< Farawa 27 >

1 Sa’ad da Ishaku ya tsufa idanunsa suka raunana har ba ya iya gani, sai ya kira Isuwa babban ɗansa ya ce masa, “Ɗana.” Isuwa kuwa ya amsa, ya ce “Ga ni.”
Or Isaac devint vieux et ses yeux s’obscurcirent, et il ne pouvait plus voir: il appela Esaü, son fils aîné, et lui dit: Mon fils. Celui-ci répondit: Me voici.
2 Ishaku ya ce, “Yanzu na tsufa kuma ban san ranar mutuwata ba.
Et son père: Tu vois, lui dit-il, que je suis devenu vieux et que j’ignore le jour de ma mort.
3 Saboda haka yanzu, ka ɗauki makamanka, kwari da bakanka, ka tafi jeji ka farauto mini nama.
Prends tes armes, ton carquois et ton arc, et sors dehors; et quand à la chasse tu auras pris quelque chose,
4 Ka shirya mini irin abinci mai daɗin da nake so, ka kawo mini in ci, domin in sa maka albarka kafin in mutu.”
Fais-m’en un mets comme tu sais que je les veux, et apporte-le-moi, afin que je le mange, et que mon âme te bénisse avant que je meure.
5 Ashe, Rebeka tana ji sa’ad da Ishaku ya yi wa ɗansa Isuwa magana. Da Isuwa ya tafi jeji don yă farauto nama yă kawo,
Lorsque Rébecca eut entendu cela, et qu’Esaü fut allé dans les champs pour remplir les ordres de son père,
6 sai Rebeka ta ce wa ɗanta Yaƙub, “Ka ji nan, na ji mahaifinka ya ce wa ɗan’uwanka Isuwa,
Elle dit à son fils Jacob: J’ai ouï ton père parlant à Esaü ton frère, et lui disant:
7 ‘Kawo mini nama ka shirya mini abinci mai daɗi don in ci, in sa maka albarka a gaban Ubangiji kafin in mutu.’
Apporte-moi de ta chasse et fais un mets, afin que je mange, et que je te bénisse devant le Seigneur avant que je meure.
8 Saboda haka ɗana, ka saurara da kyau ka kuma yi abin da na faɗa maka.
Maintenant donc, mon fils, acquiesce à mon conseil,
9 Je garke ka kawo mini awaki biyu kyawawa, domin in shirya abinci mai daɗi wa mahaifinka, kamar yadda dai yake so.
Et courant au troupeau, apporte-moi deux des meilleurs chevreaux, afin que j’en fasse à ton père un de ces mets qu’il mange avec plaisir;
10 Sa’an nan ka kai wa mahaifinka yă ci, domin yă sa maka albarka kafin yă mutu.”
Et que, quand tu l’auras présenté, et qu’il en aura mangé, il te bénisse avant qu’il meure.
11 Yaƙub ya ce wa mahaifiyarsa Rebeka, “Amma ɗan’uwana Isuwa mutum ne mai gashi a jiki, ni kuma jikina sumul yake.
Celui-ci lui répondit: Vous savez qu’Esaü mon frère est un homme velu, et moi, je ne le suis pas:
12 A ce baba ya tattaɓa ni fa? Zai zama kamar ina ruɗunsa ne, wannan fa zai jawo mini la’ana a maimakon albarka.”
Si mon père me touche et me reconnaît, je crains qu’il ne pense que j’ai voulu me jouer de lui, et que je n’attire sur moi une malédiction au lieu d’une bénédiction.
13 Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, bari la’anar tă fāɗo a kaina. Kai dai yi abin da na faɗa, jeka ka kawo mini su.”
Alors sa mère: Sur moi soit, lui dit-elle, cette malédiction, ô mon fils: seulement écoute ma voix; va, et apporte ce que j’ai dit.
14 Sai ya tafi ya kamo su, ya kawo wa mahaifiyarsa, ta kuwa shirya abinci mai daɗi, yadda mahaifinsa yake so.
Il alla, l’apporta et le donna à sa mère. Celle-ci prépara un mets, comme elle savait que son père les voulait.
15 Sa’an nan Rebeka ta ɗauki riguna mafi kyau na Isuwa babban ɗanta, waɗanda take da su a gida ta sa wa ƙaramin ɗanta Yaƙub.
Puis elle le revêtit des plus précieux vêtements d’Esaü qu’elle avait auprès d’elle dans la maison;
16 Sai ta mamanne gashin awakin nan biyu a hannuwansa da bayan wuyarsa wanda ba gashi.
Et elle lui mit la peau des chevreaux autour des mains, et lui en couvrit la partie nue du cou.
17 Sa’an nan ta ba wa ɗanta Yaƙub abinci mai daɗi da kuma burodin da ta yi.
Elle lui donna ensuite le mets, et lui remit les pains qu’elle avait fait cuire.
18 Shi kuwa ya tafi wurin mahaifinsa ya ce, “Babana.” Shi kuma ya amsa “I, ɗana, wane ne?”
Les ayant apportés, il dit à Isaac: Mon père. Et celui-ci répondit: J’entends. Qui es-tu, mon fils?
19 Yaƙub ya ce wa mahaifinsa, “Ni ne Isuwa ɗan farinka. Na yi yadda ka faɗa mini. Ina roƙonka tashi ka zauna ka ci naman, domin ka sa mini albarkarka.”
Et Jacob reprit: Je suis votre premier-né Esaü: j’ai fait comme vous m’avez commandé; levez-vous, asseyez-vous et mangez de ma chasse, afin que votre âme me bénisse.
20 Ishaku ya tambayi ɗansa, “Yaya aka yi ka samo shi da sauri haka, ɗana?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Ubangiji Allahnka ne ya ba ni nasara.”
Et de nouveau Isaac à son fils: Comment, dit-il, as-tu pu en trouver si tôt, mon fils? Il répondit: La volonté de Dieu a été que ce que je cherchais, est venu soudain au-devant de moi.
21 Sai Ishaku ya ce wa Yaƙub, “Zo kusa don in taɓa ka, ɗana, domin in sani ko tabbatacce kai ne ɗana Isuwa ko babu.”
Isaac dit encore: Approche d’ici, que je te touche, mon fils, et que je reconnaisse si tu es mon fils Esaü, ou non.
22 Yaƙub kuwa ya matsa kusa da mahaifinsa Ishaku, wanda ya tattaɓa shi, sa’an nan ya ce, “Muryan nan dai, muryar Yaƙub ce, amma hannuwan, hannuwan Isuwa ne.”
Celui-ci s’approcha de son père. Or, l’ayant touché, Isaac dit: La voix est certainement la voix de Jacob; mais les mains sont les mains d’Esaü.
23 Bai gane shi ba, gama hannuwansa suna da gashi kamar na ɗan’uwansa Isuwa, saboda haka ya albarkace shi.
Et il ne le reconnut point, parce que ses mains velues reproduisaient celles de son aîné. C’est pourquoi, le bénissant,
24 Ya tambaya, “Tabbatacce kai ne ɗana Isuwa?” Ya amsa ya ce “Ni ne.”
Il dit: Toi, tu es mon fils Esaü? Il répondit: Je le suis.
25 Sa’an nan ya ce, “Ɗana, kawo mini naman da ka farauto in ci, domin in sa maka albarka.” Yaƙub ya kawo masa ya kuwa ci; ya kuma kawo masa ruwan inabi ya kuma sha.
Alors Isaac: Apporte-moi, dit-il, le mets de ta chasse, ô mon fils, afin que mon âme te bénisse. Lorsqu’il eut mangé le mets présenté, Jacob lui présenta aussi du vin; l’ayant bu,
26 Sa’an nan mahaifinsa Ishaku ya ce masa, “Zo nan, ɗana ka sumbace ni.”
Il lui dit: Approche-toi de moi, et donne-moi un baiser, mon fils.
27 Saboda haka ya je gunsa ya sumbace shi. Sa’ad da Ishaku ya ji ƙanshin rigunansa, sai ya sa masa albarka ya ce, “Aha, ƙanshin ɗana yana kama da ƙanshin jejin da Ubangiji ya sa wa albarka ne.
Il s’approcha, et il le baisa. Et dès qu’Isaac sentit la bonne odeur de ses vêtements, le bénissant, il dit: Voici que l’odeur qui s’exhale de mon fils est comme l’odeur d’un champ plein qu’a béni le Seigneur.
28 Allah yă ba ka daga raɓar sama da kuma yalwar ƙasa, yalwar hatsi da sabon ruwan inabi.
Que Dieu te donne, de la rosée du ciel et de la graisse de la terre, une abondance de blé et de vin.
29 Bari al’ummai su bauta maka mutane kuma su rusuna maka. Ka zama shugaba a kan’yan’uwanka bari kuma’ya’yan mahaifiyarka su rusuna maka. Bari waɗanda suka la’anta ka, su la’antu; waɗanda kuma suka sa maka albarka, su sami albarka.”
Et que les peuples te servent, et que les tribus se prosternent devant toi: sois le seigneur de tes frères, et que les fils de ta mère se courbent devant toi: que celui qui te maudira, soit lui-même maudit; et que celui qui te bénira, soit rempli de bénédictions.
30 Bayan Ishaku ya gama sa masa albarka, Yaƙub yana fita daga mahaifinsa ke nan, sai ga ɗan’uwansa Isuwa ya dawo daga farauta.
À peine Isaac avait achevé ces mots, et à peine Jacob était sorti dehors, qu’Esaü arriva,
31 Shi ma ya shirya abinci mai daɗi ya kawo wa mahaifinsa. Sa’an nan ya ce masa, “Babana, tashi ka zauna ka ci daga abin da na farauto, domin ka sa mini albarka.”
Et présenta à son père le mets qu’il avait apprêté de sa chasse, disant: Levez-vous, mon père, et mangez de la chasse de votre fils, afin que votre âme me bénisse.
32 Mahaifinsa Ishaku ya tambaye shi, “Wane ne kai?” Ya amsa, “Ni ne ɗanka, ɗan farinka, Isuwa.”
Et Isaac lui demanda: Qui es-tu donc? Il répondit: Je suis votre fils premier-né Esaü.
33 Ishaku ya yi makyarkyata ƙwarai ya ce, “To, wane ne wannan da ya farauto nama ya kawo mini kafin ka zo, har na ci na kuma sa masa albarka? Tabbatacce zai zama mai albarka!”
Et Isaac fut frappé d’une grande stupeur; et surpris au delà de ce que l’on peut croire, il dit: Qui est donc celui qui m’a déjà apporté ce qu’il avait pris à la chasse, et que j’ai mangé, avant que tu vinsses? Je l’ai béni, et il sera béni.
34 Sa’ad da Isuwa ya ji kalmomin mahaifinsa, sai ya fashe da kuka mai zafi kuma da ƙarfi, ya ce wa mahaifinsa, “Ka albarkace ni, ni ma, baba!”
Esaü, les paroles de son père entendues, poussa un grand cri de fureur, et consterné, il dit: Bénissez-moi aussi, mon père.
35 Amma ya ce, “Ɗan’uwanka ya zo da makirci ya karɓi albarkarka.”
Il répondit: Ton propre frère est venu frauduleusement, et il t’a enlevé ta bénédiction.
36 Isuwa ya ce, “Ba saboda haka ne aka raɗa masa suna Yaƙub ba? Ya yi mini ƙwace sau biyu ke nan; ya ƙwace mini matsayina na ɗan fari, ga shi yanzu kuma ya karɓi albarkata.” Sa’an nan ya yi tambaya, “Ba sauran albarkar da ka rage mini?”
Mais Esaü repartit: C’est justement qu’il a été appelé du nom de Jacob; car il m’a supplanté déjà une autre fois: il m’a enlevé auparavant mon droit d’aînesse, et maintenant il m’a surpris encore ma bénédiction. Et de nouveau: N’avez-vous pas, dit-il a son père, réservé aussi pour moi une bénédiction?
37 Ishaku ya amsa wa Isuwa, “Na mai da shi shugaba a kanka, na sa dukan dangoginsa su zama bayinsa, na kuma ba shi hatsi da sabon ruwan inabi. Saboda haka me kuma zan yi maka ɗana?”
Isaac répondit: Je l’ai établi ton seigneur, j’ai soumis tous ses frères à sa domination, et je l’ai enrichi de blé et de vin; mais pour toi, mon fils, après cela, que puis-je faire?
38 Isuwa ya ce wa mahaifinsa, “Iyakar albarkar da kake da ita ke nan, baba? Ka albarkace ni ni ma, baba!” Sai Isuwa ya ɗaga murya ya yi kuka.
Alors Esaü: Est-ce, lui dit-il, une seule bénédiction que vous avez, mon père? Je vous conjure de me bénir aussi. Et comme il pleurait en jetant de grands cris,
39 Mahaifinsa Ishaku ya amsa masa ya ce, “Ga shi, ni’imar ƙasar za tă nisanci mazauninka. Raɓar samaniya can ƙwanƙoli za tă nisance ka.
Isaac ému lui dit: C’est dans la graisse de la terre et dans la rosée du ciel d’en haut,
40 Za ka rayu ta wurin takobi za ka kuwa bauta wa ɗan’uwanka. Amma sa’ad da ka ɓalle, za ka kakkarye karkiyarsa daga wuyanka.”
Que sera ta bénédiction. Tu vivras sur ton glaive, mais tu serviras ton frère; et le temps viendra où tu secoueras et délieras son joug de ton cou.
41 Isuwa ya riƙe Yaƙub a zuciya saboda albarkar da mahaifinsa ya sa masa. Ya ce wa kansa, “Kwanakin mutuwar mahaifina sun yi kusa; sa’an nan zan kashe ɗan’uwana Yaƙub.”
Esaü haïssait donc toujours Jacob, pour la bénédiction dont l’avait béni son père; et il dit en son cœur: Viendront les jours du deuil de mon père, et je tuerai Jacob mon frère.
42 Sa’ad da aka faɗa wa Rebeka abin da babban ɗanta Isuwa ya faɗa, sai ta kira ɗanta Yaƙub ta ce masa, “Ɗan’uwanka Isuwa yana ta’azantar da kansa da tunanin kashe ka.
Cela fut rapporté à Rébecca, qui envoyant et appelant Jacob son fils, lui dit: Voilà qu’Esaü ton frère menace de te tuer.
43 To, fa, ɗana, yi abin da na ce; gudu nan take zuwa wurin ɗan’uwana Laban a Haran.
Maintenant donc, mon fils, écoute ma voix, lève-toi et fuis chez Laban mon frère, à Haran:
44 Zauna tare da shi na ɗan lokaci sai ɗan’uwanka ya huce.
Tu demeureras avec lui quelques jours, jusqu’à ce que s’apaise la fureur de ton frère,
45 Sa’ad da ɗan’uwanka ya daina fushi da kai, ya kuma manta da abin da ka yi masa, zan aika don ka dawo daga can. Don me zan rasa ku biyu a rana guda?”
Que cesse son indignation, et qu’il oublie ce que tu as fait contre lui; après cela j’enverrai, et je te ramènerai de là ici: pourquoi serais-je privée de mes deux fils en un seul jour?
46 Sa’an nan Rebeka ta ce wa Ishaku, “Ni fa na gaji da matan Hittiyawan nan. In Yaƙub ya auri mata daga cikin matan ƙasan nan, wato, daga matan Hittiyawa irin waɗannan, rayuwata ba za tă daɗa mini kome ba.”
Rébecca dit encore à Isaac: Je suis lasse de ma vie, à cause des filles de Heth: si Jacob prend une femme originaire de ce pays, je ne veux plus vivre.

< Farawa 27 >