< Farawa 28 >
1 Saboda haka Ishaku ya kira Yaƙub, ya kuma albarkace shi, sa’an nan ya umarce shi ya ce, “Kada ka auri mace daga Kan’ana.
Isaac called for Jacob and blessed him. “Don't marry a Canaanite woman,” he ordered him.
2 Tashi nan da nan ka tafi Faddan Aram, zuwa gidan mahaifin mahaifiyarka Betuwel. Ka ɗauko wa kanka mata a can daga cikin’ya’ya matan Laban ɗan’uwan mahaifiyarka.
“Leave right away and go to Paddan-aram, to the home of Bethuel, your mother's father. Find yourself a wife there—a daughter of Laban, your mother's brother.
3 Bari Allah Maɗaukaki yă albarkace ka, yă kuma sa ka yi ta haihuwa ka riɓaɓɓanya har ka zama ƙungiyar jama’o’i.
God Almighty bless you and may your descendants be so numerous that you become the ancestor of many nations.
4 Bari Allah yă ba ka da kuma zuriyarka albarkar da ya ba wa Ibrahim, don ka amshi ƙasar da kake baƙunci, ƙasar da Allah ya ba wa Ibrahim.”
May he grant you and your descendants the same blessing he gave to Abraham, so that you may take over the land where you now live as a foreigner, the land God gave to Abraham.”
5 Sa’an nan Ishaku ya sallami Yaƙub, ya kuwa tafi Faddan Aram, zuwa wurin Laban ɗan Betuwel mutumin Aram. Laban ne ɗan’uwan Rebeka, wadda take mahaifiyar Yaƙub da Isuwa.
So Isaac sent Jacob on his way. He traveled to Paddan-aram, to Laban, son of Bethuel the Aramean. Laban was the brother of Rebekah, the mother of Jacob and Esau.
6 Yanzu Isuwa ya san cewa Ishaku ya albarkaci Yaƙub ya kuma aike shi zuwa Faddan Aram don yă auri mata daga can, ya kuma san cewa sa’ad da ya albarkace shi, ya umarce shi cewa, “Kada ka auro wata mace daga cikin Kan’aniyawa,”
Esau found out that Isaac had blessed Jacob and had sent him to Paddan-aram to find a wife there, and that when he blessed him he ordered him, “Don't marry a Canaanite woman.”
7 ya kuma san cewa Yaƙub ya yi biyayya da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa, ya kuwa tafi Faddan Aram.
He also discovered that Jacob had done what his father and mother told him and had left for Paddan-aram.
8 Sai Isuwa ya gane cewa matan Kan’aniyawa ba su gamshi mahaifinsa Ishaku ba;
This made Esau realize how much his father disliked Canaanite women.
9 saboda haka sai ya tafi wurin Ishmayel ya auri Mahalat,’yar’uwar Nebayiwot da kuma’yar Ishmayel ɗan Ibrahim, ban da matan da yake da su.
So he went to Ishmael's family and married an additional wife—Mahalath, the daughter of Ishmael, Abraham's son, the sister of Nebaioth.
10 Yaƙub ya bar Beyersheba ya kama hanyar Haran.
In the meantime Jacob had set off from Beersheba on his way to Haran.
11 Sa’ad da ya kai wani wuri, sai ya dakata domin yă kwana, gama rana ta riga ta fāɗi. Ya ɗauki dutse daga cikin duwatsun wurin, ya sa shi ya zama matashin kansa, sa’an nan ya kwanta don yă yi barci.
He arrived after sunset at a particular place and stopped there for the night. He picked up a stone, put it under his head, lay down and went to sleep.
12 Ya yi mafarki inda ya ga wata matakalar hawa, tsaye a ƙasa, kanta ta kai sama, mala’ikun Allah kuwa suna hawa, suna sauka a kanta.
He dreamed he saw a stairway that started on earth, and the top reached all the way into heaven. He saw God's angels going up and down on it.
13 A can bisantaUbangiji ya tsaya, ya kuma ce, “Ni ne Ubangiji Allah na mahaifinka Ibrahim da kuma Allah na Ishaku. Zan ba ka, kai da kuma zuriyarka, ƙasar da kake kwance a kai.
Then he saw the Lord standing over him, who said, “I am the Lord, the God of your father Abraham, and the God of Isaac. I'm giving you and your descendants the land you're lying on.
14 Zuriyarka za tă zama kamar ƙurar ƙasa, za ka kuma bazu zuwa yamma da kuma gabas, zuwa arewa da kuma kudu. Dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka da kuma ta wurin’ya’yanka.
Your descendants will be as numerous as the dust of the earth, and will spread out west and east, and north and south. Everyone on earth will be blessed by your descendants.
15 Ina tare da kai, zan lura da kai duk inda ka tafi, zan kuma dawo da kai zuwa wannan ƙasa. Ba zan rabu da kai ba sai na cika abin da na yi maka alkawari.”
Listen! I am with you and will take care of you wherever you go. I will bring you back to this country. I won't leave you because I'm going to do what I've promised you.”
16 Sa’ad da Yaƙub ya farka daga barci, sai ya yi tunani ya ce, “Tabbatacce Ubangiji yana a wannan wuri, ban kuwa sani ba.”
When Jacob woke up he said to himself, “The Lord is right here, in this place, and I didn't realize it!”
17 Ya ji tsoro, ya kuma ce, “Wane irin wuri ne mai banrazana haka! Lalle wannan gidan Allah ne, kuma nan ne ƙofar sama.”
He became frightened and said, “This is a scary place! It must be the house of God and the entrance to heaven.”
18 Kashegari da sassafe, sai Yaƙub ya ɗauki dutsen da ya yi matashin kai da shi, ya kafa shi al’amudi, ya kuma zuba mai a kansa.
When Jacob got up in the morning he took the stone he'd put under his head and set it upright as a stone pillar and poured some olive oil on it.
19 Ya kira wannan wuri Betel ko da yake dā ana kiran birnin Luz ne.
He named the place “Bethel,” (previously it was called Luz).
20 Sa’an nan Yaƙub ya yi alkawari cewa, “In Allah zai kasance tare da ni yă kuma lura da ni a wannan tafiya, yă kuma ba ni abinci in ci da tufafi in sa,
Jacob also made a solemn promise, saying, “God, if you will be with me, and take care of me on my journey, and give me food to eat and clothes to wear
21 har in dawo lafiya zuwa gidan mahaifina, to, Ubangiji zai zama Allahna
so I can return safely to my father's home, then you Lord will be my God.
22 kuma wannan dutsen da na kafa al’amudi, zai zama gidan Allah, kuma dukan abin da ka ba ni zan ba ka kashi ɗaya bisa goma.”
This stone pillar that I've set up will be the house of God, and I will give you one tenth of all you give me.”