< Farawa 29 >

1 Sa’an nan Yaƙub ya ci gaba da tafiyarsa har ya kai ƙasar mutanen gabashi.
Eka Jakobo nodhi nyime gi wuoth kendo nochopo e piny ogendini man yo wuok chiengʼ.
2 A can ya ga rijiya a jeji da garkuna uku na tumaki kwance kusa da ita, gama a wannan rijiya ce ake shayar da garkuna. Dutsen da ake rufe bakin rijiyar mai girma ne.
Nopo koneno soko ei pap kod kweth adek mag rombe konindo machiegni kanyo nikech kwethgo ne modho e sokono. To kidi mane nitie e dho sokono ne duongʼ.
3 Sa’ad da dukan garkuna suka taru a can, sai makiyayan su gungurar da dutsen daga bakin rijiyar su shayar da tumaki. Sa’an nan su mai da dutsen a wurinsa a bakin rijiya.
Jokwath nengʼielo kidi kane jamni osechokore kanyo mondo gimodhi. Bangʼ ka jamni duto osemodho, to ne gingʼielo kidino mondo odog oum dho soko.
4 Yaƙub ya tambayi makiyayan ya ce, “’Yan’uwa, ina kuka fito?” Suka amsa, “Mu daga Haran ne.”
Jakobo nopenjo jokwath niya, “Owetena ua kanye?” Negidwoke niya, “Waa Haran.”
5 Sai ya ce musu, “Kun san Laban, jikan Nahor?” Suka amsa, “I, mun san shi.”
Nowachonegi niya, “Bende ungʼeyo Laban nyakwar Nahor?” Negidwoke niya, “Ee, wangʼeye.”
6 Sa’an nan Yaƙub ya tambaye su, “Yana nan lafiya?” Suka ce, “I, yana lafiya, ga ma’yarsa Rahila tafe da tumaki.”
Eka Jakobo nopenjogi niya, “Ongima?” Negidwoke niya, “Ee, ongima, kendo mabiro gi rombe cha en Rael ma nyare.”
7 Ya ce, “Duba har yanzu da sauran rana da yawa, lokaci bai kai na tara garkuna ba. Ku shayar da tumaki ku mai da su wurin kiwo.”
Nowachonegi niya, “Neuru, piny pod chon, sa michokoe jamni podi. Weuru rombe omodhi bangʼe uduokgi e lek.”
8 Suka amsa suka ce, “Ba za mu iya ba, sai dukan garkunan sun taru, aka kuma gungurar da dutsen daga bakin rijiyar. Sa’an nan za mu shayar da tumakin.”
Negidwoke niya, “Ok wanyal timo kamano kapok jokwath duto ochokore ma wangʼielo kidi manie dho soko oko mondo jamni omodhi.”
9 Tun yana cikin magana da su, sai ga Rahila ta zo da tumakin mahaifinta, gama ita makiyayyiya ce.
Kane pod oyudo owuoyo kodgi, Rael nochopo gi romb wuon-gi nikech en ema nokwayogi.
10 Sa’ad da Yaƙub ya ga Rahila’yar Laban, ɗan’uwan mahaifiyarsa, da tumakin Laban, sai ya tafi ya gungurar da dutsen daga bakin rijiyar, ya kuma shayar da tumakin kawunsa.
Kane Jakobo oneno Rael, nyar Laban ner mare kod romb Laban, nodhi mongʼielo kidi oko e dho soko kendo omiyo romb ner mare omodho.
11 Sa’an nan Yaƙub ya sumbaci Rahila, ya kuma ɗaga murya ya yi kuka.
Eka Jakobo nonyodho Rael kendo noywak gi dwol maduongʼ.
12 Ya riga ya faɗa wa Rahila cewa shi dangin mahaifinta ne kuma ɗan Rebeka. Saboda haka ta ruga da gudu ta faɗa wa mahaifinta.
Noyudo osenyiso Rael ni en wat wuon Rael kendo ni en wuod Rebeka. Kuom mano Rael nodhi monyiso wuon mare.
13 Nan da nan, da Laban ya sami labari game da Yaƙub, ɗan’yar’uwarsa, ya gaggauta yă sadu da shi. Sai ya rungume shi ya sumbace shi, ya kuma kawo shi gidansa, a can kuwa Yaƙub ya faɗa masa dukan waɗannan abubuwa.
To kane Laban owinjo wach mar Jakobo, wuod nyamin noringo mondo odhi oromne. Nokwake kendo omose gimor mi orwake dalane kendo Jakobo nonyise gik moko duto.
14 Sa’an nan Laban ya ce masa, “Kai nama da jinina ne.” Bayan Yaƙub ya zauna da shi na wata guda cif,
Eka Laban nowachone niya, “In ringra awuon kendo remba.” Kane Jakobo ne osedak kod Laban kuom dwe achiel,
15 sai Laban ya ce masa, “Don kawai kai dangina ne na kusa, sai kawai ka yi mini aiki a banza? Faɗa mini abin da albashinka zai zama.”
Laban nowachone niya, “Mana nikech in watna, bende en gima ber tiyona maonge chudo? Nyisa gima dachul.”
16 Laban dai yana da’ya’ya mata biyu; sunan babbar Liyatu, sunan ƙaramar kuwa Rahila.
To Laban ne nigi nyiri ariyo: nyako maduongʼ ne nyinge Lea kendo nyako matin ne nyinge Rael.
17 Liyatu tana da raunannun idanu, amma Rahila dai tsarinta yana da kyau kuma kyakkyawa ce.
Lea ne nigi wangʼ ma ok nenre maber, to Rael ne nigi chia kendo jaber.
18 Yaƙub ya ƙaunaci Rahila, sai ya ce, “Zan yi maka aiki na shekaru bakwai domin ƙaramar’yarka Rahila.”
Jakobo nohero Rael, kendo nowacho ni Laban niya, “Abiro tiyoni kuom higni abiriyo kuom Rael nyari matin.”
19 Laban ya ce, “Ya fi kyau in ba ka ita, da in ba wani mutum dabam. Zauna tare da ni.”
Laban nowacho niya, “Ber mondo amiyi godo moloyo chiwe ni jomoko. Koro dag mana koda ka.”
20 Saboda haka Yaƙub ya yi bauta shekaru bakwai domin a ba shi Rahila, amma shekarun suka zama kamar’yan kwanaki ne kawai gare shi saboda ƙaunar da yake mata.
Omiyo Jakobo notiyone Laban higni abiriyo mondo oyud Rael, to hignigo nonenorene mana ka ndalo matin nikech hera manoherogo Rael.
21 Sa’an nan Yaƙub ya ce wa Laban, “Ba ni matata. Lokacina ya cika, ina kuma so in kwana da ita.”
Eka Jakobo nowacho ne Laban, “Asetieko ndalo mane iketona, omiyo koro miya nyari mondo obed chiega.”
22 Saboda haka Laban ya tara dukan mutanen wurin, ya yi biki.
Kuom mano Laban noloso nyasi kendo nogwelo ji duto mae pinyno.
23 Amma da yamma ta yi, sai ya ɗauki’yarsa Liyatu ya ba da ita ga Yaƙub, sai Yaƙub ya kwana da ita.
To kane ochopo odhiambo, Laban nokawo nyare ma Lea mi omiyo Jakobo mondo obed chiege.
24 Laban kuma ya ba da baranyarsa Zilfa wa’yarsa tă zama mai hidimarta.
Kendo Laban nochiwo Zilpa jatichne ma nyako ne nyare, Lea, mondo obed jatichne.
25 Sa’ad da safiya ta yi, sai ga Liyatu! Saboda haka Yaƙub ya ce wa Laban, “Mene ne ke nan ka yi mini? Na yi maka bauta domin Rahila, ba haka na yi ba? Don me ka ruɗe ni?”
Kane piny oru, Jakobo nofwenyo mana ni en Lea! Omiyo nopenjo Laban niya, “Angʼo momiyo isetimona kama? Donge natiyoni mondo imiya Rael? To angʼo momiyo isewuonda?”
26 Laban ya amsa, “Ba al’adarmu ba ce a nan a ba da’ya ƙarama aure kafin’yar fari.
Laban nodwoke niya, “Ok en timwa mondo nyako matin okuong odhi tedo ne nyako maduongʼ.
27 Ka gama makon amaryanci na’yar nan; sa’an nan za mu ba ka ƙaramar ita ma, don ƙarin waɗansu shekaru bakwai na aiki.”
Rit nyaka watiek juma achiel mar nyasi mar nyakoni; eka abiro miyi Rael kiyie tiyona kuom higni abiriyo mamoko.”
28 Haka kuwa Yaƙub ya yi. Ya gama mako guda da Liyatu, sa’an nan Laban ya ba shi’yarsa Rahila tă zama matarsa.
Kendo Jakobo notimo kamano. Notieko jumb kend mar Lea. Eka Laban nomiye Rael nyare mondo obed chiege.
29 Laban ya ba da baranyarsa Bilha wa’yarsa Rahila ta zama mai hidimarta.
Laban nochiwo Bilha jatichne ma nyako ne Rael nyare kaka jatichne.
30 Yaƙub ya kwana da Rahila ita ma, ya kuwa ƙaunaci Rahila fiye da Liyatu. Ya kuma yi wa Laban aiki na ƙarin waɗansu shekaru bakwai.
Jakobo nobedoe achiel gi Rael bende kendo nohero Rael moloyo Lea. Kendo notiyone Laban higni abiriyo moko kendo.
31 Sa’ad da Ubangiji ya ga ba a ƙaunar Liyatu, sai ya buɗe mahaifarta, amma Rahila ta zama bakararriya.
Kane Jehova Nyasaye oneno ni Lea ne ok oher, ne oyawo iye to Rael noketo obedo migumba.
32 Sai Liyatu ta yi ciki ta haifi ɗa. Ta sa masa suna Ruben, gama ta ce, “Domin Ubangiji ya ga wahalata. Tabbatacce mijina zai ƙaunace ni yanzu.”
Lea nomako ich kendo nonywolo wuowi. Nowacho niya, “Jehova Nyasaye oseneno chandruokna, kendo koro chwora biro hera.” Omiyo nochake ni Reuben.
33 Ta sāke yin ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Gama Ubangiji ya ji cewa ba a ƙaunata, ya ba ni wannan shi ma.” Saboda haka ta ba shi suna Simeyon.
Nochako omako ich, monywolo wuowi moro. Nowacho niya, “Jehova Nyasaye osemiya wuowi machielo nimar nowinjo ka chwora ok ohera.” Omiyo nochake ni Simeon.
34 Har yanzu ta yi ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Yanzu, a ƙarshe mijina zai manne mini, gama na haifa masa’ya’ya maza uku.” Saboda haka ta ba shi suna Lawi.
Nochako omako ich, kendo ochako onywolo wuowi. Nowacho niya, “Koro chwora biro padore kuoma nikech asenywolone yawuowi adek.” Omiyo nochake ni Lawi.
35 Ta sāke yin ciki, sa’ad da ta haifi ɗa sai ta ce, “A wannan lokaci zan yabi Ubangiji.” Saboda haka ta ba shi suna Yahuda. Sa’an nan ta daina haihuwa.
Nochako omako ich, kendo kane ochako onywolo wuowi nowacho niya, “Koro abiro pako Jehova Nyasaye.” Omiyo nochake ni Juda. Bangʼ mano noweyo nywolo nyithindo.

< Farawa 29 >