< Farawa 27 >

1 Sa’ad da Ishaku ya tsufa idanunsa suka raunana har ba ya iya gani, sai ya kira Isuwa babban ɗansa ya ce masa, “Ɗana.” Isuwa kuwa ya amsa, ya ce “Ga ni.”
In pacl se inge Isaac el matuoh ac mutawauk in sulonginla. El sapla solalma Esau, wen se ma matu natul, ac fahk nu sel, “Wen nutik!” Esau el topuk, “Nga inge.”
2 Ishaku ya ce, “Yanzu na tsufa kuma ban san ranar mutuwata ba.
Isaac el fahk, “Kom liye lah nga matuoh ac apkuran in misa.
3 Saboda haka yanzu, ka ɗauki makamanka, kwari da bakanka, ka tafi jeji ka farauto mini nama.
Us mwe pisr nutum an ac sruokma soko kosro inima an nak.
4 Ka shirya mini irin abinci mai daɗin da nake so, ka kawo mini in ci, domin in sa maka albarka kafin in mutu.”
Orauk kain in mongo yuyu se ma nga lungsena kang ah, ac use nu yuruk. Nga ac mongo tari, na nga fah akinsewowoyekomla meet liki nga misa.”
5 Ashe, Rebeka tana ji sa’ad da Ishaku ya yi wa ɗansa Isuwa magana. Da Isuwa ya tafi jeji don yă farauto nama yă kawo,
Ke pacl se Isaac el kaskas nu sel Esau inge, Rebecca el lohng na. Ouinge ke Esau el illa som in sruh kosro,
6 sai Rebeka ta ce wa ɗanta Yaƙub, “Ka ji nan, na ji mahaifinka ya ce wa ɗan’uwanka Isuwa,
Rebecca el fahk nu sel Jacob, “Nga lohng lah ingena papa tomom fahk nu sel Esau ange:
7 ‘Kawo mini nama ka shirya mini abinci mai daɗi don in ci, in sa maka albarka a gaban Ubangiji kafin in mutu.’
‘Use soko kosro inima an ac akmolyela nak. Tukun nga ac mongo tari, na nga ac akinsewowoye kom ye mutun LEUM GOD meet liki nga misa.’”
8 Saboda haka ɗana, ka saurara da kyau ka kuma yi abin da na faɗa maka.
Rebecca el tafwela ac fahk, “Wen nutik, porongo akwoye ac oru ma nga fahk uh.
9 Je garke ka kawo mini awaki biyu kyawawa, domin in shirya abinci mai daɗi wa mahaifinka, kamar yadda dai yake so.
Fahla nu ke un kosro uh, ac srela lukwa nani fusr na fact an. Use ngan tuh akmolyela ac orala kain mongo se ma papa tomom el arulana lungse yohk ah.
10 Sa’an nan ka kai wa mahaifinka yă ci, domin yă sa maka albarka kafin yă mutu.”
Kom ku in usla nu yorol elan kang, elan mau akinsewowoyekomla meet liki el misa.”
11 Yaƙub ya ce wa mahaifiyarsa Rebeka, “Amma ɗan’uwana Isuwa mutum ne mai gashi a jiki, ni kuma jikina sumul yake.
Tusruktu Jacob el fahk nu sin nina kial, “Kom etu na lah manol Esau unacna, a monuk fwel.
12 A ce baba ya tattaɓa ni fa? Zai zama kamar ina ruɗunsa ne, wannan fa zai jawo mini la’ana a maimakon albarka.”
Papa el ac tuh kahl monuk ac konauk lah nga kiapwel. Ac fin ange, ac tia akinsewowoyeyuk nga, a el ac selngaiyuwi.”
13 Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, bari la’anar tă fāɗo a kaina. Kai dai yi abin da na faɗa, jeka ka kawo mini su.”
Nina kial ah fahk, “Wen nutik, lela kutena selnga nu sum an in oan fuk. Oru na ma nga fahk uh. Fahla use nani an.”
14 Sai ya tafi ya kamo su, ya kawo wa mahaifiyarsa, ta kuwa shirya abinci mai daɗi, yadda mahaifinsa yake so.
Ouinge el som sruokya nani uh, ac use nu yurin nina kial, ac el orala kain mongo se ma papa sac arulana lungse ah.
15 Sa’an nan Rebeka ta ɗauki riguna mafi kyau na Isuwa babban ɗanta, waɗanda take da su a gida ta sa wa ƙaramin ɗanta Yaƙub.
Na Rebecca el srukak nuknuk se ma wo emeet lal Esau su oan yorol in lohm uh, ac sang nokmulang Jacob.
16 Sai ta mamanne gashin awakin nan biyu a hannuwansa da bayan wuyarsa wanda ba gashi.
El sang kulun nani uh nu fin paol Jacob, oayapa nu fin acn ma tia unacna ke kawal.
17 Sa’an nan ta ba wa ɗanta Yaƙub abinci mai daɗi da kuma burodin da ta yi.
Na el sang mwe mongo yuyu sac, ac bread ma el munanla nu sel.
18 Shi kuwa ya tafi wurin mahaifinsa ya ce, “Babana.” Shi kuma ya amsa “I, ɗana, wane ne?”
Na Jacob el som nu yurin papa tumal ah, ac fahk, “Papa!” El topuk, “Nga inge. Su kac sumtal ingan?”
19 Yaƙub ya ce wa mahaifinsa, “Ni ne Isuwa ɗan farinka. Na yi yadda ka faɗa mini. Ina roƙonka tashi ka zauna ka ci naman, domin ka sa mini albarkarka.”
Jacob el fahk, “Nga Esau, wen matu nutum. Ma kom sap ngan orala nom ah pa inge. Tukakek mongoi, kom in tari akinsewowoyeyula.”
20 Ishaku ya tambayi ɗansa, “Yaya aka yi ka samo shi da sauri haka, ɗana?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Ubangiji Allahnka ne ya ba ni nasara.”
Isaac el fahk nu sin wen natul, “Ku kom oru fuka tuh kom arulana sa konauk?” Jacob el fahk, LEUM GOD lom El kasreyu konauk.”
21 Sai Ishaku ya ce wa Yaƙub, “Zo kusa don in taɓa ka, ɗana, domin in sani ko tabbatacce kai ne ɗana Isuwa ko babu.”
Isaac el fahk nu sel Jacob, “Kaluku ngan kahlkomi. Pwayena lah kom pa Esau?”
22 Yaƙub kuwa ya matsa kusa da mahaifinsa Ishaku, wanda ya tattaɓa shi, sa’an nan ya ce, “Muryan nan dai, muryar Yaƙub ce, amma hannuwan, hannuwan Isuwa ne.”
Jacob el kalukyang nu yurin papa tumal ah, na Isaac el kahlilya ac fahk, “Pusrem oana pusracl Jacob, a poum paol Esau.”
23 Bai gane shi ba, gama hannuwansa suna da gashi kamar na ɗan’uwansa Isuwa, saboda haka ya albarkace shi.
El tiana akilenul Jacob, mweyen paol oana paol Esau. El akola elan akinsewowoyal,
24 Ya tambaya, “Tabbatacce kai ne ɗana Isuwa?” Ya amsa ya ce “Ni ne.”
na el sifilpa siyuk, “Ku pwayena kom pa Esau?” Ac el topuk, “Aok, pwaye.”
25 Sa’an nan ya ce, “Ɗana, kawo mini naman da ka farauto in ci, domin in sa maka albarka.” Yaƙub ya kawo masa ya kuwa ci; ya kuma kawo masa ruwan inabi ya kuma sha.
Isaac el fahk, “Kolma mongo an nu yuruk ngan kang. Nga ac mongo tari, na nga fah akinsewowoyekomla.” Jacob el kolang nu yorol, ac el oayapa sang wain nimal.
26 Sa’an nan mahaifinsa Ishaku ya ce masa, “Zo nan, ɗana ka sumbace ni.”
Na papa tumal ah fahk nu sel, “Kaluku, wen nutik, ac ngokya mutuk.”
27 Saboda haka ya je gunsa ya sumbace shi. Sa’ad da Ishaku ya ji ƙanshin rigunansa, sai ya sa masa albarka ya ce, “Aha, ƙanshin ɗana yana kama da ƙanshin jejin da Ubangiji ya sa wa albarka ne.
Ac ke el kalukyang in ngok mutal, Isaac el ngokak nuknuk lal, ouinge el akinsewowoyalla. Ac el fahk, “Foulin wen nutik uh loslos oana foulin ima ma LEUM GOD El akinsewowoye.
28 Allah yă ba ka daga raɓar sama da kuma yalwar ƙasa, yalwar hatsi da sabon ruwan inabi.
God Elan asot nu sum aunfong inkusrao me, ac akkasrupye fohkon acn in ima lom! Ac lela Elan akpusye wheat ac wain lom!
29 Bari al’ummai su bauta maka mutane kuma su rusuna maka. Ka zama shugaba a kan’yan’uwanka bari kuma’ya’yan mahaifiyarka su rusuna maka. Bari waɗanda suka la’anta ka, su la’antu; waɗanda kuma suka sa maka albarka, su sami albarka.”
Mutunfacl puspis in kulansap nu sum, ac mwet uh in faksufi ye motom. Lela kom in leum fin sou lom nukewa, ac fwilin tulik nutin nina kiom in akfulatye kom. Lela elos su selngawi kom in selngawiyuk, ac elos su akinsewowoye kom in akinsewowoyeyuk.”
30 Bayan Ishaku ya gama sa masa albarka, Yaƙub yana fita daga mahaifinsa ke nan, sai ga ɗan’uwansa Isuwa ya dawo daga farauta.
Isaac el akinsewowoyela Jacob tari, na Jacob el tuyak som. Tia paht na Esau, tamulel lal, el foloko liki sruh kosro lal.
31 Shi ma ya shirya abinci mai daɗi ya kawo wa mahaifinsa. Sa’an nan ya ce masa, “Babana, tashi ka zauna ka ci daga abin da na farauto, domin ka sa mini albarka.”
El oayapa akmolyela mwe mongo na yuyu ac usla nu yurin papa tumal. Ac el fahk, “Papa, tukakek kang kutu ikwen kosro nga us tuku nom inge, kom in tari akinsewowoyeyula.”
32 Mahaifinsa Ishaku ya tambaye shi, “Wane ne kai?” Ya amsa, “Ni ne ɗanka, ɗan farinka, Isuwa.”
Ac Isaac el siyuk, “Ku su kom an?” Ac Esau el fahk, “Nga Esau, wounse mukul nutum.”
33 Ishaku ya yi makyarkyata ƙwarai ya ce, “To, wane ne wannan da ya farauto nama ya kawo mini kafin ka zo, har na ci na kuma sa masa albarka? Tabbatacce zai zama mai albarka!”
Manol Isaac nufon rarrarak, ac el siyuk, “Fin angan, ac su sruhk uniya kosro soko use nak ah? Nga mongo tufahna tari na pa kom utyak. Nga sang nufon mwe insewowo luk nu sel, ac inge ac ma na lal nwe tok.”
34 Sa’ad da Isuwa ya ji kalmomin mahaifinsa, sai ya fashe da kuka mai zafi kuma da ƙarfi, ya ce wa mahaifinsa, “Ka albarkace ni, ni ma, baba!”
Ke Esau el lohng ma inge, el liksreni tung ac wowoyak, ac fahk, “Papa, akinsewowoyeyu pac!”
35 Amma ya ce, “Ɗan’uwanka ya zo da makirci ya karɓi albarkarka.”
Isaac el fahk, “Tamulel lom el tuku ac kiapweyula. El eisla tari mwe insewowo lom.”
36 Isuwa ya ce, “Ba saboda haka ne aka raɗa masa suna Yaƙub ba? Ya yi mini ƙwace sau biyu ke nan; ya ƙwace mini matsayina na ɗan fari, ga shi yanzu kuma ya karɓi albarkata.” Sa’an nan ya yi tambaya, “Ba sauran albarkar da ka rage mini?”
Esau el fahk, “Pacl luola el aklalfonyeyu. Fal in pangpang inel Jacob. El eisla wal lun wounse luk, ac inge el eisla pac mwe insewowo luk. Ya wangin na pwaye mwe insewowo lula kom filiya luk?”
37 Ishaku ya amsa wa Isuwa, “Na mai da shi shugaba a kanka, na sa dukan dangoginsa su zama bayinsa, na kuma ba shi hatsi da sabon ruwan inabi. Saboda haka me kuma zan yi maka ɗana?”
Isaac el topuk, “Nga orala tari elan leum fom, ac tuh mwet wial nukewa fah mwet kulansap lal. Nga sang nu sel wheat ac wain. Inge, wen nutik, wangin ma nga ku in oru nu sum!”
38 Isuwa ya ce wa mahaifinsa, “Iyakar albarkar da kake da ita ke nan, baba? Ka albarkace ni ni ma, baba!” Sai Isuwa ya ɗaga murya ya yi kuka.
Esau el sifil pacna kwafe nu sin papa tumal ah, ac fahk, “Ya mwe insewowo sefanna lom, papa? Akinsewowoyeyu pac!” Na el sifilpa tung.
39 Mahaifinsa Ishaku ya amsa masa ya ce, “Ga shi, ni’imar ƙasar za tă nisanci mazauninka. Raɓar samaniya can ƙwanƙoli za tă nisance ka.
Na Isaac el fahk nu sel, “Wangin aunfong nu sum inkusrao me, Wangin acn wo ke ima uh lom.
40 Za ka rayu ta wurin takobi za ka kuwa bauta wa ɗan’uwanka. Amma sa’ad da ka ɓalle, za ka kakkarye karkiyarsa daga wuyanka.”
Cutlass nutum pa ac sot enenu lom, Ac kom fah kulansupu tamulel lom. Tusruktu kom fin tuyak lainul, Kom ac fah pisrla liki ye nununku lal.”
41 Isuwa ya riƙe Yaƙub a zuciya saboda albarkar da mahaifinsa ya sa masa. Ya ce wa kansa, “Kwanakin mutuwar mahaifina sun yi kusa; sa’an nan zan kashe ɗan’uwana Yaƙub.”
Esau el arulana srungalla Jacob, mweyen papa tumal ah tuh sang mwe insewowo ah nu sel. Ac el nunku sel sifacna, “Akuranna sun pacl in eoksra ke misa lal papa. Fin safla, na nga ac unilya Jacob.”
42 Sa’ad da aka faɗa wa Rebeka abin da babban ɗanta Isuwa ya faɗa, sai ta kira ɗanta Yaƙub ta ce masa, “Ɗan’uwanka Isuwa yana ta’azantar da kansa da tunanin kashe ka.
Tusruktu ke Rebecca el lohng ke akoo lal Esau ah, el sapla solalma Jacob ac fahk nu sel, “Esau tamulel lom, el akoo in foloksak nu sum ac unikomi.
43 To, fa, ɗana, yi abin da na ce; gudu nan take zuwa wurin ɗan’uwana Laban a Haran.
Wen nutik, inge kom oru ma nga fahk uh. Fahla ingena nwe yorol Laban tamulel luk in acn Haran,
44 Zauna tare da shi na ɗan lokaci sai ɗan’uwanka ya huce.
ac muta yorol nwe ke na kasrkusrak lun tamulel lom ohula
45 Sa’ad da ɗan’uwanka ya daina fushi da kai, ya kuma manta da abin da ka yi masa, zan aika don ka dawo daga can. Don me zan rasa ku biyu a rana guda?”
ac el mulkunla ma kom oru nu sel inge. Tok nga ac fah supwaot sie mwet in folokinkomme. Mwe mea wen luo nutik in tukenina wanginla ke len sefanna?”
46 Sa’an nan Rebeka ta ce wa Ishaku, “Ni fa na gaji da matan Hittiyawan nan. In Yaƙub ya auri mata daga cikin matan ƙasan nan, wato, daga matan Hittiyawa irin waɗannan, rayuwata ba za tă daɗa mini kome ba.”
Rebecca el fahk nu sel Isaac, “Nga keokla sin mutan Hit kial Esau inge. Jacob el fin payukyak pac sin sie mutan Hit, ac mansis pacna ngan tari misa.”

< Farawa 27 >