< Farawa 24 >

1 Yanzu fa Ibrahim ya tsufa, yana da shekaru masu yawa, Ubangiji kuma ya albarkace shi a kowace hanya.
Now Abraham was very old and Yahweh had blessed Abraham in all things.
2 Sai Ibrahim ya ce wa babban bawan gidansa, wanda yake lura da duk abin da yake da shi, “Sa hannunka a ƙarƙashin cinyata.
Abraham said to his servant, the one who was the oldest of his household and who was in charge of all that he had, “Put your hand under my thigh
3 Ina so ka rantse da sunan Ubangiji Allah na sama da ƙasa, cewa ba za ka samo wa ɗana mata daga’yan matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama cikinsu ba.
and I will make you swear by Yahweh, the God of heaven and the God of the earth, that you will not get a wife for my son from the daughters of the Canaanites, among whom I make my home.
4 Amma za ka tafi ƙasata da kuma cikin’yan’uwana, ka samo mata saboda ɗana Ishaku.”
But you will go to my country, and to my relatives, and get a wife for my son Isaac.”
5 Bawan ya ce masa, “Me zai faru in matar ba tă yarda tă zo tare da ni zuwa wannan ƙasa ba? In komar da ɗanka a ƙasar da ka fito ne ke nan?”
The servant said to him, “What if the woman will not be willing to follow me to this land? Must I take your son back to the land from which you came?”
6 Ibrahim ya ce, “Ka tabbata ba ka komar da ɗana can ba.”
Abraham said to him, “Make sure that you do not take my son back there!
7 Ubangiji Allah na sama, wanda ya fitar da ni daga gidan mahaifina, da kuma ƙasar asalina wanda kuma ya yi magana da ni, ya yi mini alkawari da rantsuwa cewa, “Ga zuriyarka zan ba da wannan ƙasa, zai aika mala’ikansa yă sha gabanka domin ka samo wa ɗana mata daga can.
Yahweh, the God of heaven, who took me from my father's house and from the land of my relatives, and who promised me with a solemn oath saying, 'To your offspring I will give this land,' he will send his angel before you, and you will get a wife for my son from there.
8 In matar ba tă yarda tă zo tare da kai ba, za a kuɓutar da kai daga wannan rantsuwa. Sai dai kada ka kai ɗana a can.”
But if the woman is not willing to follow you, then you will be free from this oath of mine. Only you are not to take my son back there.”
9 Saboda haka bawan ya sa hannunsa a ƙarƙashin cinyar maigidansa Ibrahim, ya kuma rantse masa game da wannan al’amari.
So the servant put his hand under the thigh of Abraham his master, and swore to him concerning this matter.
10 Sai bawan ya ɗibi raƙuma goma na maigidansa ya tafi, ɗauke da kowane irin abubuwa masu kyau daga wurin maigidansa. Ya fita don yă tafi Aram-Naharayim, ya kama hanyarsa zuwa garin Nahor.
The servant took ten of his master's camels and departed. He also took with him all kinds of gifts from his master. He departed and went to the region of Aram Naharaim, to the city of Nahor.
11 Ya sa raƙuman suka durƙusa kusa da rijiya a bayan gari; wajen yamma ne, lokacin da mata sukan fita ɗiban ruwa.
He made the camels kneel down outside the city by the well of water. It was evening, the time that women go out to draw water.
12 Sai ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ka ba ni nasara yau, ka kuma nuna alheri ga maigidana Ibrahim.
Then he said, “Yahweh, God of my master Abraham, grant me success today and show covenant faithfulness to my master Abraham.
13 Duba, ina tsaye a bakin rijiyar ruwa,’ya’ya matan mutanen gari kuma suna fitowa domin ɗiban ruwa.
Look, here I am standing by the spring of water, and the daughters of the men of the city are coming out to draw water.
14 Bari yă zama sa’ad da na ce wa wata yarinya, ‘Ina roƙonki ki saukar da tulunki domin in sha,’ in ta ce, ‘Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma’; bari tă zama ita ce ka zaɓa wa bawanka Ishaku. Ta haka zan san cewa ka nuna wa maigidana alheri.”
Let it happen like this. When I say to a young woman, 'Please lower your pitcher so that I may drink,' and she says to me, 'Drink, and I will water your camels too,' then let her be the one that you have appointed for your servant Isaac. By this I will know that you have shown covenant faithfulness to my master.”
15 Kafin ya gama addu’a, sai Rebeka ta fito da tulu a kafaɗarta. Ita’yar Betuwel ɗan Milka, matar Nahor, ɗan’uwan Ibrahim.
It came about that even before he had finished speaking, behold, Rebekah came out with her water pitcher on her shoulder. Rebekah was born to Bethuel son of Milkah, the wife of Nahor, Abraham's brother.
16 Yarinyar kuwa kyakkyawa ce, budurwa, ba namijin da ya taɓa kwana da ita. Ta gangara zuwa rijiyar, ta cika tulunta ta kuma hauro.
The young woman was very beautiful and a virgin. No man had slept with her. She went down to the spring and filled her pitcher, and came up.
17 Bawan ya yi sauri ya same ta ya ce, “Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.”
Then the servant ran to meet her and said, “Please give me a little drink of water from your pitcher.”
18 Ta ce, “Ka sha, ranka yă daɗe,” ta yi sauri ta saukar da tulun a hannuwanta, ta kuma ba shi, ya sha.
She said, “Drink, my master,” and she quickly let down her pitcher on her hand, and gave him a drink.
19 Bayan ta ba shi ya sha, sai ta ce, “Zan ɗebo wa raƙumanka ruwa su ma, har sai sun gama sha.”
When she had finished giving him a drink, she said, “I will draw water for your camels also, until they have finished drinking.”
20 Sai ta yi sauri ta juye ruwan da yake tulunta cikin kwami, ta koma zuwa rijiyar da gudu don ta ƙara ɗebo ruwa, ta kuma ɗebo isashe saboda dukan raƙumansa.
So she hurried and emptied her pitcher into the trough, then ran again to the well to draw water, and drew water for all his camels.
21 Mutumin bai ce uffam ba, ya dai kalle ta sosai don yă san ko Ubangiji ya ba shi nasara a tafiyarsa ko babu.
The man watched her in silence to see whether Yahweh had prospered his journey or not.
22 Sa’ad da raƙuman suka gama shan ruwa, mutumin ya fitar da zoben hanci na zinariya mai nauyin giram biyar da woroworo biyu na zinariya masu nauyin shekel goma, ya ba ta.
As the camels finished drinking, the man brought out a gold nose ring weighing half a shekel, and two gold bracelets for her arms weighing ten shekels,
23 Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Ke’yar wace ce? Ina roƙonki ki faɗa mini, akwai wuri a gidan mahaifinki da za mu kwana?”
and asked, “Whose daughter are you? Tell me please, is there room in your father's house for us to spend the night?”
24 Sai ta ce masa, “Ni’yar Betuwel ce ɗan da Milka ta haifa wa Nahor.”
She said to him, “I am the daughter of Bethuel son of Milkah, whom she bore to Nahor.”
25 Ta ƙara da cewa, “Muna da isashen ciyawa da abincin dabbobi, da kuma wuri domin ku kwana.”
She also said to him, “We have plenty of both straw and feed, and also room for you to spend the night.”
26 Sa’an nan mutumin ya rusuna ya yi wa Ubangiji sujada,
Then the man bowed down and worshiped Yahweh.
27 yana cewa, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, wanda bai daina nuna alheri da amincinsa ga maigidana ba. Ni kam, Ubangiji ya bishe ni a tafiyata zuwa gidan’yan’uwan maigidana.”
He said, “Blessed be Yahweh, the God of my master Abraham, who has not forsaken his covenant faithfulness and his trustworthiness toward my master. As for me, Yahweh has led me directly to the house of my master's relatives.”
28 Yariyan ta gudu ta faɗa wa mutanen gidan mahaifiyarta game da abubuwan nan.
Then the young woman ran and told her mother's household about all of these things.
29 Rebeka fa tana da wani ɗan’uwa mai suna Laban, sai ya yi hanzari ya fita zuwa wurin mutumin a rijiyar.
Now Rebekah had a brother, and his name was Laban. Laban ran to the man who was out at the road by the spring.
30 Nan da nan da ya ga zoben hancin da woroworo a hannuwan’yar’uwansa, ya kuma ji Rebeka ta faɗa abin da mutumin ya ce mata, sai ya fita zuwa wurin mutumin, ya same shi yana tsaye wajen raƙuma kusa da rijiyar.
When he had seen the nose ring and the bracelets on his sister's arms, and when he had heard the words of Rebekah his sister, “This is what the man said to me,” he went to the man, and, behold, he was standing by the camels at the spring.
31 Sai ya ce, “Zo, ya kai mai albarka na Ubangiji, don me kake tsaye a waje? Gama na shirya gida da wuri domin raƙuma.”
Then Laban said, “Come, you blessed of Yahweh. Why are you standing outside? I have prepared the house, and a place for the camels.”
32 Don haka mutumin ya tafi gidan, aka kuma saukar da kaya kan raƙuman. Aka kawo wa raƙuman ciyawa da abincin dabbobi, aka kuma kawo ruwa dominsa da mutanensa su wanke ƙafafunsu.
So the man came to the house and he unloaded the camels. The camels were given straw and feed, and water was provided to wash his feet and the feet of the men who were with him.
33 Sa’an nan aka ajiye abinci a gabansa, amma ya ce, “Ba zan ci ba, sai na faɗi abin da yake tafe da ni.” Sai Laban ya ce, “Faɗa mana.”
They set food before him to eat, but he said, “I will not eat until I have said what I have to say.” So Laban said, “Speak on.”
34 Saboda haka ya ce, “Ni bawan Ibrahim ne.
He said, “I am Abraham's servant.
35 Ubangiji ya albarkaci maigidana sosai, ya kuma zama mai arziki. Ya ba shi tumaki, shanu, azurfa, zinariya, bayi maza da mata, raƙuma, da kuma jakuna.
Yahweh has blessed my master very much and he has become great. He has given him flocks and herds, silver and gold, male servants and female servants, and camels and donkeys.
36 Saratu matar maigidana ta haifa masa ɗa a tsufanta, ya kuma ba shi duk mallakarsa.
Sarah, my master's wife, bore a son to my master when she was old, and he has given everything that he owns to him.
37 Maigidana ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, ‘Kada ka ɗauko wa ɗana mata daga’ya’ya matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama a ƙasarsu,
My master made me swear, saying, 'You must not get a wife for my son from the daughters of the Canaanites, in whose land I make my home.
38 amma ka tafi wajen gidan mahaifina da kuma dangina, ka ɗauko wa ɗana mata.’
Instead, you must go to my father's family, and to my relatives, and get a wife for my son.'
39 “Sai na ce wa maigidana, ‘A ce matar ba tă yarda tă zo tare da ni ba fa?’
I said to my master, 'Perhaps the woman will not follow me.'
40 “Maigidana ya ce, ‘Ubangiji wanda yake tare da ni zai aiki mala’ikansa tare da kai, yă kuma sa tafiyarka tă yi nasara, don ka samo wa ɗana mata daga dangina, daga kuma gidan mahaifina.
But he said to me, 'Yahweh, before whom I walk, will send his angel with you and he will prosper your way, so that you will get a wife for my son from among my relatives and from my father's family line.
41 Ta haka za ka kuɓuta daga rantsuwata sa’ad da ka tafi wurin dangina, ko ma sun ƙi su ba ka ita, za ka kuɓuta daga rantsuwata.’
But you will be free from my oath if you come to my relatives and they will not give her to you. Then you will be free from my oath.'
42 “Sa’ad da na zo rijiya a yau, na ce, ‘Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ina roƙonka ka ba ni nasara a tafiyar da na yi.
So I arrived today at the spring, and said, 'O Yahweh, God of my master Abraham, please, if you do indeed intend to make my journey successful—
43 Duba, ina tsaye kusa da wannan rijiya; in wata yarinya ta fito domin tă ɗiba ruwa, wadda in na ce mata, “Ina roƙonki bari in ɗan sha ruwa daga tulunki,”
here I am, standing by the spring of water—let the young woman who comes out to draw water, the woman to whom I say, “Please give me a little water from your pitcher to drink,”
44 in ta ce, “Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma,” bari tă zama wadda Ubangiji ya zaɓar wa ɗan maigidana.’
the woman who says to me, “Drink, and I will also draw water for your camels”—let her be the woman whom you, Yahweh, have chosen for my master's son.'
45 “Kafin in gama addu’ar, a zuciyata, sai ga Rebeka ta fito da tulunta a kafaɗarta. Ta gangara zuwa rijiyar ta ɗebo ruwa, na kuma ce mata, ‘Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.’
Even before I had finished speaking in my heart, behold, Rebekah came out with her pitcher on her shoulder and she went down to the spring and drew water. So I said to her, 'Please give me a drink.'
46 “Ta yi sauri ta saukar da tulun daga kafaɗarta ta ce, ‘Sha, zan kuma ba wa raƙumanka su ma.’ Sai na sha, ta kuma shayar da raƙumana su ma.
She quickly lowered her pitcher from her shoulder and said, 'Drink, and I will give your camels water also.' So I drank, and she watered the camels also.
47 “Na tambaye ta, ‘Ke’yar wane ne?’ “Ta ce, ‘’Yar Betuwel ɗan Nahor, wanda Milka ta haifa masa.’ “Sai na sa mata zobe a hancinta, woroworo kuma a hannuwata,
I asked her and said, 'Whose daughter are you?' She said, 'The daughter of Bethuel, Nahor's son, whom Milkah bore to him.' Then I put the ring in her nose and the bracelets on her arms.
48 na kuma sunkuya na yi wa Ubangiji sujada. Na yabi Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim wanda ya bi da ni a hanyar da take daidai, don in samo wa ɗan maigidana jikanyar ɗan’uwansa.
Then I bowed down and worshiped Yahweh, and blessed Yahweh, the God of my master Abraham, who had led me by the right way to find the daughter of my master's relative for his son.
49 Yanzu fa in za ku nuna wa maigidana alheri da aminci, ku faɗa mini, in kuma ba haka ba, ku faɗa mini, don in san hanyar da zan juya.”
Now therefore, if you are prepared to show covenant faithfulness and trustworthiness to my master, tell me. But if not, tell me, so that I may turn to the right hand or to the left.”
50 Laban da Betuwel suka ce, “Wannan daga wurin Ubangiji ne, ba abin da za mu ce I, ko a’a ba.
Then Laban and Bethuel answered and said, “The thing has come from Yahweh; we cannot speak to you either bad or good.
51 Ga Rebeka, ɗauke ta ku tafi, bari tă zama matar ɗan maigidanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
Look, Rebekah is before you. Take her and go, so she may be the wife of your master's son, as Yahweh has spoken.”
52 Sa’ad da bawan Ibrahim ya ji abin da suka ce, sai ya rusuna har ƙasa a gaban Ubangiji.
When Abraham's servant heard their words, he bowed himself down to the ground to Yahweh.
53 Sa’an nan bawan ya fito da kayan ado na zinariya da azurfa da kayayyaki na tufafi ya ba wa Rebeka; ya kuma ba wa ɗan’uwanta da mahaifiyarta kyautai masu tsada.
The servant brought out articles of silver and articles of gold, and clothing, and gave them to Rebekah. He also gave precious gifts to her brother and to her mother.
54 Sa’an nan shi da mutanen da suke tare da shi suka ci, suka sha, suka kuma kwana a can. Kashegari da safe da suka tashi sai ya ce, “A sallame ni in koma wurin maigidana.”
Then he and the men who were with him ate and drank. They stayed there overnight, and when they arose in the morning, he said, “Send me away to my master.”
55 Amma ɗan’uwanta da mahaifiyarta suka ce, “Bari yarinyar ta ɗan zauna tare da mu kwana goma ko fiye, sa’an nan ka ta fi.”
Her brother and her mother said, “Let the young woman stay with us for a few more days, at least ten. After that she may go.”
56 Amma ya ce musu, “Kada ku tsai da ni, tun da Ubangiji ya ba ni nasara a tafiyata. Ku sallame ni domin in tafi wurin maigidana.”
But he said to them, “Do not hinder me, since Yahweh has prospered my way. Send me on my way so that I may go to my master.”
57 Sa’an nan suka ce, “Bari mu kira yarinyar mu tambaye ta game da zancen.”
They said, “We will call the young woman and ask her.”
58 Saboda haka suka kira Rebeka suka ce mata, “Za ki tafi tare da mutumin nan?” Sai ta ce, “Zan tafi.”
So they called Rebekah and asked her, “Will you go with this man?” She replied, “I will go.”
59 Saboda haka suka sallame Rebeka,’yar’uwarsu, duk da uwar goyonta da bawan Ibrahim da mutanensa.
So they sent their sister Rebekah, along with her female servant, on her journey with Abraham's servant and his men.
60 Suka kuma albarkaci Rebeka suka ce mata, “’Yar’uwarmu, bari ki zama mahaifiyar dubu dubbai, bari zuriyarki su mallaki ƙofofin abokan gābansu.”
They blessed Rebekah, and said to her, “Our sister, may you be the mother of thousands of ten thousands, and may your descendants possess the gate of those who hate them.”
61 Sa’an nan Rebeka da bayinta mata suka shirya suka hau raƙumansu suka koma tare da mutumin. Da haka bawan ya ɗauki Rebeka ya tafi.
Then Rebekah arose, and she and her servant girls mounted the camels, and followed the man. Thus the servant took Rebekah, and went his way.
62 Ishaku kuwa ya zo daga Beyer-Lahai-Royi, gama yana zama a Negeb.
Now Isaac was living in the Negev, and had just returned from Beer Lahai Roi.
63 Wata rana da yamma ya fita zuwa fili domin yă yi tunani, sa’ad da ya ɗaga ido, sai ya ga raƙuma suna zuwa.
Isaac went out to meditate in the field in the evening. When he looked up and saw, behold, there were camels coming!
64 Rebeka ma ta ɗaga ido sai ta ga Ishaku. Ta sauka daga raƙuminta da sauri,
Rebekah looked, and when she saw Isaac, she jumped down from the camel.
65 ta ce wa bawan, “Wane ne mutumin can a fili, da yake zuwa yă tarye mu?” Bawan ya ce, “Maigidana ne.” Saboda haka ta ɗauki mayafinta to rufe kanta.
She said to the servant, “Who is that man who is walking in the field to meet us?” The servant said, “It is my master.” So she took her veil, and covered herself.
66 Sai bawan ya faɗa wa Ishaku duk abin da ya yi.
The servant recounted to Isaac all the things that he had done.
67 Ishaku ya kawo ta cikin tentin mahaifiyarsa Saratu, ya kuma auri Rebeka. Ta haka ta zama matarsa, ya kuwa ƙaunace ta; Ishaku kuma ya ta’azantu bayan rasuwar mahaifiyarsa.
Then Isaac brought her into his mother Sarah's tent and took Rebekah, and she became his wife, and he loved her. So Isaac was comforted after his mother's death.

< Farawa 24 >