< Farawa 26 >

1 Aka yi yunwa a ƙasar; ban da yunwar da aka yi da fari a zamanin Ibrahim, sai Ishaku ya tafi wurin Abimelek sarkin Filistiyawa a Gerar.
Cependant une famine étant survenue dans ce pays, après la disette qui était arrivée dans les jours d’Abraham, Isaac s’en alla vers Abimélech, roi des Philistins, à Gérara.
2 Ubangiji kuwa ya bayyana ga Ishaku ya ce, “Kada ka gangara zuwa Masar; ka yi zauna a ƙasar da zan faɗa maka.
Or le Seigneur lui apparut, et dit: Ne descends pas en Égypte, mais demeure dans le pays que je te dirai.
3 Ka zauna a wannan ƙasa na ɗan lokaci, zan kuwa kasance tare da kai, zan kuma albarkace ka. Gama zan ba da waɗannan ƙasashe gare ka da kuma zuriyarka. Zan kuma cika rantsuwar da na yi wa mahaifinka Ibrahim.
Restes-y comme étranger, et je serai avec toi, et je te bénirai; car c’est à toi et à ta postérité que je donnerai toutes ces contrées, accomplissant le serment que j’ai fait à Abraham ton père.
4 Zan sa zuriyarka ta yi yawa kamar taurari a sararin sama zan kuwa ba su dukan waɗannan ƙasashe, ta wurin’ya’yanka kuma za a albarkaci dukan al’umman duniya,
Et je multiplierai ta postérité comme les étoiles du ciel; et je donnerai à tes descendants toutes ces contrées, et seront bénies en ta postérité toutes les nations de la terre;
5 domin Ibrahim ya yi mini biyayya ya kuma kiyaye umarnaina, ƙa’idodina da kuma dokokina.”
Parce qu’Abraham a obéi à ma voix, qu’il a gardé mes préceptes et mes commandements, et qu’il a observé les cérémonies et les lois.
6 Sai Ishaku ya zauna a Gerar.
Isaac donc demeura à Gérara.
7 Sa’ad da mutanen wurin suka tambaye shi game da matarsa, sai ya ce, “’Yar’uwata ce,” gama yana tsoro yă ce, “Ita matata ce.” Ya yi tunani, “Mutane wannan wuri za su kashe ni ta dalili Rebeka, domin kyakkyawa ce.”
Comme il était interrogé par les hommes de ce lieu sur sa femme, il répondit: C’est ma sœur; car il avait craint d’avouer qu’elle lui était unie par le mariage, pensant que peut-être ils le tueraient à cause de sa beauté.
8 Sa’ad da Ishaku ya daɗe a can, sai Abimelek sarkin Filistiyawa ya duba daga taga ya ga Ishaku yana rungumar matarsa Rebeka.
Or, lorsque beaucoup de jours furent passés, et qu’il demeurait encore en ce même endroit, Abimélech, roi des Philistins, regardant par la fenêtre, le vit jouant avec Rébecca, sa femme.
9 Saboda haka Abimelek ya aika Ishaku yă je, sa’an nan ya ce, “Tabbatacce ita matarka ce! Me ya sa ka ce, ‘Ita’yar’uwata ce?’” Ishaku ya amsa masa ya ce, “Don na yi tsammani zan rasa raina saboda ita.”
Et l’ayant fait venir, il dit: Il est évident que c’est ta femme; pourquoi as-tu menti, disant que c’est ta sœur? Il répondit: J’ai eu peur de mourir à cause d’elle.
10 Sa’an nan Abimelek ya ce, “Me ke nan ka yi mana? Da a ce wani daga mazanmu ya kwana da matarka, ai, da ka jawo laifi a kanmu.”
Et Abimélech reprit: Pourquoi nous en as-tu imposé? quelqu’un du peuple aurait pu abuser de ta femme, et tu aurais attiré sur nous un grand péché. Et il commanda à tout le peuple, disant:
11 Saboda haka Abimelek ya yi umarni ga dukan mutane. “Duk wanda ya fitine wannan mutum ko matarsa, tabbatacce za a kashe shi.”
Quiconque touchera la femme de cet homme, mourra de mort.
12 Ishaku ya shuka hatsi a wannan ƙasa, a shekaran nan ya yi girbi ninki ɗari, domin Ubangiji ya albarkace shi.
Et Isaac sema en ce pays, et il trouva dans l’année même le centuple; car le Seigneur le bénit.
13 Mutumin ya arzuta, arzikinsa ya yi ta haɓaka har ya zama attajiri.
Ainsi cet homme, s’enrichit, et il allait prospérant et s’accroissant, jusqu’à ce qu’il devint extrêmement puissant.
14 Ya kasance da garkunan tumaki da na shanu da bayi masu yawa, har Filistiyawa suka yi ƙyashinsa.
Il eut aussi des possessions de brebis et de gros troupeaux, et une nombreuse famille. A cause de cela, les Philistins jaloux de lui,
15 Saboda haka dukan rijiyoyin da bayin mahaifinsa suka haƙa a kwanakin da mahaifinsa Ibrahim yake da rai, Filistiyawa sun toshe su, suka kuma ciccike su da ƙasa.
Comblèrent en ce temps-là tous les puits qu’avaient creusés les serviteurs de son père Abraham, les remplissant de terre;
16 Sai Abimelek ya ce wa Ishaku, “Fita daga cikinmu; ka fi ƙarfinmu.”
Tellement qu’Abimélech dit à Isaac: Eloigne-toi de nous, parce que tu es devenu beaucoup plus puissant que nous.
17 Saboda haka Ishaku ya fita daga can, ya yi sansani a Kwarin Gerar, ya kuma zauna a can.
Et lui descendant, vint au torrent de Gérara pour y habiter.
18 Ishaku ya sāke tona rijiyoyi waɗanda dā aka haƙa a zamanin Ibrahim mahaifinsa, gama Filistiyawa suka tattoshe bayan mutuwar Ibrahim, ya kuma sa musu sunayen da mahaifinsa ya ba su.
Il creusa de nouveau les autres puits qu’avaient creusés les serviteurs de son père Abraham, et que, celui-ci mort, les Philistins avaient anciennement comblés; et il les appela des mêmes noms dont auparavant son père les avait nommés.
19 Barorin Ishaku suka haƙa cikin kwarin suka kuwa sami rijiya mai ruwa mai kyau a can.
Ils creusèrent aussi dans le torrent, et ils trouvèrent de l’eau vive.
20 Amma makiyayan Gerar suka yi faɗa da na Ishaku suka ce, “Ruwan namu ne!” Saboda haka Ishaku ya ba wa rijiyar suna Esek, domin sun yi faɗa da shi.
Mais là aussi les pasteurs de Gérara firent une querelle aux pasteurs d’Isaac, disant: L’eau est à nous; c’est pourquoi, il donna à ce puits, à cause de ce qui était arrivé, le nom de Calomnie.
21 Sai suka haƙa wata rijiya, amma suka yi faɗa a kanta ita ma, saboda haka ya ce da ita Sitna.
Or ils creusèrent un autre puits: et pour celui-là aussi ils se querellèrent, et il l’appela Inimitiés.
22 Sai Ishaku ya matsa daga can ya sāke haƙa wata rijiyar, babu wani kuma da yi faɗa a kanta. Sai ya ba ta suna Rehobot, yana cewa, “Yanzu Ubangiji ya ba mu wuri, za mu kuwa yi ta haihuwa a ƙasar.”
Parti de là, il creusa un autre puits, pour lequel ils ne se disputèrent point, et il l’appela du nom d’Etendue, disant: Maintenant le Seigneur nous a donné de l’étendue et nous a fait croître sur la terre,
23 Daga can ya haura zuwa Beyersheba.
Puis il monta de ce lieu à Bersabée,
24 A wannan dare Ubangiji ya bayyana gare shi ya ce, “Ni ne Allah na mahaifinka Ibrahim. Kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai, zan albarkace ka, zan kuma ƙara yawan zuriyarka saboda bawana Ibrahim.”
Où lui apparut le Seigneur cette nuit-là même, disant: Je suis le Dieu d’Abraham ton père; ne crains pas, parce que je suis avec toi: je te bénirai, et je multiplierai ta postérité à cause de mon serviteur Abraham.
25 Sai Ishaku ya gina bagade a can, ya kuma kira bisa sunan Ubangiji. A can ya kafa tentinsa, a can kuma bayinsa suka haƙa wata rijiya.
C’est pourquoi il bâtit là un autel: puis, le nom du Seigneur invoqué, il dressa sa tente, et ordonna à ses serviteurs de creuser un puits.
26 Ana cikin haka, sai Abimelek ya zo wurinsa daga Gerar, tare da Ahuzzat mai ba shi shawara da Fikol shugaban mayaƙansa.
Comme en ce lieu vinrent de Gérara, Abimélech, Ochozath son ami, et Phicol chef de ses soldats.
27 Ishaku ya tambaye su, “Me ya kawo ku gare ni, da yake kun yi gāba da ni, kuka kuma kore ni?”
Isaac leur demanda: Pourquoi venez-vous vers moi, homme que vous haïssez, et que vous avez chassé d’auprès de vous?
28 Suka amsa, “Mun ga a zahiri cewa Ubangiji yana tare da kai; saboda haka muka ce, ‘Dole rantsuwa ta kasance tsakaninmu da kai.’ Bari mu yi yarjejjeniya da kai
Ils répondirent: Nous avons vu qu’avec toi était le Seigneur, et c’est pourquoi nous avons dit: Qu’il y ait serment entre nous, et faisons alliance,
29 cewa ba za ka cuce mu ba, kamar yadda ba mu fitine ka ba, amma muka yi maka kirki, muka kuma sallame ka cikin salama. Yanzu kuwa kai albarkatacce ne na Ubangiji.”
Afin que tu ne nous fasses aucun mal, comme nous-mêmes, nous n’avons touché à rien de ce qui est à toi, et nous n’avons rien fait qui t’offensât; mais nous t’avons renvoyé en paix, comblé de la bénédiction du Seigneur.
30 Sai Ishaku ya shirya musu liyafa, suka ci suka kuma sha.
Isaac donc leur fit un festin: et après qu’ils eurent mangé et bu,
31 Kashegari da sassafe sai mutanen suka yi wa juna rantsuwa. Sa’an nan Ishaku ya sallame su, suka kuwa tafi cikin salama.
Se levant le matin, ils firent serment de part et d’autre; ensuite Isaac les envoya paisiblement chez eux.
32 A wannan rana bayin Ishaku suka zo suka faɗa masa game da rijiyar da suka haƙa. Suka ce, “Mun sami ruwa!”
Mais voilà que vinrent en ce jour-là même les serviteurs d’Isaac, lui apportant des nouvelles du puits qu’ils avaient creusé, et disant: Nous avons trouvé de l’eau.
33 Sai ya kira ta Shiba, don haka har wa yau ana kira garin Beyersheba.
D’où il l’appela Abondance: et à la ville on a imposé le nom de Bersabée jusqu’au présent jour.
34 Sa’ad da Yaƙub ya kai shekaru arba’in da haihuwa, sai ya auri Yudit’yar Beyeri mutumin Hitti, da kuma Basemat’yar Elon mutumin Hitti.
Quant à Esaü, quadragénaire, il prit pour femmes Judith, fille de Béeri l’Hétéen, et Basemath, fille d’Elon, du même lieu;
35 Su ne suka zama sanadin baƙin ciki ga Ishaku da Rebeka.
Qui toutes deux avaient irrité l’esprit d’Isaac et de Rébecca.

< Farawa 26 >