< Farawa 29 >

1 Sa’an nan Yaƙub ya ci gaba da tafiyarsa har ya kai ƙasar mutanen gabashi.
And so Jacob, setting out, arrived in the eastern land.
2 A can ya ga rijiya a jeji da garkuna uku na tumaki kwance kusa da ita, gama a wannan rijiya ce ake shayar da garkuna. Dutsen da ake rufe bakin rijiyar mai girma ne.
And he saw a well in a field, and also three flocks of sheep reclining near it. For the animals were watered from it, and its mouth was closed with a great stone.
3 Sa’ad da dukan garkuna suka taru a can, sai makiyayan su gungurar da dutsen daga bakin rijiyar su shayar da tumaki. Sa’an nan su mai da dutsen a wurinsa a bakin rijiya.
And the custom was, when all the sheep were gathered together, to roll away the stone. And when the flocks had been refreshed, they placed it over the mouth of the well again.
4 Yaƙub ya tambayi makiyayan ya ce, “’Yan’uwa, ina kuka fito?” Suka amsa, “Mu daga Haran ne.”
And he said to the shepherds, “Brothers, where are you from?” And they answered. “From Haran.”
5 Sai ya ce musu, “Kun san Laban, jikan Nahor?” Suka amsa, “I, mun san shi.”
And questioning them, he said, “Do you know Laban, the son of Nahor?” They said, “We know him.”
6 Sa’an nan Yaƙub ya tambaye su, “Yana nan lafiya?” Suka ce, “I, yana lafiya, ga ma’yarsa Rahila tafe da tumaki.”
He said, “Is he well?” “He is very well,” they said. “And behold, his daughter Rachel approaches with his flock.”
7 Ya ce, “Duba har yanzu da sauran rana da yawa, lokaci bai kai na tara garkuna ba. Ku shayar da tumaki ku mai da su wurin kiwo.”
And Jacob said, “There is still much daylight remaining, and it is not time to return the flocks to the sheepfold. Give the sheep to drink first, and then lead them back to pasture.”
8 Suka amsa suka ce, “Ba za mu iya ba, sai dukan garkunan sun taru, aka kuma gungurar da dutsen daga bakin rijiyar. Sa’an nan za mu shayar da tumakin.”
They responded, “We cannot, until all the animals are gathered together and we remove the stone from the mouth of the well, so that we may water the flocks.”
9 Tun yana cikin magana da su, sai ga Rahila ta zo da tumakin mahaifinta, gama ita makiyayyiya ce.
They were still speaking, and behold, Rachel arrived with her father’s sheep; for she pastured the flock.
10 Sa’ad da Yaƙub ya ga Rahila’yar Laban, ɗan’uwan mahaifiyarsa, da tumakin Laban, sai ya tafi ya gungurar da dutsen daga bakin rijiyar, ya kuma shayar da tumakin kawunsa.
When Jacob had seen her, and he realized that she was his maternal first cousin, and that these were the sheep of his uncle Laban, he removed the stone which closed the well.
11 Sa’an nan Yaƙub ya sumbaci Rahila, ya kuma ɗaga murya ya yi kuka.
And having watered the flock, he kissed her. And lifting up his voice, he wept.
12 Ya riga ya faɗa wa Rahila cewa shi dangin mahaifinta ne kuma ɗan Rebeka. Saboda haka ta ruga da gudu ta faɗa wa mahaifinta.
And he revealed to her that he was a brother of her father, and the son of Rebekah. And so, hurrying, she announced it to her father.
13 Nan da nan, da Laban ya sami labari game da Yaƙub, ɗan’yar’uwarsa, ya gaggauta yă sadu da shi. Sai ya rungume shi ya sumbace shi, ya kuma kawo shi gidansa, a can kuwa Yaƙub ya faɗa masa dukan waɗannan abubuwa.
And when he had heard that Jacob, his sister’s son, had arrived, he ran to meet him. And embracing him, and kissing him heartily, he brought him into his house. But when he had heard the reasons for his journey,
14 Sa’an nan Laban ya ce masa, “Kai nama da jinina ne.” Bayan Yaƙub ya zauna da shi na wata guda cif,
he responded, “You are my bone and my flesh.” And after the days of one month were completed,
15 sai Laban ya ce masa, “Don kawai kai dangina ne na kusa, sai kawai ka yi mini aiki a banza? Faɗa mini abin da albashinka zai zama.”
he said to him: “Though you are my brother, will you serve me for nothing? Tell me what wages you would accept.”
16 Laban dai yana da’ya’ya mata biyu; sunan babbar Liyatu, sunan ƙaramar kuwa Rahila.
In truth, he had two daughters: the name of the elder was Leah; and truly the younger was called Rachel.
17 Liyatu tana da raunannun idanu, amma Rahila dai tsarinta yana da kyau kuma kyakkyawa ce.
But while Leah was bleary-eyed, Rachel had an elegant appearance and was attractive to behold.
18 Yaƙub ya ƙaunaci Rahila, sai ya ce, “Zan yi maka aiki na shekaru bakwai domin ƙaramar’yarka Rahila.”
And Jacob, loving her, said, “I will serve you for seven years, for your younger daughter Rachel.”
19 Laban ya ce, “Ya fi kyau in ba ka ita, da in ba wani mutum dabam. Zauna tare da ni.”
Laban responded, “It is better that I give her to you than to another man; remain with me.”
20 Saboda haka Yaƙub ya yi bauta shekaru bakwai domin a ba shi Rahila, amma shekarun suka zama kamar’yan kwanaki ne kawai gare shi saboda ƙaunar da yake mata.
Therefore, Jacob served for seven years for Rachel. And these seemed like only a few days, because of the greatness of love.
21 Sa’an nan Yaƙub ya ce wa Laban, “Ba ni matata. Lokacina ya cika, ina kuma so in kwana da ita.”
And he said to Laban, “Give my wife to me. For now the time has been fulfilled, so that I may go in to her.”
22 Saboda haka Laban ya tara dukan mutanen wurin, ya yi biki.
And he, having called a great crowd of his friends to the feast, agreed to the marriage.
23 Amma da yamma ta yi, sai ya ɗauki’yarsa Liyatu ya ba da ita ga Yaƙub, sai Yaƙub ya kwana da ita.
And at night, he brought in his daughter Leah to him,
24 Laban kuma ya ba da baranyarsa Zilfa wa’yarsa tă zama mai hidimarta.
giving his daughter a handmaid named Zilpah. After Jacob had gone in to her, according to custom, when morning had arrived, he saw Leah.
25 Sa’ad da safiya ta yi, sai ga Liyatu! Saboda haka Yaƙub ya ce wa Laban, “Mene ne ke nan ka yi mini? Na yi maka bauta domin Rahila, ba haka na yi ba? Don me ka ruɗe ni?”
And he said to his father-in-law, “What is it that you intended to do? Did I not serve you for Rachel? Why have you deceived me?”
26 Laban ya amsa, “Ba al’adarmu ba ce a nan a ba da’ya ƙarama aure kafin’yar fari.
Laban responded, “It is not the practice in this place to give the younger in marriage first.
27 Ka gama makon amaryanci na’yar nan; sa’an nan za mu ba ka ƙaramar ita ma, don ƙarin waɗansu shekaru bakwai na aiki.”
Complete a week of days with this mating. And then I will give this one to you also, for the service that you will provide to me for another seven years.”
28 Haka kuwa Yaƙub ya yi. Ya gama mako guda da Liyatu, sa’an nan Laban ya ba shi’yarsa Rahila tă zama matarsa.
He agreed to his pleading. And after the week had passed, he took Rachel as a wife.
29 Laban ya ba da baranyarsa Bilha wa’yarsa Rahila ta zama mai hidimarta.
To her, the father had given Bilhah as her servant.
30 Yaƙub ya kwana da Rahila ita ma, ya kuwa ƙaunaci Rahila fiye da Liyatu. Ya kuma yi wa Laban aiki na ƙarin waɗansu shekaru bakwai.
And, having at last obtained the marriage he desired, he preferred the love of the latter before the former, and he served with him another seven years.
31 Sa’ad da Ubangiji ya ga ba a ƙaunar Liyatu, sai ya buɗe mahaifarta, amma Rahila ta zama bakararriya.
But the Lord, seeing that he despised Leah, opened her womb, but her sister remained barren.
32 Sai Liyatu ta yi ciki ta haifi ɗa. Ta sa masa suna Ruben, gama ta ce, “Domin Ubangiji ya ga wahalata. Tabbatacce mijina zai ƙaunace ni yanzu.”
Having conceived, she gave birth to a son, and she called his name Reuben, saying: “The Lord saw my humiliation; now my husband will love me.”
33 Ta sāke yin ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Gama Ubangiji ya ji cewa ba a ƙaunata, ya ba ni wannan shi ma.” Saboda haka ta ba shi suna Simeyon.
And again she conceived and bore a son, and she said, “Because the Lord heard that I was treated with contempt, he has also given this one to me.” And she called his name Simeon.
34 Har yanzu ta yi ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Yanzu, a ƙarshe mijina zai manne mini, gama na haifa masa’ya’ya maza uku.” Saboda haka ta ba shi suna Lawi.
And she conceived a third time, and she gave birth to another son, and she said: “Now likewise my husband will unite with me, because I have borne him three sons.” And because of this, she called his name Levi.
35 Ta sāke yin ciki, sa’ad da ta haifi ɗa sai ta ce, “A wannan lokaci zan yabi Ubangiji.” Saboda haka ta ba shi suna Yahuda. Sa’an nan ta daina haihuwa.
A fourth time she conceived and bore a son, and she said, “Only now will I confess to the Lord.” And for this reason, she called him Judah. And she ceased from child-bearing.

< Farawa 29 >