< Farawa 25 >
1 Ibrahim ya auro wata mace, mai suna Ketura.
E Abrahão tomou outra mulher; e o seu nome era Ketura;
2 Ta haifa masa Zimran, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak da Shuwa.
E pariu-lhe Zimran, e Joksan, e Medan, e Midian, e Jisbac, e Shuah.
3 Yokshan shi ne mahaifin Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Ashur, da mutanen Letush, da kuma mutanen Lewummin.
E Joksan gerou Seba e Dedan: e os filhos de Dedan foram Assurim, e Letusim e Leummim.
4 ’Ya’yan Midiyan maza su ne, Efa, Efer, Hanok, Abida, da kuma Elda’a. Dukan waɗannan zuriyar Ketura ce.
E os filhos de Midian foram Epha, e Epher, e Henoch, e Abidah, e Eldah: estes todos foram filhos de Ketura.
5 Ibrahim ya bar wa Ishaku kome da ya mallaka.
Porém Abrahão deu tudo o que tinha a Isaac;
6 Amma yayinda Ibrahim yake da rai, ya ba wa’ya’yan ƙwarƙwaransa maza kyautai, ya kuma sallame su daga ɗansa Ishaku zuwa ƙasashen gabas.
Mas aos filhos das concubinas que Abrahão tinha, deu Abrahão presentes, e, vivendo elle ainda, despediu-os do seu filho Isaac, ao oriente, para a terra oriental.
7 Duka-duka, Ibrahim ya yi shekara ɗari da saba’in da biyar.
Estes pois são os dias dos annos da vida de Abrahão, que viveu cento e setenta e cinco annos.
8 Sa’an nan Ibrahim ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu da kyakkyawar tsufa, tsoho da kuma shekaru masu yawa; aka kuma tara shi ga mutanensa.
E Abrahão expirou e morreu em boa velhice, velho e farto de dias: e foi congregado ao seu povo;
9 ’Ya’yansa maza kuwa Ishaku da Ishmayel suka binne shi cikin kogon Makfela, kusa da Mamre, a cikin filin Efron ɗan Zohar mutumin Hitti,
E sepultaram-o Isaac e Ishmael, seus filhos, na cova de Machpelah, no campo d'Ephron, filho de Zohar hetheo, que estava em frente de Mamre,
10 filin da Ibrahim ya saya daga Hittiyawa. A nan aka binne Ibrahim tare da matarsa Saratu.
O campo que Abrahão comprara aos filhos de Heth. Ali está sepultado Abrahão, e Sarah sua mulher.
11 Bayan rasuwar Ibrahim, Allah ya albarkaci ɗansa Ishaku wanda a lokacin yana zama kusa da Beyer-Lahai-Royi.
E aconteceu depois da morte de Abrahão, que Deus abençoou a Isaac seu filho; e habitava Isaac junto ao poço Lahai-roi.
12 Waɗannan su ne zuriyar Ishmayel ɗan Ibrahim, wanda Hagar mutuniyar Masar, baranyar Saratu, ta haifa wa Ibrahim.
Estas porém são as gerações de Ishmael filho de Abrahão, que a serva de Sarah, Hagar Egypcia, pariu a Abrahão.
13 Ga jerin sunayen’ya’yan Ishmayel maza bisa ga haihuwarsu, Nebayiwot ɗan farin Ishmayel, Kedar, Adbeyel, Mibsam,
E estes são os nomes dos filhos de Ishmael pelos seus nomes, segundo as suas gerações: o primogenito de Ishmael era Nebajoth, depois Kedar, e Abdeel, e Mibsam,
E Misma, e Duma, e Massa,
15 Hadad, Tema, Yetur, Nafish da Kedema.
Hadar, e Tema, Jetur, Nafis, e Kedma.
16 Waɗannan su ne’ya’yan Ishmayel maza, waɗanda kuma suke sunayen kabilu goma sha biyu masu mulki bisa ga wuraren zamansu da sansaninsu.
Estes são os filhos de Ishmael, e estes são os seus nomes pelas suas villas e pelos seus castellos: doze principes segundo as suas familias.
17 Duka-duka Ishmayel ya yi shekara ɗari da talatin da bakwai; sai ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa.
E estes são os annos da vida de Ishmael, cento e trinta e sete annos; e elle expirou, e morreu, e foi congregado ao seu povo.
18 Zuriyarsa sun zauna tsakanin Hawila ne da Shur, wanda yake kusa da gabashin iyakar Masar wajen Asshur. Sun yi zaman rikici da dukan sauran’yan’uwansu.
E habitaram desde Havila até Sur, que está em frente do Egypto, indo para Assur; e fez o seu assento diante da face de todos os seus irmãos.
19 Waɗannan su ne zuriyar Ishaku ɗan Ibrahim. Ibrahim ya haifi Ishaku,
E estas são as gerações de Isaac, filho de Abrahão: Abrahão gerou a Isaac:
20 Ishaku yana da shekara arba’in sa’ad da ya auri Rebeka’yar Betuwel, mutumin Aram, daga Faddan Aram,’yar’uwar Laban mutumin Aram.
E era Isaac da edade de quarenta annos, quando tomou a Rebecca, filha de Bethuel arameo de Paddan-aram, irmã de Labão arameo, por sua mulher.
21 Ishaku ya yi addu’a ga Ubangiji a madadin matarsa, saboda ba ta haihuwa. Ubangiji ya amsa addu’arsa, matarsa Rebeka kuwa ta yi ciki.
E Isaac orou instantemente ao Senhor por sua mulher, porquanto era esteril; e o Senhor ouviu as suas orações, e Rebecca sua mulher concebeu.
22 Jariran suka kama kokawa da juna a cikinta, sai ta ce, “Me ya sa wannan yake faruwa da ni?” Saboda haka ta tafi don ta nemi nufin Ubangiji.
E os filhos luctavam dentro d'ella; então disse: Se assim é, porque sou eu assim? E foi-se a perguntar ao Senhor.
23 Ubangiji ya ce mata, “Al’ummai biyu suna a cikin mahaifarki mutum biyu da za ki haifa, za su rabu da juna, ɗayan zai fi ɗayan ƙarfi, babban kuma zai bauta wa ƙaramin.”
E o Senhor lhe disse: Duas nações ha no teu ventre, e dois povos se dividirão das tuas entranhas, e um povo-será mais forte do que o outro povo, e o maior servirá ao menor.
24 Da lokaci ya yi da za tă haihu, sai ga’yan biyu maza a mahaifarta.
E cumprindo-se os seus dias para parir, eis gemeos no seu ventre.
25 Wanda ya fara fita ja ne, dukan jikinsa kuwa kamar riga mai gashi. Don haka aka sa masa suna Isuwa.
E saiu o primeiro ruivo e todo como um vestido cabelludo; por isso chamaram o seu nome Esaú.
26 Bayan wannan, ɗan’uwansa ya fito, da hannunsa yana riƙe da ɗiɗɗigen Isuwa; don haka aka sa masa suna Yaƙub. Ishaku yana da shekara sittin, lokacin da Rebeka ta haife su.
E depois saiu o seu irmão, agarrada sua mão ao calcanhar de Esaú; por isso se chamou o seu nome Jacob. E era Isaac da edade de sessenta annos quando os gerou.
27 Yaran suka yi girma, Isuwa kuwa ya zama riƙaƙƙen maharbi, mutumin jeji, yayinda Yaƙub, shiru-shiru ne mai son zama a tentuna.
E cresceram os meninos, e Esaú foi varão perito na caça, varão do campo; mas Jacob era varão simples, habitando em tendas.
28 Ishaku, mai son ci naman jeji, ya ƙaunaci Isuwa, amma Rebeka ta ƙaunaci Yaƙub.
E amava Isaac a Esaú, porque a caça era de seu gosto, mas Rebecca amava a Jacob.
29 Wata rana sa’ad da Yaƙub yana dafa fate. Isuwa ya shigo daga jeji, da yunwa sosai.
E Jacob cozera um guisado; e veiu Esaú do campo, e estava elle cançado:
30 Ya ce wa Yaƙub, “Ina roƙonka, ka ɗan ɗiba mini faten nan! Ina fama da yunwa!” (Shi ya sa aka kira shi Edom.)
E disse Esaú a Jacob: Deixa-me, peço-te, sorver d'esse guisado vermelho, porque estou cançado. Por isso se chamou o seu nome Edom.
31 Yaƙub ya amsa ya ce, “Ka fara sayar mini da matsayinka na ɗan fari tukuna.”
Então disse Jacob: Vende-me hoje a tua primogenitura.
32 Isuwa ya ce, “Duba, ina gab da mutuwa, me matsayina na ɗan fari zai yi mini?”
E disse Esaú: Eis que estou a ponto de morrer, e para que me servirá logo a primogenitura?
33 Amma Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini tukuna.” Don haka ya rantse masa, ya sayar da matsayinsa na ɗan fari ga Yaƙub.
Então disse Jacob: Jura-me hoje. E jurou-lhe e vendeu a sua primogenitura a Jacob.
34 Sa’an nan Yaƙub ya ba wa Isuwa burodi da ɗan miyan lansir. Ya ci, ya sha, sa’an nan ya tashi ya tafi. Ta haka Isuwa ya yi banza da matsayinsa na ɗan fari.
E Jacob deu pão a Esaú e o guisado das lentilhas; e comeu, e bebeu, e levantou-se, e foi-se. Assim desprezou Esaú a sua primogenitura.