< Farawa 27 >

1 Sa’ad da Ishaku ya tsufa idanunsa suka raunana har ba ya iya gani, sai ya kira Isuwa babban ɗansa ya ce masa, “Ɗana.” Isuwa kuwa ya amsa, ya ce “Ga ni.”
And it came to pass, when Isaac was old, and his eyes were too dim to see, that he called Esau his eldest son, and said unto him, My son: and he said unto him, Behold, here am I.
2 Ishaku ya ce, “Yanzu na tsufa kuma ban san ranar mutuwata ba.
And he said, Behold now, I am grown old, I know not the day of my death:
3 Saboda haka yanzu, ka ɗauki makamanka, kwari da bakanka, ka tafi jeji ka farauto mini nama.
Now therefore take, I pray thee, thy weapons, thy quiver and thy bow, and go out to the field, and hunt for me some venison;
4 Ka shirya mini irin abinci mai daɗin da nake so, ka kawo mini in ci, domin in sa maka albarka kafin in mutu.”
And make me savory food, such as I love, and bring it to me, that I may eat; that my soul may bless thee before I die.
5 Ashe, Rebeka tana ji sa’ad da Ishaku ya yi wa ɗansa Isuwa magana. Da Isuwa ya tafi jeji don yă farauto nama yă kawo,
And Rebekah heard as Isaac was speaking to Esau his son. And Esau went to the field to hunt for venison, and to bring it.
6 sai Rebeka ta ce wa ɗanta Yaƙub, “Ka ji nan, na ji mahaifinka ya ce wa ɗan’uwanka Isuwa,
And Rebekah spoke unto Jacob her son, saying, Behold, I heard thy father speak unto Esau thy brother, saying,
7 ‘Kawo mini nama ka shirya mini abinci mai daɗi don in ci, in sa maka albarka a gaban Ubangiji kafin in mutu.’
Bring me venison, and make me savory food, that I may eat and bless thee before the Lord before my death.
8 Saboda haka ɗana, ka saurara da kyau ka kuma yi abin da na faɗa maka.
And now, my son, obey my voice in that which I command thee.
9 Je garke ka kawo mini awaki biyu kyawawa, domin in shirya abinci mai daɗi wa mahaifinka, kamar yadda dai yake so.
Go, I pray thee, to the flock, and fetch me from there two good kids; and I will make them savory food for thy father, such as he loveth:
10 Sa’an nan ka kai wa mahaifinka yă ci, domin yă sa maka albarka kafin yă mutu.”
And thou shalt bring it to thy father, that he may eat; for the sake that he may bless thee before his death.
11 Yaƙub ya ce wa mahaifiyarsa Rebeka, “Amma ɗan’uwana Isuwa mutum ne mai gashi a jiki, ni kuma jikina sumul yake.
And Jacob said to Rebekah his mother, Behold, Esau my brother is a hairy man, and I am a smooth man:
12 A ce baba ya tattaɓa ni fa? Zai zama kamar ina ruɗunsa ne, wannan fa zai jawo mini la’ana a maimakon albarka.”
Peradventure my father will feel me, and I shall then seem to him as a deceiver; and I would bring upon me a curse, and not a blessing.
13 Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, bari la’anar tă fāɗo a kaina. Kai dai yi abin da na faɗa, jeka ka kawo mini su.”
And his mother said unto him, Upon me be thy curse, my son; only obey my voice, and go fetch them to me.
14 Sai ya tafi ya kamo su, ya kawo wa mahaifiyarsa, ta kuwa shirya abinci mai daɗi, yadda mahaifinsa yake so.
And he went, and fetched, and brought them to his mother: and his mother made savory food, such as his father loved.
15 Sa’an nan Rebeka ta ɗauki riguna mafi kyau na Isuwa babban ɗanta, waɗanda take da su a gida ta sa wa ƙaramin ɗanta Yaƙub.
And Rebekah took the goodly garments of her eldest son Esau, which were with her in the house, and clothed therewith Jacob her younger son;
16 Sai ta mamanne gashin awakin nan biyu a hannuwansa da bayan wuyarsa wanda ba gashi.
And the skins of the kids she put upon his hands, and upon the smooth part of his neck;
17 Sa’an nan ta ba wa ɗanta Yaƙub abinci mai daɗi da kuma burodin da ta yi.
And she gave the savory food and bread, which she had prepared, into the hand of Jacob her son.
18 Shi kuwa ya tafi wurin mahaifinsa ya ce, “Babana.” Shi kuma ya amsa “I, ɗana, wane ne?”
And he came unto his father, and said, My father: and he said, Here am I; who art thou my son?
19 Yaƙub ya ce wa mahaifinsa, “Ni ne Isuwa ɗan farinka. Na yi yadda ka faɗa mini. Ina roƙonka tashi ka zauna ka ci naman, domin ka sa mini albarkarka.”
And Jacob said unto his father, I am Esau thy first-born; I have done as thou didst speak to me: arise I pray thee, sit here and eat of my venison, that thy soul may bless me.
20 Ishaku ya tambayi ɗansa, “Yaya aka yi ka samo shi da sauri haka, ɗana?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Ubangiji Allahnka ne ya ba ni nasara.”
And Isaac said unto his son, How is it that thou hast found it so quickly, my son? And he said, Because the Lord thy God brought it before me.
21 Sai Ishaku ya ce wa Yaƙub, “Zo kusa don in taɓa ka, ɗana, domin in sani ko tabbatacce kai ne ɗana Isuwa ko babu.”
And Isaac said unto Jacob, Come near, I pray thee, that I may feel thee, my son, whether thou be truly my son Esau or not.
22 Yaƙub kuwa ya matsa kusa da mahaifinsa Ishaku, wanda ya tattaɓa shi, sa’an nan ya ce, “Muryan nan dai, muryar Yaƙub ce, amma hannuwan, hannuwan Isuwa ne.”
And Jacob went near unto Isaac his father, and he felt him; and he said, The voice is the voice of Jacob, but the hands are the hands of Esau.
23 Bai gane shi ba, gama hannuwansa suna da gashi kamar na ɗan’uwansa Isuwa, saboda haka ya albarkace shi.
And he recognized him not, because his hands were hairy, as his brother Esau's hands: so he blessed him.
24 Ya tambaya, “Tabbatacce kai ne ɗana Isuwa?” Ya amsa ya ce “Ni ne.”
And he said, Art thou indeed my son Esau? and he said I am.
25 Sa’an nan ya ce, “Ɗana, kawo mini naman da ka farauto in ci, domin in sa maka albarka.” Yaƙub ya kawo masa ya kuwa ci; ya kuma kawo masa ruwan inabi ya kuma sha.
And he said, Bring it near to me, and I will eat of my son's venison, that my soul may bless thee. And he brought it near to him, and he did eat, and he brought him wine, and he drank.
26 Sa’an nan mahaifinsa Ishaku ya ce masa, “Zo nan, ɗana ka sumbace ni.”
And Isaac his father said unto him, Come near, I pray thee, and kiss me, my son.
27 Saboda haka ya je gunsa ya sumbace shi. Sa’ad da Ishaku ya ji ƙanshin rigunansa, sai ya sa masa albarka ya ce, “Aha, ƙanshin ɗana yana kama da ƙanshin jejin da Ubangiji ya sa wa albarka ne.
And he came near, and kissed him: and he smelled the smell of his garments and blessed him, and said, See, the smell of my son is the smell of the field which the Lord hath blessed.
28 Allah yă ba ka daga raɓar sama da kuma yalwar ƙasa, yalwar hatsi da sabon ruwan inabi.
And may God give thee of the dew of heaven, and the fatness of the earth, and plenty of corn and wine;
29 Bari al’ummai su bauta maka mutane kuma su rusuna maka. Ka zama shugaba a kan’yan’uwanka bari kuma’ya’yan mahaifiyarka su rusuna maka. Bari waɗanda suka la’anta ka, su la’antu; waɗanda kuma suka sa maka albarka, su sami albarka.”
Nations shall serve thee, and people bow down to thee; be lord over thy brethren, and thy mother's sons shall bow down to thee; cursed be they that curse thee, and blessed be they that bless thee.
30 Bayan Ishaku ya gama sa masa albarka, Yaƙub yana fita daga mahaifinsa ke nan, sai ga ɗan’uwansa Isuwa ya dawo daga farauta.
And it came to pass, as soon as Isaac had made an end of blessing Jacob, and Jacob was yet scarcely gone out from the presence of his father, that Esau his brother came in from his hunting.
31 Shi ma ya shirya abinci mai daɗi ya kawo wa mahaifinsa. Sa’an nan ya ce masa, “Babana, tashi ka zauna ka ci daga abin da na farauto, domin ka sa mini albarka.”
And he also made savory food, and brought it unto his father, and said unto his father, Let my father arise, and eat of his son's venison, in order that thy soul may bless me.
32 Mahaifinsa Ishaku ya tambaye shi, “Wane ne kai?” Ya amsa, “Ni ne ɗanka, ɗan farinka, Isuwa.”
And Isaac his father said unto him, Who art thou? And he said, I am thy son, thy first-born, Esau.
33 Ishaku ya yi makyarkyata ƙwarai ya ce, “To, wane ne wannan da ya farauto nama ya kawo mini kafin ka zo, har na ci na kuma sa masa albarka? Tabbatacce zai zama mai albarka!”
And Isaac trembled greatly, exceedingly, and said, Who was it? where is he that had hunted venison, and brought it me, and I ate of all before thou camest, and blessed him? yea, he shall also remain blessed.
34 Sa’ad da Isuwa ya ji kalmomin mahaifinsa, sai ya fashe da kuka mai zafi kuma da ƙarfi, ya ce wa mahaifinsa, “Ka albarkace ni, ni ma, baba!”
When Esau heard the words of his father, he uttered a great and exceedingly bitter cry, and said unto his father, Bless me, also me, my father.
35 Amma ya ce, “Ɗan’uwanka ya zo da makirci ya karɓi albarkarka.”
And he said, Thy brother came with subtilty, and took away thy blessing.
36 Isuwa ya ce, “Ba saboda haka ne aka raɗa masa suna Yaƙub ba? Ya yi mini ƙwace sau biyu ke nan; ya ƙwace mini matsayina na ɗan fari, ga shi yanzu kuma ya karɓi albarkata.” Sa’an nan ya yi tambaya, “Ba sauran albarkar da ka rage mini?”
And he said, Hath he been therefore named Jacob, because he hath supplanted me these two times? my right of first-born he took away; and, behold, now he hath taken away my blessing: and he said, Hast thou not reserved a blessing for me.
37 Ishaku ya amsa wa Isuwa, “Na mai da shi shugaba a kanka, na sa dukan dangoginsa su zama bayinsa, na kuma ba shi hatsi da sabon ruwan inabi. Saboda haka me kuma zan yi maka ɗana?”
And Isaac answered and said unto Esau, Behold, I have made him thy lord, and all his brethren have I given to him for servants; and with corn and wine have I endowed him: and what can I do now for thee, my son.
38 Isuwa ya ce wa mahaifinsa, “Iyakar albarkar da kake da ita ke nan, baba? Ka albarkace ni ni ma, baba!” Sai Isuwa ya ɗaga murya ya yi kuka.
And Esau said unto his father, Hast thou then but one blessing, my father? bless me, also me, my father. And Esau lifted up his voice, and wept.
39 Mahaifinsa Ishaku ya amsa masa ya ce, “Ga shi, ni’imar ƙasar za tă nisanci mazauninka. Raɓar samaniya can ƙwanƙoli za tă nisance ka.
And Isaac his father answered and said unto him, Behold, thy dwelling shall be the fatness of the earth, and [blessed] by the dew of heaven from above;
40 Za ka rayu ta wurin takobi za ka kuwa bauta wa ɗan’uwanka. Amma sa’ad da ka ɓalle, za ka kakkarye karkiyarsa daga wuyanka.”
And by thy sword shalt thou live, and thy brother shalt thou serve; and it shall come to pass, that when thou shalt have the dominion, thou canst break his yoke from off thy neck.
41 Isuwa ya riƙe Yaƙub a zuciya saboda albarkar da mahaifinsa ya sa masa. Ya ce wa kansa, “Kwanakin mutuwar mahaifina sun yi kusa; sa’an nan zan kashe ɗan’uwana Yaƙub.”
And Esau hated Jacob because of the blessing wherewith his father had blessed him; and Esau said in his heart, The days of mourning for my father will be at hand; then will I slay my brother Jacob.
42 Sa’ad da aka faɗa wa Rebeka abin da babban ɗanta Isuwa ya faɗa, sai ta kira ɗanta Yaƙub ta ce masa, “Ɗan’uwanka Isuwa yana ta’azantar da kansa da tunanin kashe ka.
And Rebekah was informed of the words of Esau her elder son: and she sent and called Jacob her younger son, and said unto him, Behold, thy brother Esau doth comfort himself, with regard to thee, purposing to kill thee.
43 To, fa, ɗana, yi abin da na ce; gudu nan take zuwa wurin ɗan’uwana Laban a Haran.
Now therefore, my son, obey my voice; and arise, flee thou to Laban my brother, to Charan;
44 Zauna tare da shi na ɗan lokaci sai ɗan’uwanka ya huce.
And tarry with him a short time, until thy brother's fury turn away;
45 Sa’ad da ɗan’uwanka ya daina fushi da kai, ya kuma manta da abin da ka yi masa, zan aika don ka dawo daga can. Don me zan rasa ku biyu a rana guda?”
Until thy brother's anger turn away from thee, and he forget that which thou hast done to him: then will I send, and fetch thee from there; why should I be deprived of both of you at once in one day?
46 Sa’an nan Rebeka ta ce wa Ishaku, “Ni fa na gaji da matan Hittiyawan nan. In Yaƙub ya auri mata daga cikin matan ƙasan nan, wato, daga matan Hittiyawa irin waɗannan, rayuwata ba za tă daɗa mini kome ba.”
And Rebekah said to Isaac, I am weary of my life because of the daughters of Heth; if Jacob take a wife from the daughters of Heth, such as these, from the daughters of the land, what good will life do me?

< Farawa 27 >