< Farawa 24 >

1 Yanzu fa Ibrahim ya tsufa, yana da shekaru masu yawa, Ubangiji kuma ya albarkace shi a kowace hanya.
Abraham was now a very old man. Yahweh had blessed Abraham in many ways.
2 Sai Ibrahim ya ce wa babban bawan gidansa, wanda yake lura da duk abin da yake da shi, “Sa hannunka a ƙarƙashin cinyata.
One day Abraham said to the chief servant of his household, the man who was in charge of everything Abraham owned, “Put your hand between my thighs to solemnly promise you will do what I tell you.
3 Ina so ka rantse da sunan Ubangiji Allah na sama da ƙasa, cewa ba za ka samo wa ɗana mata daga’yan matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama cikinsu ba.
Knowing that Yahweh God [who created] the heavens and the earth is listening, promise that you will not get a wife for my son, Isaac, from the women here in Canaan.
4 Amma za ka tafi ƙasata da kuma cikin’yan’uwana, ka samo mata saboda ɗana Ishaku.”
Instead, go back to my country and to my relatives and get a wife for my son Isaac from among them.”
5 Bawan ya ce masa, “Me zai faru in matar ba tă yarda tă zo tare da ni zuwa wannan ƙasa ba? In komar da ɗanka a ƙasar da ka fito ne ke nan?”
The servant asked him, “If I find a woman among your relatives, what if she is not willing to come back with me to this land? Shall I take your son back there to the country you came from, [so he can find a wife and live there]?”
6 Ibrahim ya ce, “Ka tabbata ba ka komar da ɗana can ba.”
Abraham replied to him, “No! Be certain that you don’t take my son there!
7 Ubangiji Allah na sama, wanda ya fitar da ni daga gidan mahaifina, da kuma ƙasar asalina wanda kuma ya yi magana da ni, ya yi mini alkawari da rantsuwa cewa, “Ga zuriyarka zan ba da wannan ƙasa, zai aika mala’ikansa yă sha gabanka domin ka samo wa ɗana mata daga can.
Yahweh God, who created the heavens, brought me here. He brought me from my father’s household, and from the land where my relatives lived. He spoke to me and made a solemn promise to me, saying, ‘I will give this land [of Canaan] to your descendants.’ He will send an angel who will go there ahead of you, and enable you to get a wife for my son [there and bring her to live here].
8 In matar ba tă yarda tă zo tare da kai ba, za a kuɓutar da kai daga wannan rantsuwa. Sai dai kada ka kai ɗana a can.”
But if the woman you find will not come back with you, you are free to disregard the promise you are making. The only thing that you must not do is to take my son to live there!”
9 Saboda haka bawan ya sa hannunsa a ƙarƙashin cinyar maigidansa Ibrahim, ya kuma rantse masa game da wannan al’amari.
So the servant put his hand between Abraham’s thighs and made a solemn promise about the matter.
10 Sai bawan ya ɗibi raƙuma goma na maigidansa ya tafi, ɗauke da kowane irin abubuwa masu kyau daga wurin maigidansa. Ya fita don yă tafi Aram-Naharayim, ya kama hanyarsa zuwa garin Nahor.
Then the servant took ten of his master’s camels and loaded them with all kinds of goods that his master gave him to take along. Then he left to go to Aram-Naharaim, [which is in (northern Mesopotamia/Syria)]. He arrived in Nahor city.
11 Ya sa raƙuman suka durƙusa kusa da rijiya a bayan gari; wajen yamma ne, lokacin da mata sukan fita ɗiban ruwa.
It was late in the afternoon, at the time when the women go to the well to get water, when he arrived there. He made the camels kneel down near the well, which was outside the city.
12 Sai ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ka ba ni nasara yau, ka kuma nuna alheri ga maigidana Ibrahim.
The servant prayed, “Yahweh God whom my master Abraham worships, enable me to be successful today! Act kindly to my master, Abraham!
13 Duba, ina tsaye a bakin rijiyar ruwa,’ya’ya matan mutanen gari kuma suna fitowa domin ɗiban ruwa.
Listen to me. I am standing near a well of water, and the young women of the city are coming to get water.
14 Bari yă zama sa’ad da na ce wa wata yarinya, ‘Ina roƙonki ki saukar da tulunki domin in sha,’ in ta ce, ‘Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma’; bari tă zama ita ce ka zaɓa wa bawanka Ishaku. Ta haka zan san cewa ka nuna wa maigidana alheri.”
I am asking you this: ‘I will say to some girl, “Please lower your jar so that I may drink some water.” If she says, “Drink some, and I will draw some water [from the well] for your camels, too,” I will know that she is the woman whom you chose to be a wife for your servant, Isaac, and I will know that you have been kind to my master.’”
15 Kafin ya gama addu’a, sai Rebeka ta fito da tulu a kafaɗarta. Ita’yar Betuwel ɗan Milka, matar Nahor, ɗan’uwan Ibrahim.
Before he finished praying, [amazingly], Rebekah arrived there, carrying a jar on her shoulder. She was the daughter of Bethuel, who was the son of Milcah, the wife of Abraham’s younger brother Nahor.
16 Yarinyar kuwa kyakkyawa ce, budurwa, ba namijin da ya taɓa kwana da ita. Ta gangara zuwa rijiyar, ta cika tulunta ta kuma hauro.
She was very beautiful and still a virgin. She went down to the edge of the well, filled her jar with water, and then came back up.
17 Bawan ya yi sauri ya same ta ya ce, “Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.”
Abraham’s servant immediately ran to meet her, and said, “Please give me a little water from your jar.”
18 Ta ce, “Ka sha, ranka yă daɗe,” ta yi sauri ta saukar da tulun a hannuwanta, ta kuma ba shi, ya sha.
She replied, “Drink some, sir!” She lowered her jar from her shoulder to her hands and gave him a drink.
19 Bayan ta ba shi ya sha, sai ta ce, “Zan ɗebo wa raƙumanka ruwa su ma, har sai sun gama sha.”
After she had finished giving him a drink, she said, “I will also get some water for your camels, until they have had enough to drink.”
20 Sai ta yi sauri ta juye ruwan da yake tulunta cikin kwami, ta koma zuwa rijiyar da gudu don ta ƙara ɗebo ruwa, ta kuma ɗebo isashe saboda dukan raƙumansa.
She quickly emptied the water in her jar into the trough [for giving water to animals], and then ran back to the well, and kept getting water for all the camels.
21 Mutumin bai ce uffam ba, ya dai kalle ta sosai don yă san ko Ubangiji ya ba shi nasara a tafiyarsa ko babu.
The servant just watched her, without saying anything. He wanted to know if Yahweh had caused his trip to be successful or not.
22 Sa’ad da raƙuman suka gama shan ruwa, mutumin ya fitar da zoben hanci na zinariya mai nauyin giram biyar da woroworo biyu na zinariya masu nauyin shekel goma, ya ba ta.
Finally, after the camels finished drinking, the servant took out a gold nose ring that weighed (two ounces/6 grams), and two large gold bracelets for her arms, and gave them to Rebekah [and told her to put them on].
23 Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Ke’yar wace ce? Ina roƙonki ki faɗa mini, akwai wuri a gidan mahaifinki da za mu kwana?”
Then he said, “Tell me whose daughter you are. Also, tell me, is there room in your father’s house for me and my men to sleep there tonight?”
24 Sai ta ce masa, “Ni’yar Betuwel ce ɗan da Milka ta haifa wa Nahor.”
She replied, “My father’s name is Bethuel. He is the son of Nahor and his wife Milcah.
25 Ta ƙara da cewa, “Muna da isashen ciyawa da abincin dabbobi, da kuma wuri domin ku kwana.”
Yes, we have room where you all can sleep tonight, and we also have plenty of straw and grain to feed the camels.”
26 Sa’an nan mutumin ya rusuna ya yi wa Ubangiji sujada,
The servant bowed and worshiped Yahweh.
27 yana cewa, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, wanda bai daina nuna alheri da amincinsa ga maigidana ba. Ni kam, Ubangiji ya bishe ni a tafiyata zuwa gidan’yan’uwan maigidana.”
He said, “I thank you, Yahweh God, whom my master Abraham worships. You have continued to be kind and faithful to my master. You led me on this journey straight/directly to the house of my master’s relatives!”
28 Yariyan ta gudu ta faɗa wa mutanen gidan mahaifiyarta game da abubuwan nan.
The girl ran and told everyone in her mother’s household about what had happened.
29 Rebeka fa tana da wani ɗan’uwa mai suna Laban, sai ya yi hanzari ya fita zuwa wurin mutumin a rijiyar.
Rebekah had a brother whose name was Laban. Laban went quickly to Abraham’s servant, who was still by the well.
30 Nan da nan da ya ga zoben hancin da woroworo a hannuwan’yar’uwansa, ya kuma ji Rebeka ta faɗa abin da mutumin ya ce mata, sai ya fita zuwa wurin mutumin, ya same shi yana tsaye wajen raƙuma kusa da rijiyar.
He was surprised to have seen the bracelets on his sister’s arms and the nose ring and to have heard Rebekah tell what the man had said to her. So he went out and saw the man standing near the camels, close to the well.
31 Sai ya ce, “Zo, ya kai mai albarka na Ubangiji, don me kake tsaye a waje? Gama na shirya gida da wuri domin raƙuma.”
He said to the man, “You who have been blessed by Yahweh, come with me! (Why are standing out here?/You should not keep standing out here!) [RHQ] I have prepared a room for you in the house, and a place for the camels to stay.”
32 Don haka mutumin ya tafi gidan, aka kuma saukar da kaya kan raƙuman. Aka kawo wa raƙuman ciyawa da abincin dabbobi, aka kuma kawo ruwa dominsa da mutanensa su wanke ƙafafunsu.
So the servant went to the house, and Laban’s servants unloaded the camels, and brought straw and grain for the camels, and water for him and the men with him to wash their feet.
33 Sa’an nan aka ajiye abinci a gabansa, amma ya ce, “Ba zan ci ba, sai na faɗi abin da yake tafe da ni.” Sai Laban ya ce, “Faɗa mana.”
They set food in front of him for him to eat, but he said, “I will not eat until I tell you (what I need to tell you/why I have come).” So Laban said, “Tell us!”
34 Saboda haka ya ce, “Ni bawan Ibrahim ne.
So the servant said, “I am Abraham’s servant.
35 Ubangiji ya albarkaci maigidana sosai, ya kuma zama mai arziki. Ya ba shi tumaki, shanu, azurfa, zinariya, bayi maza da mata, raƙuma, da kuma jakuna.
Yahweh has greatly blessed my master so that he has become very rich. Yahweh has given him many sheep and cattle, a lot of gold and silver, male and female servants, camels and donkeys.
36 Saratu matar maigidana ta haifa masa ɗa a tsufanta, ya kuma ba shi duk mallakarsa.
My master’s wife, Sarah, bore a son for him when she was very old, and my master has given to his son everything he owns.
37 Maigidana ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, ‘Kada ka ɗauko wa ɗana mata daga’ya’ya matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama a ƙasarsu,
My master made me solemnly promise, saying, ‘Do not get a wife for my son from the women here in Canaan.
38 amma ka tafi wajen gidan mahaifina da kuma dangina, ka ɗauko wa ɗana mata.’
Instead, go back to my father’s family, to my own clan, and get from them a wife for my son.’
39 “Sai na ce wa maigidana, ‘A ce matar ba tă yarda tă zo tare da ni ba fa?’
Then I asked my master, ‘What shall I do if the woman you show me will not come back with me?’
40 “Maigidana ya ce, ‘Ubangiji wanda yake tare da ni zai aiki mala’ikansa tare da kai, yă kuma sa tafiyarka tă yi nasara, don ka samo wa ɗana mata daga dangina, daga kuma gidan mahaifina.
He replied, ‘Yahweh, whom I have always obeyed [MTY], will send his angel with you, and he will cause your journey to be successful, with the result that you can get a wife for my son from my clan, from my father’s family.
41 Ta haka za ka kuɓuta daga rantsuwata sa’ad da ka tafi wurin dangina, ko ma sun ƙi su ba ka ita, za ka kuɓuta daga rantsuwata.’
But if my clan refuses to allow her to return with you, you will be freed from being cursed because of not obeying me.’
42 “Sa’ad da na zo rijiya a yau, na ce, ‘Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ina roƙonka ka ba ni nasara a tafiyar da na yi.
“When I came today to the well, I prayed, ‘Yahweh God whom my master, Abraham worships, if you are willing, please allow this journey of mine to be successful.
43 Duba, ina tsaye kusa da wannan rijiya; in wata yarinya ta fito domin tă ɗiba ruwa, wadda in na ce mata, “Ina roƙonki bari in ɗan sha ruwa daga tulunki,”
Listen to me. I am standing beside a well. A young woman may come to draw water. I will say to her, “Please, give me a little water to drink from your jar.”
44 in ta ce, “Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma,” bari tă zama wadda Ubangiji ya zaɓar wa ɗan maigidana.’
If she says to me, “Certainly, drink some! And I will also draw some water for your camels,” that will be the woman whom you have chosen for my master’s son!’
45 “Kafin in gama addu’ar, a zuciyata, sai ga Rebeka ta fito da tulunta a kafaɗarta. Ta gangara zuwa rijiyar ta ɗebo ruwa, na kuma ce mata, ‘Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.’
Before I finished praying, [amazingly], Rebekah approached with her water jar on her shoulder. She went down to the well and got some water. I said to her, ‘Please give me a drink!’
46 “Ta yi sauri ta saukar da tulun daga kafaɗarta ta ce, ‘Sha, zan kuma ba wa raƙumanka su ma.’ Sai na sha, ta kuma shayar da raƙumana su ma.
She quickly lowered her jar and said, ‘Drink some! And I will draw water [from the well] for your camels, too.’ So I drank some water, and she also got water for the camels.
47 “Na tambaye ta, ‘Ke’yar wane ne?’ “Ta ce, ‘’Yar Betuwel ɗan Nahor, wanda Milka ta haifa masa.’ “Sai na sa mata zobe a hancinta, woroworo kuma a hannuwata,
Then I asked her, ‘Whose daughter are you?’ She said, ‘The daughter of Bethuel, the son of Nahor and his wife, Milcah.’ I had [a ring and bracelets with me, and] I put the ring in her nose and put the bracelets on her arms.
48 na kuma sunkuya na yi wa Ubangiji sujada. Na yabi Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim wanda ya bi da ni a hanyar da take daidai, don in samo wa ɗan maigidana jikanyar ɗan’uwansa.
Then I bowed and worshiped Yahweh, and I thanked Yahweh God, the one my master Abraham worships, the one who led me on the right road to get the granddaughter of my master’s brother to be a wife for my master’s son.
49 Yanzu fa in za ku nuna wa maigidana alheri da aminci, ku faɗa mini, in kuma ba haka ba, ku faɗa mini, don in san hanyar da zan juya.”
Now, if you are kind and faithful to my master, tell me that you will do what I am asking. If you will not do that, tell me that also, so I may know what to do [MTY].”
50 Laban da Betuwel suka ce, “Wannan daga wurin Ubangiji ne, ba abin da za mu ce I, ko a’a ba.
Laban and Bethuel answered, “It is clear that Yahweh has caused this to happen. So we two cannot say anything more.
51 Ga Rebeka, ɗauke ta ku tafi, bari tă zama matar ɗan maigidanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
Rebekah is here in front of you. Take her and go, and let her be a wife for your master’s son, just as Yahweh has indicated.”
52 Sa’ad da bawan Ibrahim ya ji abin da suka ce, sai ya rusuna har ƙasa a gaban Ubangiji.
When Abraham’s servant heard these words, he bowed down to the ground to [thank] Yahweh.
53 Sa’an nan bawan ya fito da kayan ado na zinariya da azurfa da kayayyaki na tufafi ya ba wa Rebeka; ya kuma ba wa ɗan’uwanta da mahaifiyarta kyautai masu tsada.
Then the servant brought out silver and gold jewelry and clothes, and gave them to Rebekah. And he gave gifts to her brother Laban and to her mother.
54 Sa’an nan shi da mutanen da suke tare da shi suka ci, suka sha, suka kuma kwana a can. Kashegari da safe da suka tashi sai ya ce, “A sallame ni in koma wurin maigidana.”
Then they ate a meal together. The men who were with Abraham’s servant also slept there that night. The next morning, the servant said, “Allow me now to return to my master.”
55 Amma ɗan’uwanta da mahaifiyarta suka ce, “Bari yarinyar ta ɗan zauna tare da mu kwana goma ko fiye, sa’an nan ka ta fi.”
But her brother and her mother replied, “Let the girl remain with us for about ten days. After that, you may take her and go.”
56 Amma ya ce musu, “Kada ku tsai da ni, tun da Ubangiji ya ba ni nasara a tafiyata. Ku sallame ni domin in tafi wurin maigidana.”
But he replied to them, “Yahweh has made my journey successful, so do not detain me. Let me take her back to my master now!”
57 Sa’an nan suka ce, “Bari mu kira yarinyar mu tambaye ta game da zancen.”
They said, “Let’s call Rebekah and ask her what she wants to do.” [MTY]
58 Saboda haka suka kira Rebeka suka ce mata, “Za ki tafi tare da mutumin nan?” Sai ta ce, “Zan tafi.”
So they summoned Rebekah and asked her, “Will you go with this man now?” She replied, “Yes, I will go.”
59 Saboda haka suka sallame Rebeka,’yar’uwarsu, duk da uwar goyonta da bawan Ibrahim da mutanensa.
So they allowed Rebekah, a woman who had taken care of her when she was very young, Abraham’s servant, and the men who had come with him. to go.
60 Suka kuma albarkaci Rebeka suka ce mata, “’Yar’uwarmu, bari ki zama mahaifiyar dubu dubbai, bari zuriyarki su mallaki ƙofofin abokan gābansu.”
Before they all left, they [asked God to] bless Rebekah, and said to her, “Our sister, we ask that Yahweh will cause you to have millions of descendants, and allow them to completely defeat [MET] all those that hate them.”
61 Sa’an nan Rebeka da bayinta mata suka shirya suka hau raƙumansu suka koma tare da mutumin. Da haka bawan ya ɗauki Rebeka ya tafi.
Then Rebekah and her maid servants got ready and got on their camels and went with Abraham’s servant.
62 Ishaku kuwa ya zo daga Beyer-Lahai-Royi, gama yana zama a Negeb.
At that time, Isaac was living in the Negev desert. He had gone there from Beer-Lahai-Roi.
63 Wata rana da yamma ya fita zuwa fili domin yă yi tunani, sa’ad da ya ɗaga ido, sai ya ga raƙuma suna zuwa.
One evening he went out into the field to meditate as he walked. He looked up and [was surprised to] see some camels coming.
64 Rebeka ma ta ɗaga ido sai ta ga Ishaku. Ta sauka daga raƙuminta da sauri,
Rebekah also looked up and saw Isaac. She got off the camel,
65 ta ce wa bawan, “Wane ne mutumin can a fili, da yake zuwa yă tarye mu?” Bawan ya ce, “Maigidana ne.” Saboda haka ta ɗauki mayafinta to rufe kanta.
and asked the servant, “Who is that man who is approaching?” The servant replied, “That is Isaac, my master, [the man you will be marrying].” So she took her veil and covered her face, which was the custom for a woman who was about to be married.
66 Sai bawan ya faɗa wa Ishaku duk abin da ya yi.
The servant told Isaac everything that had happened.
67 Ishaku ya kawo ta cikin tentin mahaifiyarsa Saratu, ya kuma auri Rebeka. Ta haka ta zama matarsa, ya kuwa ƙaunace ta; Ishaku kuma ya ta’azantu bayan rasuwar mahaifiyarsa.
Then Isaac took Rebekah into the tent that belonged to his mother, Sarah, and she became his wife. And he loved her. So Isaac was comforted about his mother’s death.

< Farawa 24 >