< Farawa 26 >

1 Aka yi yunwa a ƙasar; ban da yunwar da aka yi da fari a zamanin Ibrahim, sai Ishaku ya tafi wurin Abimelek sarkin Filistiyawa a Gerar.
And there fell a derth in ye lande passinge the first derth yt fell in the dayes of Abraham. Wherfore Isaac went vnto Abimelech kinge of ye Philistias vnto Gerar.
2 Ubangiji kuwa ya bayyana ga Ishaku ya ce, “Kada ka gangara zuwa Masar; ka yi zauna a ƙasar da zan faɗa maka.
The the LORde apeared vnto him and sayde goo not doune in to Egipte but byde in ye land which I saye vnto ye:
3 Ka zauna a wannan ƙasa na ɗan lokaci, zan kuwa kasance tare da kai, zan kuma albarkace ka. Gama zan ba da waɗannan ƙasashe gare ka da kuma zuriyarka. Zan kuma cika rantsuwar da na yi wa mahaifinka Ibrahim.
Sogeorne in this lade and I wyll be with ye and wyll blesse ye: for vnto the and vnto thy sede I will geue all these cotreis And I will performe the oothe which I swore vnto Abraha thy father
4 Zan sa zuriyarka ta yi yawa kamar taurari a sararin sama zan kuwa ba su dukan waɗannan ƙasashe, ta wurin’ya’yanka kuma za a albarkaci dukan al’umman duniya,
and will multiplye thy seed as ye starres of heave and will geue vnto thy seed all these contreis. And thorow thy seed shall all the natios of the erth be blessed
5 domin Ibrahim ya yi mini biyayya ya kuma kiyaye umarnaina, ƙa’idodina da kuma dokokina.”
because yt Abraha harkened vnto mi voyce and kepte mine ordinauces comaudmetes statutes and lawes
6 Sai Ishaku ya zauna a Gerar.
And Isaac dwelled in Gerar.
7 Sa’ad da mutanen wurin suka tambaye shi game da matarsa, sai ya ce, “’Yar’uwata ce,” gama yana tsoro yă ce, “Ita matata ce.” Ya yi tunani, “Mutane wannan wuri za su kashe ni ta dalili Rebeka, domin kyakkyawa ce.”
And yt me of the place asked hi of his wife and he sayde yt she was his sister: for he feared to calle her his wife lest the me of the place shulde haue kylled hym for hir sake because she was bewtyfull to ye eye.
8 Sa’ad da Ishaku ya daɗe a can, sai Abimelek sarkin Filistiyawa ya duba daga taga ya ga Ishaku yana rungumar matarsa Rebeka.
And it happened after he had bene there longe tyme yt Abimelech kinge of ye Philistias loked out at a wyndow and sawe Isaac sportinge with Rebecca his wife.
9 Saboda haka Abimelek ya aika Ishaku yă je, sa’an nan ya ce, “Tabbatacce ita matarka ce! Me ya sa ka ce, ‘Ita’yar’uwata ce?’” Ishaku ya amsa masa ya ce, “Don na yi tsammani zan rasa raina saboda ita.”
And Abimelech sende for Isaac and sayde: se she is of a suertie thi wife and why saydest thou yt she was thi sister? And Isaac saide vnto hi: I thoughte yt I mighte peradventure haue dyed for hir sake.
10 Sa’an nan Abimelek ya ce, “Me ke nan ka yi mana? Da a ce wani daga mazanmu ya kwana da matarka, ai, da ka jawo laifi a kanmu.”
The fayde Abimelech: whi hast thou done this vnto vs? one of ye people myght lightely haue lyne by thy wife and so shuldest thou haue broughte synne vpon vs
11 Saboda haka Abimelek ya yi umarni ga dukan mutane. “Duk wanda ya fitine wannan mutum ko matarsa, tabbatacce za a kashe shi.”
Tha Abimelech charged all his people saynge: he yt toucheth this man or his wife shall surely dye for it.
12 Ishaku ya shuka hatsi a wannan ƙasa, a shekaran nan ya yi girbi ninki ɗari, domin Ubangiji ya albarkace shi.
And Isaac sowed in yt lade and founde in ye same yere an hudred bushels: for ye LORde blessed hi
13 Mutumin ya arzuta, arzikinsa ya yi ta haɓaka har ya zama attajiri.
and the man waxed mightye and wet forth and grewe till he was exceadinge great
14 Ya kasance da garkunan tumaki da na shanu da bayi masu yawa, har Filistiyawa suka yi ƙyashinsa.
yt he had possessio of shepe of oxe and a myghtie housholde: so yt the Philestians had envy at him:
15 Saboda haka dukan rijiyoyin da bayin mahaifinsa suka haƙa a kwanakin da mahaifinsa Ibrahim yake da rai, Filistiyawa sun toshe su, suka kuma ciccike su da ƙasa.
In so moch yt they stopped and fylled vp with erth all the welles which his fathers servauntes dygged in his father Abrahams tyme.
16 Sai Abimelek ya ce wa Ishaku, “Fita daga cikinmu; ka fi ƙarfinmu.”
Than sayde Abimelech vnto Isaac: gett the fro me for thou art myhhtier then we a greate deale.
17 Saboda haka Ishaku ya fita daga can, ya yi sansani a Kwarin Gerar, ya kuma zauna a can.
Than Isaac departed thense and pitched his tente in the valey Gerar and dwelt there,
18 Ishaku ya sāke tona rijiyoyi waɗanda dā aka haƙa a zamanin Ibrahim mahaifinsa, gama Filistiyawa suka tattoshe bayan mutuwar Ibrahim, ya kuma sa musu sunayen da mahaifinsa ya ba su.
And Isaac digged agayne the welles of water which they dygged in the dayes of Abraha his father which the Philestias had stoppe after ye deth of Abraha and gaue the the same names which hys father gaue the.
19 Barorin Ishaku suka haƙa cikin kwarin suka kuwa sami rijiya mai ruwa mai kyau a can.
As Isaacs seruautes dygged in the valey they founde a well of springynge water.
20 Amma makiyayan Gerar suka yi faɗa da na Ishaku suka ce, “Ruwan namu ne!” Saboda haka Ishaku ya ba wa rijiyar suna Esek, domin sun yi faɗa da shi.
And the herdme of Gerar dyd stryue with Isaacs herdme saynge: the water is oures Than called he the well Eseck because they stroue with hym.
21 Sai suka haƙa wata rijiya, amma suka yi faɗa a kanta ita ma, saboda haka ya ce da ita Sitna.
Than dygged they another well and they stroue for yt also. Therfore called he it Sitena.
22 Sai Ishaku ya matsa daga can ya sāke haƙa wata rijiyar, babu wani kuma da yi faɗa a kanta. Sai ya ba ta suna Rehobot, yana cewa, “Yanzu Ubangiji ya ba mu wuri, za mu kuwa yi ta haihuwa a ƙasar.”
And than he departed these and dygged a nother well for the which they stroue not: therfore called he it Rehoboth saige: ye LORde hath now made vs rowme and we are encreased vpo the erth.
23 Daga can ya haura zuwa Beyersheba.
Afterward departed he thece and came to Berseba
24 A wannan dare Ubangiji ya bayyana gare shi ya ce, “Ni ne Allah na mahaifinka Ibrahim. Kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai, zan albarkace ka, zan kuma ƙara yawan zuriyarka saboda bawana Ibrahim.”
And the LORde apered vnto hi the same nyghte and sayde. I am the God of Abraha thy father feare not for I am with the and will blesse the and multiplye thy sede for my seruaute Abrahams sake.
25 Sai Ishaku ya gina bagade a can, ya kuma kira bisa sunan Ubangiji. A can ya kafa tentinsa, a can kuma bayinsa suka haƙa wata rijiya.
And than he buylded an aulter there and called vpo the name of the LORde and there pitched his tente. And there Isaacs servauntes dygged a well.
26 Ana cikin haka, sai Abimelek ya zo wurinsa daga Gerar, tare da Ahuzzat mai ba shi shawara da Fikol shugaban mayaƙansa.
Than came Abimelech to him fro Gerar and Ahusath his frende and Phicol his chefe captayne.
27 Ishaku ya tambaye su, “Me ya kawo ku gare ni, da yake kun yi gāba da ni, kuka kuma kore ni?”
And Isaac sayde vnto the: wherfore come ye to me seige ye hate me and haue put me awaye fro you?
28 Suka amsa, “Mun ga a zahiri cewa Ubangiji yana tare da kai; saboda haka muka ce, ‘Dole rantsuwa ta kasance tsakaninmu da kai.’ Bari mu yi yarjejjeniya da kai
Than sayde they: we sawe that the LORde was with the and therfore we sayde that there shulde be an oothe betwixte vs ad the and that we wolde make a bonde with the:
29 cewa ba za ka cuce mu ba, kamar yadda ba mu fitine ka ba, amma muka yi maka kirki, muka kuma sallame ka cikin salama. Yanzu kuwa kai albarkatacce ne na Ubangiji.”
yt thou shuldeste do vs no hurte as we haue not touched the and haue done vnto the nothinge but good and sed the awaye in peace: for thou art now the blessed of the LORde.
30 Sai Ishaku ya shirya musu liyafa, suka ci suka kuma sha.
And he made the a feast and they ate ad droke.
31 Kashegari da sassafe sai mutanen suka yi wa juna rantsuwa. Sa’an nan Ishaku ya sallame su, suka kuwa tafi cikin salama.
And they rose vp by tymes in the mornynge and sware one to another. And Isaac sent the awaye. And they departed from him in peace.
32 A wannan rana bayin Ishaku suka zo suka faɗa masa game da rijiyar da suka haƙa. Suka ce, “Mun sami ruwa!”
And ye same daye came Isaacs servautes and tolde hi of a well which they had dygged: and sayde vnto hi that thei had founde water.
33 Sai ya kira ta Shiba, don haka har wa yau ana kira garin Beyersheba.
And he called it Seba wherfore the name of the cyte is called Berseba vnto this daye.
34 Sa’ad da Yaƙub ya kai shekaru arba’in da haihuwa, sai ya auri Yudit’yar Beyeri mutumin Hitti, da kuma Basemat’yar Elon mutumin Hitti.
When Esau was. xl. yere olde he toke to wyfe Judith the doughter of Bely an Hethite and Busmath the doughter of Elon an Hethite
35 Su ne suka zama sanadin baƙin ciki ga Ishaku da Rebeka.
also which were dishobedient vnto Isaac and Rebecca.

< Farawa 26 >