< Farawa 26 >
1 Aka yi yunwa a ƙasar; ban da yunwar da aka yi da fari a zamanin Ibrahim, sai Ishaku ya tafi wurin Abimelek sarkin Filistiyawa a Gerar.
Bila je lakota v deželi, poleg prve lakote, ki je bila v Abrahamovih dneh. In Izak je odšel k filistejskemu kralju Abimélehu v Gerár.
2 Ubangiji kuwa ya bayyana ga Ishaku ya ce, “Kada ka gangara zuwa Masar; ka yi zauna a ƙasar da zan faɗa maka.
Prikazal se mu je Gospod ter rekel: »Ne hodi dol v Egipt; prebivaj v deželi, ki ti bom o njej povedal.
3 Ka zauna a wannan ƙasa na ɗan lokaci, zan kuwa kasance tare da kai, zan kuma albarkace ka. Gama zan ba da waɗannan ƙasashe gare ka da kuma zuriyarka. Zan kuma cika rantsuwar da na yi wa mahaifinka Ibrahim.
Začasno bivaj v tej deželi in jaz bom s teboj in te bom blagoslavljal, kajti tebi in tvojemu potomcu bom dal vse te dežele in jaz bom izpolnil prisego, ki sem jo prisegel tvojemu očetu Abrahamu;
4 Zan sa zuriyarka ta yi yawa kamar taurari a sararin sama zan kuwa ba su dukan waɗannan ƙasashe, ta wurin’ya’yanka kuma za a albarkaci dukan al’umman duniya,
in tvojemu semenu bom storil, da se pomnoži kakor zvezde neba in tvojemu semenu bom dal vse te dežele in v tvojem semenu bodo blagoslovljeni narodi zemlje,
5 domin Ibrahim ya yi mini biyayya ya kuma kiyaye umarnaina, ƙa’idodina da kuma dokokina.”
zato ker je Abraham ubogal moj glas in ohranil moj ukaz, moje zapovedi, moje zakone in moje postave.«
6 Sai Ishaku ya zauna a Gerar.
In Izak je prebival v Gerárju.
7 Sa’ad da mutanen wurin suka tambaye shi game da matarsa, sai ya ce, “’Yar’uwata ce,” gama yana tsoro yă ce, “Ita matata ce.” Ya yi tunani, “Mutane wannan wuri za su kashe ni ta dalili Rebeka, domin kyakkyawa ce.”
Možje [tega] kraja so ga vprašali o njegovi ženi in rekel je: »Ona je moja sestra, « kajti bal se je reči: » Ona je moja žena.« Rekel je, »da me ne bi možje [tega] kraja ubili zaradi Rebeke, « kajti bila je zelo lepa na pogled.
8 Sa’ad da Ishaku ya daɗe a can, sai Abimelek sarkin Filistiyawa ya duba daga taga ya ga Ishaku yana rungumar matarsa Rebeka.
Pripetilo se je, ko je bil tam dolgo časa, da je Abiméleh, kralj Filistejcev, pogledal skozi okno in zagledal in glej, Izak se je ljubimkal s svojo ženo Rebeko.
9 Saboda haka Abimelek ya aika Ishaku yă je, sa’an nan ya ce, “Tabbatacce ita matarka ce! Me ya sa ka ce, ‘Ita’yar’uwata ce?’” Ishaku ya amsa masa ya ce, “Don na yi tsammani zan rasa raina saboda ita.”
Abiméleh je poklical Izaka ter rekel: »Glej, ona je zagotovo tvoja žena. Kako si rekel: ›Ona je moja sestra?‹« Izak mu je odgovoril: »Ker sem rekel: ›Da zaradi nje ne bi umrl.‹«
10 Sa’an nan Abimelek ya ce, “Me ke nan ka yi mana? Da a ce wani daga mazanmu ya kwana da matarka, ai, da ka jawo laifi a kanmu.”
Abiméleh je rekel: »Kaj je to, kar si nam storil? Nekdo izmed ljudstva bi lahko mirno ležal s tvojo ženo in ti bi nad nas privedel krivdo.«
11 Saboda haka Abimelek ya yi umarni ga dukan mutane. “Duk wanda ya fitine wannan mutum ko matarsa, tabbatacce za a kashe shi.”
Abiméleh je vsem svojim ljudem naročil, rekoč: »Kdor se dotakne tega moža ali njegove žene, bo zagotovo usmrčen.«
12 Ishaku ya shuka hatsi a wannan ƙasa, a shekaran nan ya yi girbi ninki ɗari, domin Ubangiji ya albarkace shi.
Potem je Izak sejal v tej deželi in v istem letu prejel stokratno in Gospod ga je blagoslovil.
13 Mutumin ya arzuta, arzikinsa ya yi ta haɓaka har ya zama attajiri.
Mož je postal velik in šel naprej in rasel, dokler ni postal zelo velik,
14 Ya kasance da garkunan tumaki da na shanu da bayi masu yawa, har Filistiyawa suka yi ƙyashinsa.
kajti imel je posest tropov in posest čred in veliko število služabnikov, in Filistejci so mu zavidali.
15 Saboda haka dukan rijiyoyin da bayin mahaifinsa suka haƙa a kwanakin da mahaifinsa Ibrahim yake da rai, Filistiyawa sun toshe su, suka kuma ciccike su da ƙasa.
Kajti vse vodnjake, ki so jih služabniki njegovega očeta izkopali v dneh njegovega očeta Abrahama, so Filistejci zamašili in jih napolnili s prstjo.
16 Sai Abimelek ya ce wa Ishaku, “Fita daga cikinmu; ka fi ƙarfinmu.”
Abiméleh je rekel Izaku: »Pojdi od nas, kajti mnogo mogočnejši si kakor mi.«
17 Saboda haka Ishaku ya fita daga can, ya yi sansani a Kwarin Gerar, ya kuma zauna a can.
Izak se je odpravil od tam in svoj šotor postavil v dolini Gerár ter tam prebival.
18 Ishaku ya sāke tona rijiyoyi waɗanda dā aka haƙa a zamanin Ibrahim mahaifinsa, gama Filistiyawa suka tattoshe bayan mutuwar Ibrahim, ya kuma sa musu sunayen da mahaifinsa ya ba su.
Izak je ponovno izkopal vodnjake, ki so jih izkopali v dneh njegovega očeta Abrahama, kajti Filistejci so jih po Abrahamovi smrti zamašili. Njihova imena je poimenoval po imenih, po katerih jih je imenoval njegov oče.
19 Barorin Ishaku suka haƙa cikin kwarin suka kuwa sami rijiya mai ruwa mai kyau a can.
Izakovi služabniki so kopáli v dolini in tam našli vodnjak izvirne vode.
20 Amma makiyayan Gerar suka yi faɗa da na Ishaku suka ce, “Ruwan namu ne!” Saboda haka Ishaku ya ba wa rijiyar suna Esek, domin sun yi faɗa da shi.
Čredniki iz Gerárja pa so se prepirali z Izakovimi čredniki, rekoč: »Voda je naša.« In ime vodnjaka je poimenoval Esek, ker so se z njim prepirali.
21 Sai suka haƙa wata rijiya, amma suka yi faɗa a kanta ita ma, saboda haka ya ce da ita Sitna.
In izkopali so še en vodnjak in tudi za tega so se prepirali. Njegovo ime je poimenoval Sitna.
22 Sai Ishaku ya matsa daga can ya sāke haƙa wata rijiyar, babu wani kuma da yi faɗa a kanta. Sai ya ba ta suna Rehobot, yana cewa, “Yanzu Ubangiji ya ba mu wuri, za mu kuwa yi ta haihuwa a ƙasar.”
Odstranil se je od tam ter izkopal nov vodnjak. Zanj pa se niso prepirali in njegovo ime je imenoval Rehobót in rekel je: »Kajti sedaj je Gospod za nas pripravil prostor in bomo rodovitni v deželi.«
23 Daga can ya haura zuwa Beyersheba.
In od tam se je dvignil v Beeršébo.
24 A wannan dare Ubangiji ya bayyana gare shi ya ce, “Ni ne Allah na mahaifinka Ibrahim. Kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai, zan albarkace ka, zan kuma ƙara yawan zuriyarka saboda bawana Ibrahim.”
Isto noč se mu je prikazal Gospod ter rekel: »Jaz sem Bog Abrahama, tvojega očeta. Ne boj se, kajti jaz sem s teboj in zaradi svojega služabnika Abrahama te bom blagoslovil in pomnožil tvoje seme.«
25 Sai Ishaku ya gina bagade a can, ya kuma kira bisa sunan Ubangiji. A can ya kafa tentinsa, a can kuma bayinsa suka haƙa wata rijiya.
Tam je zgradil oltar in klical h Gospodovemu imenu ter tam postavil svoj šotor in tam so Izakovi služabniki izkopali vodnjak.
26 Ana cikin haka, sai Abimelek ya zo wurinsa daga Gerar, tare da Ahuzzat mai ba shi shawara da Fikol shugaban mayaƙansa.
Potem so iz Gerárja odšli k njemu Abiméleh in Ahuzát, eden izmed njegovih prijateljev ter Pihól, vrhovni poveljnik njegove vojske.
27 Ishaku ya tambaye su, “Me ya kawo ku gare ni, da yake kun yi gāba da ni, kuka kuma kore ni?”
Izak pa jim je rekel: »Zakaj ste prišli k meni, glede na to, da me sovražite in ste me odposlali od sebe?«
28 Suka amsa, “Mun ga a zahiri cewa Ubangiji yana tare da kai; saboda haka muka ce, ‘Dole rantsuwa ta kasance tsakaninmu da kai.’ Bari mu yi yarjejjeniya da kai
Rekli so: »Zagotovo smo videli, da je bil s teboj Gospod in smo rekli: ›Naj bo torej prisega med nami, torej med nami in teboj in naj sklenemo zavezo s teboj,
29 cewa ba za ka cuce mu ba, kamar yadda ba mu fitine ka ba, amma muka yi maka kirki, muka kuma sallame ka cikin salama. Yanzu kuwa kai albarkatacce ne na Ubangiji.”
da nam ne boš storil nobene škode, kakor se mi nismo dotaknili tebe in kakor ti nismo storili nič drugega, temveč dobro in smo te odposlali v miru.‹ Ti si torej blagoslovljen od Gospoda.«
30 Sai Ishaku ya shirya musu liyafa, suka ci suka kuma sha.
In pripravil jim je gostijo in jedli so ter pili.
31 Kashegari da sassafe sai mutanen suka yi wa juna rantsuwa. Sa’an nan Ishaku ya sallame su, suka kuwa tafi cikin salama.
Zjutraj pa so zgodaj vstali in drug drugemu prisegli in Izak jih je odposlal proč in od njega so odšli v miru.
32 A wannan rana bayin Ishaku suka zo suka faɗa masa game da rijiyar da suka haƙa. Suka ce, “Mun sami ruwa!”
Istega dne se je pripetilo, da so prišli Izakovi služabniki in mu povedali glede vodnjaka, ki so ga izkopali ter mu rekel: »Našli smo vodo.«
33 Sai ya kira ta Shiba, don haka har wa yau ana kira garin Beyersheba.
In imenoval ga je Šiba; zato je ime mesta Beeršéba do današnjega dne.
34 Sa’ad da Yaƙub ya kai shekaru arba’in da haihuwa, sai ya auri Yudit’yar Beyeri mutumin Hitti, da kuma Basemat’yar Elon mutumin Hitti.
Ezav je bil star štirideset let, ko je vzel Judito, hčer Hetejca Beeríja in Basemáto, hči Hetejca Elóna,
35 Su ne suka zama sanadin baƙin ciki ga Ishaku da Rebeka.
ki sta bili Izaku in Rebeki v žalostno mišljenje.