< Farawa 25 >

1 Ibrahim ya auro wata mace, mai suna Ketura.
[Some time after Sarah died], Abraham married another woman, whose name was Keturah.
2 Ta haifa masa Zimran, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak da Shuwa.
She later gave birth to six sons: Zimran, Jokshan, Medan, Midian, Ishbak, and Shuah.
3 Yokshan shi ne mahaifin Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Ashur, da mutanen Letush, da kuma mutanen Lewummin.
Jokshan became the father of two sons, Sheba and Dedan. The descendants of Dedan were the Asshur people-group, the Letush people-group, and the Leum people-group.
4 ’Ya’yan Midiyan maza su ne, Efa, Efer, Hanok, Abida, da kuma Elda’a. Dukan waɗannan zuriyar Ketura ce.
The sons of Midian were Ephah, Epher, Hanoch, Abida, and Eldaah. They were all descendants of Keturah.
5 Ibrahim ya bar wa Ishaku kome da ya mallaka.
Abraham declared that after he died, Isaac would inherit everything he owned.
6 Amma yayinda Ibrahim yake da rai, ya ba wa’ya’yan ƙwarƙwaransa maza kyautai, ya kuma sallame su daga ɗansa Ishaku zuwa ƙasashen gabas.
But while Abraham was still living, he gave gifts to the sons of his (concubines/slaves that he had taken to be his secondary wives), and then he sent them away to live in a land to the east, to keep them far from his son Isaac.
7 Duka-duka, Ibrahim ya yi shekara ɗari da saba’in da biyar.
Abraham lived until he was 175 years old.
8 Sa’an nan Ibrahim ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu da kyakkyawar tsufa, tsoho da kuma shekaru masu yawa; aka kuma tara shi ga mutanensa.
He died at a very old age, joining his ancestors who had died previously [DOU].
9 ’Ya’yansa maza kuwa Ishaku da Ishmayel suka binne shi cikin kogon Makfela, kusa da Mamre, a cikin filin Efron ɗan Zohar mutumin Hitti,
His sons Isaac and Ishmael buried his body in the cave at Machpelah area, near Mamre, in the field that Abraham had previously bought from Ephron, one of the descendants of Heth.
10 filin da Ibrahim ya saya daga Hittiyawa. A nan aka binne Ibrahim tare da matarsa Saratu.
Isaac and Ishmael buried his body there, where Abraham previously buried his wife Sarah.
11 Bayan rasuwar Ibrahim, Allah ya albarkaci ɗansa Ishaku wanda a lokacin yana zama kusa da Beyer-Lahai-Royi.
After Abraham died, God blessed his son Isaac. And Isaac moved to live near Beer-Lahai-Roi.
12 Waɗannan su ne zuriyar Ishmayel ɗan Ibrahim, wanda Hagar mutuniyar Masar, baranyar Saratu, ta haifa wa Ibrahim.
(These are/I will now give a list of) the descendants of Abraham’s son, Ishmael, to whom Sarah’s female slave, Hagar from Egypt, had given birth.
13 Ga jerin sunayen’ya’yan Ishmayel maza bisa ga haihuwarsu, Nebayiwot ɗan farin Ishmayel, Kedar, Adbeyel, Mibsam,
These are their names, in the order in which they were born: Ishmael’s oldest son was named Nebaioth. After him were born Kedar, Adbeel, Mibsam,
14 Mishma, Duma, Massa,
Mishma, Dumah, Massa,
15 Hadad, Tema, Yetur, Nafish da Kedema.
Hadar, Tema, Jetur, Naphish, and Kedemah.
16 Waɗannan su ne’ya’yan Ishmayel maza, waɗanda kuma suke sunayen kabilu goma sha biyu masu mulki bisa ga wuraren zamansu da sansaninsu.
The twelve sons of Ishmael became the leaders/chiefs of people-groups that had those names. They each had their own settlement and campsite.
17 Duka-duka Ishmayel ya yi shekara ɗari da talatin da bakwai; sai ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa.
Ishmael lived until he was 137 years old. Then he died, [EUP] joining his ancestors who had previously died.
18 Zuriyarsa sun zauna tsakanin Hawila ne da Shur, wanda yake kusa da gabashin iyakar Masar wajen Asshur. Sun yi zaman rikici da dukan sauran’yan’uwansu.
His descendants (settled/went to live) in the area between Shur and Havilah, near the border of Egypt as a person travels toward Asshur. All of their camps were close to each other (OR, they all frequently attacked each other).
19 Waɗannan su ne zuriyar Ishaku ɗan Ibrahim. Ibrahim ya haifi Ishaku,
(This is an account of/I will now tell you about) Abraham’s son, Isaac. Abraham became the father of Isaac,
20 Ishaku yana da shekara arba’in sa’ad da ya auri Rebeka’yar Betuwel, mutumin Aram, daga Faddan Aram,’yar’uwar Laban mutumin Aram.
and when Isaac was 40 years old, he married Rebekah, the daughter of Bethuel. Bethuel was one of the descendants of Aram from Paddan-Aram. Rebekah was the sister of Laban, who belonged to the Aram people-group.
21 Ishaku ya yi addu’a ga Ubangiji a madadin matarsa, saboda ba ta haihuwa. Ubangiji ya amsa addu’arsa, matarsa Rebeka kuwa ta yi ciki.
Almost 20 years after they were married, Rebekah still had no children. So Isaac prayed to Yahweh concerning his wife, and Yahweh answered his prayer. His wife Rebekah became pregnant.
22 Jariran suka kama kokawa da juna a cikinta, sai ta ce, “Me ya sa wannan yake faruwa da ni?” Saboda haka ta tafi don ta nemi nufin Ubangiji.
She was carrying twins in her womb, and they kept jostling each other. So she said, “Why is it [that this is happening to me]?” So she asked Yahweh about it.
23 Ubangiji ya ce mata, “Al’ummai biyu suna a cikin mahaifarki mutum biyu da za ki haifa, za su rabu da juna, ɗayan zai fi ɗayan ƙarfi, babban kuma zai bauta wa ƙaramin.”
Yahweh said to her, “The older one of your twins will serve the younger one. The twins will be ancestors of two nations. And those two people-groups will separate from each other.” [CHI]
24 Da lokaci ya yi da za tă haihu, sai ga’yan biyu maza a mahaifarta.
When Rebekah gave birth, it was true! Twin boys were born!
25 Wanda ya fara fita ja ne, dukan jikinsa kuwa kamar riga mai gashi. Don haka aka sa masa suna Isuwa.
The first one born was red, and his body had hair all over it, like a garment made of hair. So they named him Esau, [which sounds like the Hebrew word that means ‘hairy'].
26 Bayan wannan, ɗan’uwansa ya fito, da hannunsa yana riƙe da ɗiɗɗigen Isuwa; don haka aka sa masa suna Yaƙub. Ishaku yana da shekara sittin, lokacin da Rebeka ta haife su.
Then his brother was born, grasping Esau’s heel. So they named him Jacob, [which sounds like the Hebrew word that means ‘heel’]. Isaac was 60 years old when the twins were born.
27 Yaran suka yi girma, Isuwa kuwa ya zama riƙaƙƙen maharbi, mutumin jeji, yayinda Yaƙub, shiru-shiru ne mai son zama a tentuna.
When the boys grew up, Esau became a skilled hunter. He spent a lot of time out in the fields. Jacob was a quiet man who stayed close to the campsite.
28 Ishaku, mai son ci naman jeji, ya ƙaunaci Isuwa, amma Rebeka ta ƙaunaci Yaƙub.
Isaac liked Esau more, because he enjoyed the taste of the meat of the animals that Esau killed. But Rebekah liked Jacob more.
29 Wata rana sa’ad da Yaƙub yana dafa fate. Isuwa ya shigo daga jeji, da yunwa sosai.
One day while Jacob was cooking some stew, Esau came home from the field, very hungry.
30 Ya ce wa Yaƙub, “Ina roƙonka, ka ɗan ɗiba mini faten nan! Ina fama da yunwa!” (Shi ya sa aka kira shi Edom.)
He said to Jacob, “Give me some of that red stew to eat right now, because I am very hungry!” [That is why Esau’s other name was Edom, [which sounds like the Hebrew word that means ‘red]’.]
31 Yaƙub ya amsa ya ce, “Ka fara sayar mini da matsayinka na ɗan fari tukuna.”
Jacob said, “I will give you some if you sell me (your birthright/the privileges you have because you are the firstborn son).”
32 Isuwa ya ce, “Duba, ina gab da mutuwa, me matsayina na ɗan fari zai yi mini?”
Esau replied, “Well, I am about to die [from being so hungry]. [If I die now], (my birthright will not benefit me./What good will my birthright be to me?)” [RHQ]
33 Amma Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini tukuna.” Don haka ya rantse masa, ya sayar da matsayinsa na ɗan fari ga Yaƙub.
Jacob said, “(Swear to/Solemnly promise) me that you are giving me the privileges that you will have from being the firstborn son!” So that is what Esau did. He sold his birthright to Jacob.
34 Sa’an nan Yaƙub ya ba wa Isuwa burodi da ɗan miyan lansir. Ya ci, ya sha, sa’an nan ya tashi ya tafi. Ta haka Isuwa ya yi banza da matsayinsa na ɗan fari.
Then Jacob gave to Esau some bread and some stew made of lentils/beans. Esau ate and drank, and then he got up and left. By doing that, Esau showed that he (was not interested in/did not value) the privileges that would be his because of being the firstborn son.

< Farawa 25 >