< Farawa 28 >

1 Saboda haka Ishaku ya kira Yaƙub, ya kuma albarkace shi, sa’an nan ya umarce shi ya ce, “Kada ka auri mace daga Kan’ana.
پس اسحاق یعقوب را فرا‌خوانده، او را برکت داد و به او گفت: «با هیچ‌یک از این دختران کنعانی ازدواج نکن.
2 Tashi nan da nan ka tafi Faddan Aram, zuwa gidan mahaifin mahaifiyarka Betuwel. Ka ɗauko wa kanka mata a can daga cikin’ya’ya matan Laban ɗan’uwan mahaifiyarka.
بلکه بلند شو و به فَدّان‌اَرام، به خانهٔ پدر بزرگت بتوئیل برو و با یکی از دختران دایی خود لابان ازدواج کن.
3 Bari Allah Maɗaukaki yă albarkace ka, yă kuma sa ka yi ta haihuwa ka riɓaɓɓanya har ka zama ƙungiyar jama’o’i.
خدای قادر مطلق تو را برکت دهد و به تو فرزندان بسیار ببخشد تا از نسل تو قبایل زیادی به وجود آیند!
4 Bari Allah yă ba ka da kuma zuriyarka albarkar da ya ba wa Ibrahim, don ka amshi ƙasar da kake baƙunci, ƙasar da Allah ya ba wa Ibrahim.”
او برکتی را که به ابراهیم وعده داد، به تو و نسل تو دهد تا صاحب این سرزمینی که خدا آن را به ابراهیم بخشیده و اکنون در آن غریب هستیم بشوی.»
5 Sa’an nan Ishaku ya sallami Yaƙub, ya kuwa tafi Faddan Aram, zuwa wurin Laban ɗan Betuwel mutumin Aram. Laban ne ɗan’uwan Rebeka, wadda take mahaifiyar Yaƙub da Isuwa.
پس اسحاق یعقوب را روانه نمود و او به فَدّان‌اَرام، نزد دایی خود لابان، پسر بتوئیل ارامی رفت.
6 Yanzu Isuwa ya san cewa Ishaku ya albarkaci Yaƙub ya kuma aike shi zuwa Faddan Aram don yă auri mata daga can, ya kuma san cewa sa’ad da ya albarkace shi, ya umarce shi cewa, “Kada ka auro wata mace daga cikin Kan’aniyawa,”
عیسو فهمید که پدرش اسحاق از دختران کنعانی بیزار است، و یعقوب را از گرفتن زن کنعانی برحذر داشته و پس از برکت دادن او، وی را به فَدّان‌اَرام فرستاده است تا از آنجا زنی برای خود بگیرد و یعقوب هم از پدر و مادر خود اطاعت کرده به فَدّان‌اَرام رفته است.
7 ya kuma san cewa Yaƙub ya yi biyayya da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa, ya kuwa tafi Faddan Aram.
8 Sai Isuwa ya gane cewa matan Kan’aniyawa ba su gamshi mahaifinsa Ishaku ba;
9 saboda haka sai ya tafi wurin Ishmayel ya auri Mahalat,’yar’uwar Nebayiwot da kuma’yar Ishmayel ɗan Ibrahim, ban da matan da yake da su.
پس عیسو هم نزد خاندان عمویش اسماعیل که پسر ابراهیم بود رفت و علاوه بر زنانی که داشت، محلت، دختر اسماعیل، خواهر نبایوت را نیز به زنی گرفت.
10 Yaƙub ya bar Beyersheba ya kama hanyar Haran.
پس یعقوب بئرشبع را به قصد حران ترک نمود.
11 Sa’ad da ya kai wani wuri, sai ya dakata domin yă kwana, gama rana ta riga ta fāɗi. Ya ɗauki dutse daga cikin duwatsun wurin, ya sa shi ya zama matashin kansa, sa’an nan ya kwanta don yă yi barci.
همان روز پس از غروب آفتاب، به مکانی رسید و خواست شب را در آنجا به سر برد. پس سنگی برداشت و زیر سر خود نهاده، همان جا خوابید.
12 Ya yi mafarki inda ya ga wata matakalar hawa, tsaye a ƙasa, kanta ta kai sama, mala’ikun Allah kuwa suna hawa, suna sauka a kanta.
در خواب نردبانی را دید که پایهٔ آن بر زمین بود و سرش به آسمان می‌رسد و فرشتگان خدا از آن بالا و پایین می‌روند
13 A can bisantaUbangiji ya tsaya, ya kuma ce, “Ni ne Ubangiji Allah na mahaifinka Ibrahim da kuma Allah na Ishaku. Zan ba ka, kai da kuma zuriyarka, ƙasar da kake kwance a kai.
و خداوند بر بالای نردبان ایستاده است. سپس خداوند چنین فرمود: «من خداوند، خدای ابراهیم و خدای پدرت اسحاق هستم. زمینی که روی آن خوابیده‌ای از آن توست. من آن را به تو و نسل تو می‌بخشم.
14 Zuriyarka za tă zama kamar ƙurar ƙasa, za ka kuma bazu zuwa yamma da kuma gabas, zuwa arewa da kuma kudu. Dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka da kuma ta wurin’ya’yanka.
فرزندان تو چون غبار زمین، بی‌شمار خواهند شد! از مشرق تا مغرب، و از شمال تا جنوب را خواهند پوشانید. تمامی مردمِ زمین توسط تو و نسل تو برکت خواهند یافت.
15 Ina tare da kai, zan lura da kai duk inda ka tafi, zan kuma dawo da kai zuwa wannan ƙasa. Ba zan rabu da kai ba sai na cika abin da na yi maka alkawari.”
هر جا که بروی من با تو خواهم بود و از تو حمایت نموده، دوباره تو را به سلامت به این سرزمین باز خواهم آورد. تا آنچه به تو وعده داده‌ام به جا نیاورم تو را رها نخواهم کرد.»
16 Sa’ad da Yaƙub ya farka daga barci, sai ya yi tunani ya ce, “Tabbatacce Ubangiji yana a wannan wuri, ban kuwa sani ba.”
سپس یعقوب از خواب بیدار شد و گفت: «بدون شک خداوند در این مکان حضور دارد و من ندانستم!»
17 Ya ji tsoro, ya kuma ce, “Wane irin wuri ne mai banrazana haka! Lalle wannan gidan Allah ne, kuma nan ne ƙofar sama.”
پس ترسید و گفت: «این چه جای ترسناکی است! این است خانهٔ خدا و این است دروازهٔ آسمان!»
18 Kashegari da sassafe, sai Yaƙub ya ɗauki dutsen da ya yi matashin kai da shi, ya kafa shi al’amudi, ya kuma zuba mai a kansa.
پس یعقوب صبح زود برخاست و سنگی را که زیر سر نهاده بود، چون ستونی بر پا داشت و بر آن روغن زیتون ریخت.
19 Ya kira wannan wuri Betel ko da yake dā ana kiran birnin Luz ne.
او آن مکان را بیت‌ئیل (یعنی «خانهٔ خدا») نامید. (نام این شهر پیش از آن لوز بود.)
20 Sa’an nan Yaƙub ya yi alkawari cewa, “In Allah zai kasance tare da ni yă kuma lura da ni a wannan tafiya, yă kuma ba ni abinci in ci da tufafi in sa,
آنگاه یعقوب نذر کرده گفت: «اگر خدا در این سفر با من باشد و مرا محافظت نماید و خوراک و پوشاک به من بدهد،
21 har in dawo lafiya zuwa gidan mahaifina, to, Ubangiji zai zama Allahna
و مرا به سلامت به خانهٔ پدرم بازگرداند، آنگاه یهوه خدای من خواهد بود؛
22 kuma wannan dutsen da na kafa al’amudi, zai zama gidan Allah, kuma dukan abin da ka ba ni zan ba ka kashi ɗaya bisa goma.”
و این ستونی که به عنوان یادبود بر پا کردم، مکانی خواهد بود برای عبادت خدا و ده‌یک هر چه را که او به من بدهد به وی باز خواهم داد.»

< Farawa 28 >