ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Gama Ubangiji ya ji cewa ba a ƙaunata, ya ba ni wannan shi ma.” Saboda haka ta ba shi suna Simeyon.
Later she became pregnant again and gave birth to another son. She said, “Because Yahweh has heard that my husband doesn’t love me, he has given me this son, too.” So she named him Simeon, [which means ‘someone who hears’].
34 Har yanzu ta yi ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Yanzu, a ƙarshe mijina zai manne mini, gama na haifa masa’ya’ya maza uku.” Saboda haka ta ba shi suna Lawi.
Later she became pregnant again, and gave birth to another son. She said, “Now, finally, my husband will hold me close to him.” So she named him Levi, [which means ‘hold close’].
35 Ta sāke yin ciki, sa’ad da ta haifi ɗa sai ta ce, “A wannan lokaci zan yabi Ubangiji.” Saboda haka ta ba shi suna Yahuda. Sa’an nan ta daina haihuwa.
Later she became pregnant again and gave birth to another son. She said, “(This time/Now) I will praise Yahweh.” So she called his name Judah, [which sounds like the Hebrew word that means ‘praise’]. After that, she did not give birth to any more children [for several years].

< Farawa 29 >