< Farawa 24 >

1 Yanzu fa Ibrahim ya tsufa, yana da shekaru masu yawa, Ubangiji kuma ya albarkace shi a kowace hanya.
Or Abraham était vieux et plein de jours; et le Seigneur l’avait béni en toutes choses.
2 Sai Ibrahim ya ce wa babban bawan gidansa, wanda yake lura da duk abin da yake da shi, “Sa hannunka a ƙarƙashin cinyata.
Et il dit au serviteur le plus ancien de sa maison, qui présidait sur tout ce qu’il avait: Pose ta main sous ma cuisse,
3 Ina so ka rantse da sunan Ubangiji Allah na sama da ƙasa, cewa ba za ka samo wa ɗana mata daga’yan matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama cikinsu ba.
Afin que je t’adjure par le Seigneur Dieu du ciel et de la terre, que tu ne prendras pas de femme pour mon fils parmi les filles des Chananéens au milieu desquels j’habite;
4 Amma za ka tafi ƙasata da kuma cikin’yan’uwana, ka samo mata saboda ɗana Ishaku.”
Mais que tu iras dans mon pays et dans ma parenté, et que c’est de là que tu prendras une femme pour mon fils Isaac.
5 Bawan ya ce masa, “Me zai faru in matar ba tă yarda tă zo tare da ni zuwa wannan ƙasa ba? In komar da ɗanka a ƙasar da ka fito ne ke nan?”
Le serviteur répondit: Si la femme ne veut pas venir avec moi dans ce pays-ci, dois-je remener votre fils dans le lieu d’où vous êtes sorti?
6 Ibrahim ya ce, “Ka tabbata ba ka komar da ɗana can ba.”
Et Abraham dit: Garde-toi de jamais y remener mon fils
7 Ubangiji Allah na sama, wanda ya fitar da ni daga gidan mahaifina, da kuma ƙasar asalina wanda kuma ya yi magana da ni, ya yi mini alkawari da rantsuwa cewa, “Ga zuriyarka zan ba da wannan ƙasa, zai aika mala’ikansa yă sha gabanka domin ka samo wa ɗana mata daga can.
Le Seigneur Dieu du ciel qui m’a tiré de la maison de mon père et du pays de ma naissance, qui m’a parlée et m’a juré, disant: C’est à ta postérité que je donnerai ce pays, enverra lui-même son ange devant toi, et tu prendras de là une femme pour mon fils.
8 In matar ba tă yarda tă zo tare da kai ba, za a kuɓutar da kai daga wannan rantsuwa. Sai dai kada ka kai ɗana a can.”
Que si la femme ne veut pas te suivre, tu ne seras pas engagé par le serment; seulement ne remène jamais là mon fils.
9 Saboda haka bawan ya sa hannunsa a ƙarƙashin cinyar maigidansa Ibrahim, ya kuma rantse masa game da wannan al’amari.
Le serviteur donc posa la main sous la cuisse d’Abraham son maître, et il le lui jura.
10 Sai bawan ya ɗibi raƙuma goma na maigidansa ya tafi, ɗauke da kowane irin abubuwa masu kyau daga wurin maigidansa. Ya fita don yă tafi Aram-Naharayim, ya kama hanyarsa zuwa garin Nahor.
C’est pourquoi il prit dix chameaux du troupeau de son maître, et s’en alla portant avec lui de tous ses biens; et étant parti, il se dirigea en Mésopotamie, vers la ville de Nachor.
11 Ya sa raƙuman suka durƙusa kusa da rijiya a bayan gari; wajen yamma ne, lokacin da mata sukan fita ɗiban ruwa.
Et lorsqu’il eut fait agenouiller ses chameaux hors de la ville, près du puits, sur le soir, temps où les jeunes filles ont coutume de sortir pour puiser de l’eau, il dit:
12 Sai ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ka ba ni nasara yau, ka kuma nuna alheri ga maigidana Ibrahim.
Seigneur Dieu de mon maître Abraham, je vous supplie, venez-moi en aide aujourd’hui, et faites miséricorde à mon maître Abraham.
13 Duba, ina tsaye a bakin rijiyar ruwa,’ya’ya matan mutanen gari kuma suna fitowa domin ɗiban ruwa.
Me voici près de la source d’eau, et les filles des habitants de cette ville sortiront pour puiser de l’eau.
14 Bari yă zama sa’ad da na ce wa wata yarinya, ‘Ina roƙonki ki saukar da tulunki domin in sha,’ in ta ce, ‘Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma’; bari tă zama ita ce ka zaɓa wa bawanka Ishaku. Ta haka zan san cewa ka nuna wa maigidana alheri.”
Que la jeune fille donc à qui je dirai: Incline ta cruche, afin que je boive, et qui répondra: Bois, et je donnerai aussi à boire à tes chameaux, soit celle que vous avez préparée à votre serviteur Isaac: et c’est à cela que je connaîtrai que vous aurez fait miséricorde à mon maître.
15 Kafin ya gama addu’a, sai Rebeka ta fito da tulu a kafaɗarta. Ita’yar Betuwel ɗan Milka, matar Nahor, ɗan’uwan Ibrahim.
Il n’avait pas encore achevé ces mots en lui-même, et voilà que sortit Rébecca, la fille de Bathuel, fils de Melcha, femme de Nachor, frère d’Abraham, laquelle portait une cruche sur son épaule;
16 Yarinyar kuwa kyakkyawa ce, budurwa, ba namijin da ya taɓa kwana da ita. Ta gangara zuwa rijiyar, ta cika tulunta ta kuma hauro.
Jeune fille fort gracieuse, vierge très belle et inconnue à tout homme: or elle était déjà descendue à la fontaine, avait rempli sa cruche, et elle s’en retournait.
17 Bawan ya yi sauri ya same ta ya ce, “Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.”
Aussitôt le serviteur courut au-devant d’elle, et dit: Donne-moi un peu d’eau à boire de ta cruche.
18 Ta ce, “Ka sha, ranka yă daɗe,” ta yi sauri ta saukar da tulun a hannuwanta, ta kuma ba shi, ya sha.
Elle répondit: Bois, mon seigneur; et elle posa promptement sa cruche sur son bras, et elle lui donna à boire.
19 Bayan ta ba shi ya sha, sai ta ce, “Zan ɗebo wa raƙumanka ruwa su ma, har sai sun gama sha.”
Et lorsqu’il eut bu, elle ajouta: Et même pour tes chameaux je puiserai de l’eau, jusqu’à ce que tous aient bu.
20 Sai ta yi sauri ta juye ruwan da yake tulunta cikin kwami, ta koma zuwa rijiyar da gudu don ta ƙara ɗebo ruwa, ta kuma ɗebo isashe saboda dukan raƙumansa.
Et versant sa cruche dans les canaux, elle courut au puits pour puiser de l’eau, et quand elle l’eut puisée, elle la donna à tous les chameaux.
21 Mutumin bai ce uffam ba, ya dai kalle ta sosai don yă san ko Ubangiji ya ba shi nasara a tafiyarsa ko babu.
Cependant lui la contemplait en silence, voulant savoir si le Seigneur avait rendu son voyage heureux ou non.
22 Sa’ad da raƙuman suka gama shan ruwa, mutumin ya fitar da zoben hanci na zinariya mai nauyin giram biyar da woroworo biyu na zinariya masu nauyin shekel goma, ya ba ta.
Or, après que les chameaux eurent bu, cet homme lui présenta des pendants d’oreilles d’or, pesant deux sicles, et autant de bracelets du poids de dix sicles.
23 Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Ke’yar wace ce? Ina roƙonki ki faɗa mini, akwai wuri a gidan mahaifinki da za mu kwana?”
Puis il dit: De qui es-tu fille? dis-le moi: y a-t-il dans la maison de ton père un lieu pour y loger?
24 Sai ta ce masa, “Ni’yar Betuwel ce ɗan da Milka ta haifa wa Nahor.”
Elle répondit: Je suis la fille de Bathuel, fils de Melcha et que lui a engendré Nachor.
25 Ta ƙara da cewa, “Muna da isashen ciyawa da abincin dabbobi, da kuma wuri domin ku kwana.”
Et elle ajouta, disant: Il y a chez nous beaucoup de foin et de paille, et un lieu spacieux pour y loger.
26 Sa’an nan mutumin ya rusuna ya yi wa Ubangiji sujada,
L’homme s’inclina, et adora le Seigneur,
27 yana cewa, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, wanda bai daina nuna alheri da amincinsa ga maigidana ba. Ni kam, Ubangiji ya bishe ni a tafiyata zuwa gidan’yan’uwan maigidana.”
Disant: Béni le Seigneur Dieu de mon maître Abraham, qui ne lui a pas retiré sa miséricorde et sa fidélité, et qui m’a conduit par une voie droite dans la maison du frère de mon maître!
28 Yariyan ta gudu ta faɗa wa mutanen gidan mahaifiyarta game da abubuwan nan.
C’est pourquoi la jeune fille courut et annonça à la maison de sa mère tout ce qu’elle avait entendu.
29 Rebeka fa tana da wani ɗan’uwa mai suna Laban, sai ya yi hanzari ya fita zuwa wurin mutumin a rijiyar.
Or Rébecca avait un frère du nom de Laban, qui sortit en grande hâte pour aller vers l’homme là où était la fontaine.
30 Nan da nan da ya ga zoben hancin da woroworo a hannuwan’yar’uwansa, ya kuma ji Rebeka ta faɗa abin da mutumin ya ce mata, sai ya fita zuwa wurin mutumin, ya same shi yana tsaye wajen raƙuma kusa da rijiyar.
Et, comme il avait vu les pendants d’oreilles et les bracelets aux mains de sa sœur, et qu’il avait entendu toutes ses paroles, lorsqu’elle disait: Ainsi m’a parlé cet homme, il vint vers l’homme, qui se tenait à côté de ses chameaux et près de la source d’eau.
31 Sai ya ce, “Zo, ya kai mai albarka na Ubangiji, don me kake tsaye a waje? Gama na shirya gida da wuri domin raƙuma.”
Et il lui dit: Entre, béni du Seigneur; pourquoi restes-tu dehors? J’ai préparé la maison et un lieu pour tes chameaux.
32 Don haka mutumin ya tafi gidan, aka kuma saukar da kaya kan raƙuman. Aka kawo wa raƙuman ciyawa da abincin dabbobi, aka kuma kawo ruwa dominsa da mutanensa su wanke ƙafafunsu.
Puis il le fit entrer dans le logis, dessangla les chameaux, leur donna de la paille et du foin, et à lui-même et à ceux qui étaient venus avec lui, de l’eau pour laver leurs pieds.
33 Sa’an nan aka ajiye abinci a gabansa, amma ya ce, “Ba zan ci ba, sai na faɗi abin da yake tafe da ni.” Sai Laban ya ce, “Faɗa mana.”
On mit aussi du pain en sa présence. Il dit: Je ne mangerai pas que je ne vous aie énoncé mon message. Laban lui répondit: Parle.
34 Saboda haka ya ce, “Ni bawan Ibrahim ne.
Alors lui: Je suis, dit-il, serviteur d’Abraham.
35 Ubangiji ya albarkaci maigidana sosai, ya kuma zama mai arziki. Ya ba shi tumaki, shanu, azurfa, zinariya, bayi maza da mata, raƙuma, da kuma jakuna.
Le Seigneur a béni beaucoup mon maître, et il est devenu grand; car il lui a donné des brebis et des bœufs, de l’argent et de l’or, des serviteurs et des servantes, des chameaux et des ânes.
36 Saratu matar maigidana ta haifa masa ɗa a tsufanta, ya kuma ba shi duk mallakarsa.
Et Sara la femme de mon maître lui a enfanté un fils dans sa vieillesse, et il lui a donné tout ce qu’il avait.
37 Maigidana ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, ‘Kada ka ɗauko wa ɗana mata daga’ya’ya matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama a ƙasarsu,
Et mon maître m’a adjuré, disant: Tu ne prendras point de femme pour mon fils parmi les filles des Chananéens dans le pays desquels j’habite;
38 amma ka tafi wajen gidan mahaifina da kuma dangina, ka ɗauko wa ɗana mata.’
Mais tu iras à la maison de mon père, et tu prendras dans ma parenté une femme pour mon fils.
39 “Sai na ce wa maigidana, ‘A ce matar ba tă yarda tă zo tare da ni ba fa?’
Et moi j’ai répondu à mon maître: Mais si la femme ne veut pas venir avec moi?
40 “Maigidana ya ce, ‘Ubangiji wanda yake tare da ni zai aiki mala’ikansa tare da kai, yă kuma sa tafiyarka tă yi nasara, don ka samo wa ɗana mata daga dangina, daga kuma gidan mahaifina.
Le Seigneur, reprit-il, en présence de qui je marche, enverra son ange avec toi, et dirigera ta voie; et tu prendras une femme pour mon fils dans ma parenté et de la maison de mon père.
41 Ta haka za ka kuɓuta daga rantsuwata sa’ad da ka tafi wurin dangina, ko ma sun ƙi su ba ka ita, za ka kuɓuta daga rantsuwata.’
Tu seras exempt de ma malédiction, si tu vas vers mes parents et qu’ils te refusent.
42 “Sa’ad da na zo rijiya a yau, na ce, ‘Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ina roƙonka ka ba ni nasara a tafiyar da na yi.
Je suis donc venu aujourd’hui près de la source d’eau, et j’ai dit: Seigneur Dieu de mon maître Abraham, si vous avez dirigé la voie dans laquelle je marche maintenant,
43 Duba, ina tsaye kusa da wannan rijiya; in wata yarinya ta fito domin tă ɗiba ruwa, wadda in na ce mata, “Ina roƙonki bari in ɗan sha ruwa daga tulunki,”
Me voici près de la source d’eau; que la vierge donc qui sortira pour puiser de l’eau, qui entendra de moi: Donne-moi un peu d’eau à boire de ta cruche,
44 in ta ce, “Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma,” bari tă zama wadda Ubangiji ya zaɓar wa ɗan maigidana.’
Et qui me répondra: Bois, toi; je puiserai ensuite de l’eau pour tes chameaux, soit la femme que le Seigneur a préparée au fils de mon maître.
45 “Kafin in gama addu’ar, a zuciyata, sai ga Rebeka ta fito da tulunta a kafaɗarta. Ta gangara zuwa rijiyar ta ɗebo ruwa, na kuma ce mata, ‘Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.’
Pendant que sans rien dire, j’agitais ces pensées au-dedans de moi-même, parut Rébecca venant avec sa cruche qu’elle portait sur l’épaule: elle descendit à la fontaine et puisa de l’eau. Et je lui dis: Donne-moi un peu à boire.
46 “Ta yi sauri ta saukar da tulun daga kafaɗarta ta ce, ‘Sha, zan kuma ba wa raƙumanka su ma.’ Sai na sha, ta kuma shayar da raƙumana su ma.
Elle se hâtant, descendit sa cruche de dessus son épaule et me dit: Bois, toi; je donnerai ensuite à boire à tes chameaux. Je bus, et elle abreuva les chameaux.
47 “Na tambaye ta, ‘Ke’yar wane ne?’ “Ta ce, ‘’Yar Betuwel ɗan Nahor, wanda Milka ta haifa masa.’ “Sai na sa mata zobe a hancinta, woroworo kuma a hannuwata,
Je l’interrogeai alors, et je dis: De qui es-tu fille? Elle répondit: Je suis fille de Bathuel, fils de Nachor, que lui a enfanté Melcha. Je lui ai donc mis les pendants d’oreilles pour orner son visage, et j’ai attaché les bracelets à ses bras.
48 na kuma sunkuya na yi wa Ubangiji sujada. Na yabi Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim wanda ya bi da ni a hanyar da take daidai, don in samo wa ɗan maigidana jikanyar ɗan’uwansa.
Et incliné, j’ai adoré le Seigneur, bénissant le Seigneur Dieu de mon maître Abraham, qui m’a conduit par une voie droite, afin de prendre la fille du frère de mon maître pour son fils.
49 Yanzu fa in za ku nuna wa maigidana alheri da aminci, ku faɗa mini, in kuma ba haka ba, ku faɗa mini, don in san hanyar da zan juya.”
C’est pourquoi, si vous agissez avec miséricorde et loyauté envers mon maître, dites-le-moi; mais si autre chose vous plaît, dites-le-moi encore; afin que j’aille à droite ou à gauche.
50 Laban da Betuwel suka ce, “Wannan daga wurin Ubangiji ne, ba abin da za mu ce I, ko a’a ba.
Laban et Bathuel répondirent: C’est du Seigneur qu’est sortie cette parole; nous ne pouvons en dehors de sa volonté, te dire rien autre chose.
51 Ga Rebeka, ɗauke ta ku tafi, bari tă zama matar ɗan maigidanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
Voici Rébecca devant toi: prends-la, pars, et qu’elle soit la femme du fils de ton maître, selon qu’a parlé le Seigneur.
52 Sa’ad da bawan Ibrahim ya ji abin da suka ce, sai ya rusuna har ƙasa a gaban Ubangiji.
Ce qu’ayant entendu le serviteur d’Abraham, se prosternant en terre, il adora le Seigneur.
53 Sa’an nan bawan ya fito da kayan ado na zinariya da azurfa da kayayyaki na tufafi ya ba wa Rebeka; ya kuma ba wa ɗan’uwanta da mahaifiyarta kyautai masu tsada.
Puis, tirant des vases d’or et d’argent, et des vêtements, il les donna à Rébecca en présent; et à ses frères et à sa mère, il offrit aussi des dons.
54 Sa’an nan shi da mutanen da suke tare da shi suka ci, suka sha, suka kuma kwana a can. Kashegari da safe da suka tashi sai ya ce, “A sallame ni in koma wurin maigidana.”
Le repas commencé, mangeant ensemble et buvant, ils demeurèrent là. Mais se levant le matin, le serviteur dit: Laissez-moi partir, afin que j’aille vers mon maître.
55 Amma ɗan’uwanta da mahaifiyarta suka ce, “Bari yarinyar ta ɗan zauna tare da mu kwana goma ko fiye, sa’an nan ka ta fi.”
Les frères de Rébecca et sa mère répondirent: Que la jeune fille demeure au moins dix jours auprès de nous, et ensuite elle partira.
56 Amma ya ce musu, “Kada ku tsai da ni, tun da Ubangiji ya ba ni nasara a tafiyata. Ku sallame ni domin in tafi wurin maigidana.”
Ne me retenez pas, reprit-il, puisque le Seigneur a dirigé ma voie: laissez-moi partir, afin que j’aille vers mon maître.
57 Sa’an nan suka ce, “Bari mu kira yarinyar mu tambaye ta game da zancen.”
Et ils dirent: Appelons la jeune fille, et demandons-lui ce qu’elle veut.
58 Saboda haka suka kira Rebeka suka ce mata, “Za ki tafi tare da mutumin nan?” Sai ta ce, “Zan tafi.”
Lorsque appelée, elle fut venue, ils lui demandèrent: Veux-tu aller avec cet homme? Elle dit: J’irai.
59 Saboda haka suka sallame Rebeka,’yar’uwarsu, duk da uwar goyonta da bawan Ibrahim da mutanensa.
Ils renvoyèrent donc, elle, sa nourrice, le serviteur d’Abraham et ses compagnons.
60 Suka kuma albarkaci Rebeka suka ce mata, “’Yar’uwarmu, bari ki zama mahaifiyar dubu dubbai, bari zuriyarki su mallaki ƙofofin abokan gābansu.”
Implorant des choses heureuses pour leur sœur, et disant: Tu es notre sœur; puisses-tu croître en mille et mille générations, et puisse ta postérité posséder les portes de ses ennemis!
61 Sa’an nan Rebeka da bayinta mata suka shirya suka hau raƙumansu suka koma tare da mutumin. Da haka bawan ya ɗauki Rebeka ya tafi.
Ainsi Rébecca et ses servantes étant montées sur les chameaux, suivirent le serviteur qui en grande hâte retournait vers son maître.
62 Ishaku kuwa ya zo daga Beyer-Lahai-Royi, gama yana zama a Negeb.
En ce même temps se promenait Isaac dans le chemin qui mène au puits dont le nom est puits Du vivant et voyant; car il habitait dans la terre australe.
63 Wata rana da yamma ya fita zuwa fili domin yă yi tunani, sa’ad da ya ɗaga ido, sai ya ga raƙuma suna zuwa.
Et il était sorti pour méditer dans la campagne, le jour étant déjà sur son déclin: et comme il avait levé les yeux, il vit les chameaux venant de loin.
64 Rebeka ma ta ɗaga ido sai ta ga Ishaku. Ta sauka daga raƙuminta da sauri,
Rébecca aussi, Isaac aperçu, descendit de son chameau,
65 ta ce wa bawan, “Wane ne mutumin can a fili, da yake zuwa yă tarye mu?” Bawan ya ce, “Maigidana ne.” Saboda haka ta ɗauki mayafinta to rufe kanta.
Et dit au serviteur: Quel est cet homme qui vient par la campagne, à notre rencontre? Et il lui dit: C’est mon maître. Et elle, prenant aussitôt son voile, se couvrit.
66 Sai bawan ya faɗa wa Ishaku duk abin da ya yi.
Or le serviteur raconta tout ce qu’il avait fait, à Isaac,
67 Ishaku ya kawo ta cikin tentin mahaifiyarsa Saratu, ya kuma auri Rebeka. Ta haka ta zama matarsa, ya kuwa ƙaunace ta; Ishaku kuma ya ta’azantu bayan rasuwar mahaifiyarsa.
Qui conduisit Rébecca dans la tente de Sara sa mère, et la reçut pour femme: et il l’aima tellement, qu’il tempéra la douleur qu’il avait eue de la mort de sa mère.

< Farawa 24 >