< Farawa 26 >

1 Aka yi yunwa a ƙasar; ban da yunwar da aka yi da fari a zamanin Ibrahim, sai Ishaku ya tafi wurin Abimelek sarkin Filistiyawa a Gerar.
And it was a famine in the land besides the famine former which it was in [the] days of Abraham and he went Isaac to Abimelech [the] king of [the] Philistines Gerar towards.
2 Ubangiji kuwa ya bayyana ga Ishaku ya ce, “Kada ka gangara zuwa Masar; ka yi zauna a ƙasar da zan faɗa maka.
And he appeared to him Yahweh and he said may not you go down Egypt towards dwell in the land which I will say to you.
3 Ka zauna a wannan ƙasa na ɗan lokaci, zan kuwa kasance tare da kai, zan kuma albarkace ka. Gama zan ba da waɗannan ƙasashe gare ka da kuma zuriyarka. Zan kuma cika rantsuwar da na yi wa mahaifinka Ibrahim.
Sojourn in the land this so I may be with you and I will bless you for to you and to offspring your I will give all the lands these and I will establish the oath which I swore to Abraham father your.
4 Zan sa zuriyarka ta yi yawa kamar taurari a sararin sama zan kuwa ba su dukan waɗannan ƙasashe, ta wurin’ya’yanka kuma za a albarkaci dukan al’umman duniya,
And I will multiply offspring your like [the] stars of the heavens and I will give to offspring your all the lands these and they will bless themselves by offspring your all [the] nations of the earth.
5 domin Ibrahim ya yi mini biyayya ya kuma kiyaye umarnaina, ƙa’idodina da kuma dokokina.”
Consequence that he listened Abraham to voice my and he kept duty my commandments my statutes my and laws my.
6 Sai Ishaku ya zauna a Gerar.
And he dwelt Isaac in Gerar.
7 Sa’ad da mutanen wurin suka tambaye shi game da matarsa, sai ya ce, “’Yar’uwata ce,” gama yana tsoro yă ce, “Ita matata ce.” Ya yi tunani, “Mutane wannan wuri za su kashe ni ta dalili Rebeka, domin kyakkyawa ce.”
And they asked [the] men of the place of wife his and he said [is] sister my she for he was afraid to say wife my lest they should kill me [the] men of the place on Rebekah for [was] good of appearance she.
8 Sa’ad da Ishaku ya daɗe a can, sai Abimelek sarkin Filistiyawa ya duba daga taga ya ga Ishaku yana rungumar matarsa Rebeka.
And it was that they had become long to him there the days and he looked down Abimelech [the] king of [the] Philistines through the window and he saw and there! Isaac [was] playing with Rebekah wife his.
9 Saboda haka Abimelek ya aika Ishaku yă je, sa’an nan ya ce, “Tabbatacce ita matarka ce! Me ya sa ka ce, ‘Ita’yar’uwata ce?’” Ishaku ya amsa masa ya ce, “Don na yi tsammani zan rasa raina saboda ita.”
And he summoned Abimelech Isaac and he said surely here! [is] wife your she and how? did you say [is] sister my she and he said to him Isaac for I thought lest I should die on her.
10 Sa’an nan Abimelek ya ce, “Me ke nan ka yi mana? Da a ce wani daga mazanmu ya kwana da matarka, ai, da ka jawo laifi a kanmu.”
And he said Abimelech what? this have you done to us like a little he lay with one of the people wife your and you will bring on us guilt.
11 Saboda haka Abimelek ya yi umarni ga dukan mutane. “Duk wanda ya fitine wannan mutum ko matarsa, tabbatacce za a kashe shi.”
And he commanded Abimelech all the people saying who [-ever] touches the man this and wife his certainly he will be put to death.
12 Ishaku ya shuka hatsi a wannan ƙasa, a shekaran nan ya yi girbi ninki ɗari, domin Ubangiji ya albarkace shi.
And he sowed Isaac in the land that and he found in the year that one hundred measures and he blessed him Yahweh.
13 Mutumin ya arzuta, arzikinsa ya yi ta haɓaka har ya zama attajiri.
And he became great the man and he went continuously and becoming great until for he became great exceedingly.
14 Ya kasance da garkunan tumaki da na shanu da bayi masu yawa, har Filistiyawa suka yi ƙyashinsa.
And it be[longed] to him livestock of flock and livestock of herd and service much and they envied him [the] Philistines.
15 Saboda haka dukan rijiyoyin da bayin mahaifinsa suka haƙa a kwanakin da mahaifinsa Ibrahim yake da rai, Filistiyawa sun toshe su, suka kuma ciccike su da ƙasa.
And all the wells which they had dug [the] servants of father his in [the] days of Abraham father his they stopped up them [the] Philistines and they filled them earth.
16 Sai Abimelek ya ce wa Ishaku, “Fita daga cikinmu; ka fi ƙarfinmu.”
And he said Abimelech to Isaac go from with us for you have become [too] powerful for us much.
17 Saboda haka Ishaku ya fita daga can, ya yi sansani a Kwarin Gerar, ya kuma zauna a can.
And he went from there Isaac and he encamped in [the] wadi of Gerar and he dwelt there.
18 Ishaku ya sāke tona rijiyoyi waɗanda dā aka haƙa a zamanin Ibrahim mahaifinsa, gama Filistiyawa suka tattoshe bayan mutuwar Ibrahim, ya kuma sa musu sunayen da mahaifinsa ya ba su.
And he returned Isaac and he dug - [the] wells of water which people had dug in [the] days of Abraham father his and they had stopped up them [the] Philistines after [the] death of Abraham and he called them names like the names which he had called them father his.
19 Barorin Ishaku suka haƙa cikin kwarin suka kuwa sami rijiya mai ruwa mai kyau a can.
And they dug [the] servants of Isaac in the wadi and they found there a well of water living.
20 Amma makiyayan Gerar suka yi faɗa da na Ishaku suka ce, “Ruwan namu ne!” Saboda haka Ishaku ya ba wa rijiyar suna Esek, domin sun yi faɗa da shi.
And they disputed [the] herdsmen of Gerar with [the] herdsmen of Isaac saying [belongs] to us the water and he called [the] name of the well Esek for they quarreled with him.
21 Sai suka haƙa wata rijiya, amma suka yi faɗa a kanta ita ma, saboda haka ya ce da ita Sitna.
And they dug a well another and they disputed also on it and he called name its Sitnah.
22 Sai Ishaku ya matsa daga can ya sāke haƙa wata rijiyar, babu wani kuma da yi faɗa a kanta. Sai ya ba ta suna Rehobot, yana cewa, “Yanzu Ubangiji ya ba mu wuri, za mu kuwa yi ta haihuwa a ƙasar.”
And he moved on from there and he dug a well another and not they disputed on it and he called name its Rehoboth and he said that now he has made space Yahweh for us and we will be fruitful in the land.
23 Daga can ya haura zuwa Beyersheba.
And he went up from there Beer Sheba.
24 A wannan dare Ubangiji ya bayyana gare shi ya ce, “Ni ne Allah na mahaifinka Ibrahim. Kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai, zan albarkace ka, zan kuma ƙara yawan zuriyarka saboda bawana Ibrahim.”
And he appeared to him Yahweh in the night that and he said I [am] [the] God of Abraham father your may not you be afraid for [am] with you I and I will bless you and I will multiply offspring your for sake of Abraham servant my.
25 Sai Ishaku ya gina bagade a can, ya kuma kira bisa sunan Ubangiji. A can ya kafa tentinsa, a can kuma bayinsa suka haƙa wata rijiya.
And he built there an altar and he called on [the] name of Yahweh and he pitched there tent his and they dug there [the] servants of Isaac a well.
26 Ana cikin haka, sai Abimelek ya zo wurinsa daga Gerar, tare da Ahuzzat mai ba shi shawara da Fikol shugaban mayaƙansa.
And Abimelech he came to him from Gerar and Ahuzzah close friend his and Phicol [the] commander of army his.
27 Ishaku ya tambaye su, “Me ya kawo ku gare ni, da yake kun yi gāba da ni, kuka kuma kore ni?”
And he said to them Isaac why? have you come to me and you you hate me and you sent away me from with you.
28 Suka amsa, “Mun ga a zahiri cewa Ubangiji yana tare da kai; saboda haka muka ce, ‘Dole rantsuwa ta kasance tsakaninmu da kai.’ Bari mu yi yarjejjeniya da kai
And they said certainly we have seen that he has been Yahweh - with you and we said let it be please an oath between us between us and between you and let us make a covenant with you.
29 cewa ba za ka cuce mu ba, kamar yadda ba mu fitine ka ba, amma muka yi maka kirki, muka kuma sallame ka cikin salama. Yanzu kuwa kai albarkatacce ne na Ubangiji.”
If you will do with us harm just as not we have touched you and just as we have done with you only good and we sent away you in peace you now [are] blessed of Yahweh.
30 Sai Ishaku ya shirya musu liyafa, suka ci suka kuma sha.
And he prepared for them a feast and they ate and they drank.
31 Kashegari da sassafe sai mutanen suka yi wa juna rantsuwa. Sa’an nan Ishaku ya sallame su, suka kuwa tafi cikin salama.
And they rose early in the morning and they swore an oath each to brother his and he sent off them Isaac and they went from with him in peace.
32 A wannan rana bayin Ishaku suka zo suka faɗa masa game da rijiyar da suka haƙa. Suka ce, “Mun sami ruwa!”
And it was - on the day that and they came [the] servants of Isaac and they told to him on [the] causes of the well which they had dug and they said to him we have found water.
33 Sai ya kira ta Shiba, don haka har wa yau ana kira garin Beyersheba.
And he called it Shibah there-fore [the] name of the city [is] Beer Sheba until the day this.
34 Sa’ad da Yaƙub ya kai shekaru arba’in da haihuwa, sai ya auri Yudit’yar Beyeri mutumin Hitti, da kuma Basemat’yar Elon mutumin Hitti.
And he was Esau a son of forty year[s] and he took a wife Judith [the] daughter of Beeri the Hittite and Basemath [the] daughter of Elon the Hittite.
35 Su ne suka zama sanadin baƙin ciki ga Ishaku da Rebeka.
And they were bitterness of spirit to Isaac and to Rebekah.

< Farawa 26 >