< Farawa 28 >
1 Saboda haka Ishaku ya kira Yaƙub, ya kuma albarkace shi, sa’an nan ya umarce shi ya ce, “Kada ka auri mace daga Kan’ana.
Then Isaac sent for Jacob, and blessing him, said, Do not take a wife from among the women of Canaan;
2 Tashi nan da nan ka tafi Faddan Aram, zuwa gidan mahaifin mahaifiyarka Betuwel. Ka ɗauko wa kanka mata a can daga cikin’ya’ya matan Laban ɗan’uwan mahaifiyarka.
But go to Paddan-aram, to the house of Bethuel, your mother's father, and there get yourself a wife from the daughters of Laban, your mother's brother.
3 Bari Allah Maɗaukaki yă albarkace ka, yă kuma sa ka yi ta haihuwa ka riɓaɓɓanya har ka zama ƙungiyar jama’o’i.
And may God, the Ruler of all, give you his blessing, giving you fruit and increase, so that you may become an army of peoples.
4 Bari Allah yă ba ka da kuma zuriyarka albarkar da ya ba wa Ibrahim, don ka amshi ƙasar da kake baƙunci, ƙasar da Allah ya ba wa Ibrahim.”
And may God give you the blessing of Abraham, to you and to your seed, so that the land of your wanderings, which God gave to Abraham, may be your heritage.
5 Sa’an nan Ishaku ya sallami Yaƙub, ya kuwa tafi Faddan Aram, zuwa wurin Laban ɗan Betuwel mutumin Aram. Laban ne ɗan’uwan Rebeka, wadda take mahaifiyar Yaƙub da Isuwa.
So Isaac sent Jacob away: and he went to Paddan-aram, to Laban, son of Bethuel the Aramaean, the brother of Rebekah, the mother of Jacob and Esau.
6 Yanzu Isuwa ya san cewa Ishaku ya albarkaci Yaƙub ya kuma aike shi zuwa Faddan Aram don yă auri mata daga can, ya kuma san cewa sa’ad da ya albarkace shi, ya umarce shi cewa, “Kada ka auro wata mace daga cikin Kan’aniyawa,”
So when Esau saw that Isaac had given Jacob his blessing, and sent him away to Paddan-aram to get a wife for himself there, blessing him and saying to him, Do not take a wife from among the women of Canaan;
7 ya kuma san cewa Yaƙub ya yi biyayya da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa, ya kuwa tafi Faddan Aram.
And that Jacob had done as his father and mother said and had gone to Paddan-aram;
8 Sai Isuwa ya gane cewa matan Kan’aniyawa ba su gamshi mahaifinsa Ishaku ba;
It was clear to Esau that his father had no love for the women of Canaan,
9 saboda haka sai ya tafi wurin Ishmayel ya auri Mahalat,’yar’uwar Nebayiwot da kuma’yar Ishmayel ɗan Ibrahim, ban da matan da yake da su.
So Esau went to Ishmael and took Mahalath, the daughter of Abraham's son Ishmael, the sister of Nebaioth, to be his wife in addition to the wives he had.
10 Yaƙub ya bar Beyersheba ya kama hanyar Haran.
So Jacob went out from Beer-sheba to go to Haran.
11 Sa’ad da ya kai wani wuri, sai ya dakata domin yă kwana, gama rana ta riga ta fāɗi. Ya ɗauki dutse daga cikin duwatsun wurin, ya sa shi ya zama matashin kansa, sa’an nan ya kwanta don yă yi barci.
And coming to a certain place, he made it his resting-place for the night, for the sun had gone down; and he took one of the stones which were there, and putting it under his head he went to sleep in that place.
12 Ya yi mafarki inda ya ga wata matakalar hawa, tsaye a ƙasa, kanta ta kai sama, mala’ikun Allah kuwa suna hawa, suna sauka a kanta.
And he had a dream, and in his dream he saw steps stretching from earth to heaven, and the angels of God were going up and down on them.
13 A can bisantaUbangiji ya tsaya, ya kuma ce, “Ni ne Ubangiji Allah na mahaifinka Ibrahim da kuma Allah na Ishaku. Zan ba ka, kai da kuma zuriyarka, ƙasar da kake kwance a kai.
And he saw the Lord by his side, saying, I am the Lord, the God of Abraham your father, and the God of Isaac: I will give to you and to your seed this land on which you are sleeping.
14 Zuriyarka za tă zama kamar ƙurar ƙasa, za ka kuma bazu zuwa yamma da kuma gabas, zuwa arewa da kuma kudu. Dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka da kuma ta wurin’ya’yanka.
Your seed will be like the dust of the earth, covering all the land to the west and to the east, to the north and to the south: you and your seed will be a name of blessing to all the families of the earth.
15 Ina tare da kai, zan lura da kai duk inda ka tafi, zan kuma dawo da kai zuwa wannan ƙasa. Ba zan rabu da kai ba sai na cika abin da na yi maka alkawari.”
And truly, I will be with you, and will keep you wherever you go, guiding you back again to this land; and I will not give you up till I have done what I have said to you.
16 Sa’ad da Yaƙub ya farka daga barci, sai ya yi tunani ya ce, “Tabbatacce Ubangiji yana a wannan wuri, ban kuwa sani ba.”
And Jacob, awaking from his sleep, said, Truly, the Lord is in this place and I was not conscious of it.
17 Ya ji tsoro, ya kuma ce, “Wane irin wuri ne mai banrazana haka! Lalle wannan gidan Allah ne, kuma nan ne ƙofar sama.”
And fear came on him, and he said, This is a holy place; this is nothing less than the house of God and the doorway of heaven.
18 Kashegari da sassafe, sai Yaƙub ya ɗauki dutsen da ya yi matashin kai da shi, ya kafa shi al’amudi, ya kuma zuba mai a kansa.
And early in the morning Jacob took the stone which had been under his head, and put it up as a pillar and put oil on it.
19 Ya kira wannan wuri Betel ko da yake dā ana kiran birnin Luz ne.
And he gave that place the name of Beth-el, but before that time the town was named Luz.
20 Sa’an nan Yaƙub ya yi alkawari cewa, “In Allah zai kasance tare da ni yă kuma lura da ni a wannan tafiya, yă kuma ba ni abinci in ci da tufafi in sa,
Then Jacob took an oath, and said, If God will be with me, and keep me safe on my journey, and give me food and clothing to put on,
21 har in dawo lafiya zuwa gidan mahaifina, to, Ubangiji zai zama Allahna
So that I come again to my father's house in peace, then I will take the Lord to be my God,
22 kuma wannan dutsen da na kafa al’amudi, zai zama gidan Allah, kuma dukan abin da ka ba ni zan ba ka kashi ɗaya bisa goma.”
And this stone which I have put up for a pillar will be God's house: and of all you give me, I will give a tenth part to you.