< Farawa 24 >

1 Yanzu fa Ibrahim ya tsufa, yana da shekaru masu yawa, Ubangiji kuma ya albarkace shi a kowace hanya.
Og Abraham var gammel, vel ved Alder, og Herren havde velsignet Abraham i alting.
2 Sai Ibrahim ya ce wa babban bawan gidansa, wanda yake lura da duk abin da yake da shi, “Sa hannunka a ƙarƙashin cinyata.
Og Abraham sagde til sin ældste Svend i sit Hus, som raadede over alt hans Gods: Kære, læg din Haand under min Lænd,
3 Ina so ka rantse da sunan Ubangiji Allah na sama da ƙasa, cewa ba za ka samo wa ɗana mata daga’yan matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama cikinsu ba.
og jeg vil lade dig sværge ved Herren, Himmelens Gud og Jordens Gud, at du ikke skal tage min Søn en Hustru af Kananiternes Døtre, iblandt hvilke jeg bor;
4 Amma za ka tafi ƙasata da kuma cikin’yan’uwana, ka samo mata saboda ɗana Ishaku.”
men du skal gaa til mit Land og til min Slægt og tage min Søn Isak en Hustru.
5 Bawan ya ce masa, “Me zai faru in matar ba tă yarda tă zo tare da ni zuwa wannan ƙasa ba? In komar da ɗanka a ƙasar da ka fito ne ke nan?”
Og Svenden sagde til ham: Maaske Kvinden ikke vil drage med mig til dette Land; skal jeg da vel føre din Søn tilbage til det Land, som du er kommen fra?
6 Ibrahim ya ce, “Ka tabbata ba ka komar da ɗana can ba.”
Og Abraham sagde til ham: Forvar dig, at du ikke fører min Søn did igen.
7 Ubangiji Allah na sama, wanda ya fitar da ni daga gidan mahaifina, da kuma ƙasar asalina wanda kuma ya yi magana da ni, ya yi mini alkawari da rantsuwa cewa, “Ga zuriyarka zan ba da wannan ƙasa, zai aika mala’ikansa yă sha gabanka domin ka samo wa ɗana mata daga can.
Herren, Himmelens Gud, som tog mig fra min Faders Hus og fra min Slægts Land, og som talede med mig, og som tilsvor mig og sagde: dette Land vil jeg give din Sæd, han skal sende sin Engel for dig, at du skal tage min Søn en Hustru derfra.
8 In matar ba tă yarda tă zo tare da kai ba, za a kuɓutar da kai daga wannan rantsuwa. Sai dai kada ka kai ɗana a can.”
Men dersom Kvinden ikke vil følge dig, da skal du være fri for denne min Ed; ikkun min Søn skal du ikke føre derhen.
9 Saboda haka bawan ya sa hannunsa a ƙarƙashin cinyar maigidansa Ibrahim, ya kuma rantse masa game da wannan al’amari.
Da lagde Svenden sin Haand under Abrahams, sin Herres, Lænd og tilsvor ham om denne Sag.
10 Sai bawan ya ɗibi raƙuma goma na maigidansa ya tafi, ɗauke da kowane irin abubuwa masu kyau daga wurin maigidansa. Ya fita don yă tafi Aram-Naharayim, ya kama hanyarsa zuwa garin Nahor.
Saa tog Svenden ti Kameler af sin Herres Kameler og for bort og havde alle Haande af sin Herres Gods med sig og gjorde sig rede og drog til Aram Naharaim, til Nakors Stad.
11 Ya sa raƙuman suka durƙusa kusa da rijiya a bayan gari; wajen yamma ne, lokacin da mata sukan fita ɗiban ruwa.
Der lod han Kamelerne lægge sig uden for Staden ved en Vandbrønd mod Aftens Tid, mod den Tid da Kvinderne gaa ud at drage Vand.
12 Sai ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ka ba ni nasara yau, ka kuma nuna alheri ga maigidana Ibrahim.
Og han sagde: Herre, min Herre Abrahams Gud! Kære, lad det møde mig i Dag, og gør Miskundhed mod min Herre Abraham.
13 Duba, ina tsaye a bakin rijiyar ruwa,’ya’ya matan mutanen gari kuma suna fitowa domin ɗiban ruwa.
Se, jeg staar ved denne Vandbrønd, og Byens Folks Døtre komme ud at drage Vand.
14 Bari yă zama sa’ad da na ce wa wata yarinya, ‘Ina roƙonki ki saukar da tulunki domin in sha,’ in ta ce, ‘Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma’; bari tă zama ita ce ka zaɓa wa bawanka Ishaku. Ta haka zan san cewa ka nuna wa maigidana alheri.”
Og naar det sker, at der kommer en Pige, til hvem jeg siger: Bøj nu din Krukke ned og lad mig drikke, og hun siger: Drik, og jeg vil ogsaa give dine Kameler at drikke, lad hende da være den, som du har udset til din Tjener Isak, saa jeg derpaa kan kende, at du har gjort Miskundhed mod min Herre.
15 Kafin ya gama addu’a, sai Rebeka ta fito da tulu a kafaɗarta. Ita’yar Betuwel ɗan Milka, matar Nahor, ɗan’uwan Ibrahim.
Og det skete, før han havde endt at tale, se, da kom Rebekka ud, som var en Datter af Bethuel, som var en Søn af Milka, Nakors, Abrahams Broders, Hustru, og hendes Krukke var paa hendes Skulder.
16 Yarinyar kuwa kyakkyawa ce, budurwa, ba namijin da ya taɓa kwana da ita. Ta gangara zuwa rijiyar, ta cika tulunta ta kuma hauro.
Og Pigen var meget smuk af Anseelse, en Jomfru, og ingen Mand havde kendt hende, og hun gik ned til Brønden og fyldte sin Krukke og gik op.
17 Bawan ya yi sauri ya same ta ya ce, “Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.”
Da løb Svenden imod hende og sagde: Kære, lad mig drikke lidt Vand af din Krukke.
18 Ta ce, “Ka sha, ranka yă daɗe,” ta yi sauri ta saukar da tulun a hannuwanta, ta kuma ba shi, ya sha.
Og hun sagde: Drik, min Herre! og hun skyndte sig og tog sin Krukke ned i sin Haand og gav ham at drikke.
19 Bayan ta ba shi ya sha, sai ta ce, “Zan ɗebo wa raƙumanka ruwa su ma, har sai sun gama sha.”
Der hun havde givet ham at drikke, da sagde hun: Jeg vil og drage Vand til dine Kameler, til de have afdrukket.
20 Sai ta yi sauri ta juye ruwan da yake tulunta cikin kwami, ta koma zuwa rijiyar da gudu don ta ƙara ɗebo ruwa, ta kuma ɗebo isashe saboda dukan raƙumansa.
Og hun skyndte sig og tømte sin Krukke i Truget og løb fremdeles til Brønden at øse, og hun drog til alle hans Kameler.
21 Mutumin bai ce uffam ba, ya dai kalle ta sosai don yă san ko Ubangiji ya ba shi nasara a tafiyarsa ko babu.
Og Manden undrede sig over hende, tav dog stille for at faa at vide, om Herren havde ladet hans Rejse lykkes eller ej.
22 Sa’ad da raƙuman suka gama shan ruwa, mutumin ya fitar da zoben hanci na zinariya mai nauyin giram biyar da woroworo biyu na zinariya masu nauyin shekel goma, ya ba ta.
Og det skete, der Kamelerne havde afdrukket, gav Manden hende en Guldring, som vejede en halv Sekel, og satte to Armbaand paa hendes Hænder, de vejede ti Guldsekler.
23 Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Ke’yar wace ce? Ina roƙonki ki faɗa mini, akwai wuri a gidan mahaifinki da za mu kwana?”
Og han sagde: Hvis Datter er du? Kære, sig mig, monne der være Rum i din Faders Hus at give os Nattely?
24 Sai ta ce masa, “Ni’yar Betuwel ce ɗan da Milka ta haifa wa Nahor.”
Og hun sagde til ham: Jeg er en Datter af Bethuel, som er en Søn af Milka, der fødte ham for Nakor.
25 Ta ƙara da cewa, “Muna da isashen ciyawa da abincin dabbobi, da kuma wuri domin ku kwana.”
Og hun sagde til ham: Der er baade Straa og meget Foder hos os, ogsaa er der Rum til Herberge i Nat.
26 Sa’an nan mutumin ya rusuna ya yi wa Ubangiji sujada,
Og Manden bøjede sig og tilbad Herren.
27 yana cewa, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, wanda bai daina nuna alheri da amincinsa ga maigidana ba. Ni kam, Ubangiji ya bishe ni a tafiyata zuwa gidan’yan’uwan maigidana.”
Og han sagde: Lovet være Herren, min Herre Abrahams Gud, som ikke har afladt med sin Miskundhed og sin Trofasthed mod min Herre! mig, ja, mig har Herren ført paa Vejen til min Herres Broders Hus.
28 Yariyan ta gudu ta faɗa wa mutanen gidan mahaifiyarta game da abubuwan nan.
Og Pigen løb og kundgjorde i sin Moders Hus disse Ting.
29 Rebeka fa tana da wani ɗan’uwa mai suna Laban, sai ya yi hanzari ya fita zuwa wurin mutumin a rijiyar.
Og Rebekka havde en Broder, og hans Navn var Laban, og Laban løb ud til Manden, til Brønden.
30 Nan da nan da ya ga zoben hancin da woroworo a hannuwan’yar’uwansa, ya kuma ji Rebeka ta faɗa abin da mutumin ya ce mata, sai ya fita zuwa wurin mutumin, ya same shi yana tsaye wajen raƙuma kusa da rijiyar.
Og det skete, der han saa Ringen og Armbaandene paa sin Søsters Hænder, og der han hørte Rebekkas, sin Søsters, Ord, at hun sagde: Saaledes har Manden sagt til mig, da kom han til Manden, og se, han stod hos Kamelerne ved Brønden.
31 Sai ya ce, “Zo, ya kai mai albarka na Ubangiji, don me kake tsaye a waje? Gama na shirya gida da wuri domin raƙuma.”
Og han sagde: Kom ind, du Herrens Velsignede, hvi staar du herude? thi jeg har beredt Huset, og der er Rum for Kamelerne.
32 Don haka mutumin ya tafi gidan, aka kuma saukar da kaya kan raƙuman. Aka kawo wa raƙuman ciyawa da abincin dabbobi, aka kuma kawo ruwa dominsa da mutanensa su wanke ƙafafunsu.
Saa kom Manden i Huset og løste Kamelerne, og han gav Straa og Foder til Kamelerne, og Vand til at to hans Fødder og de Mænds Fødder, som vare med ham.
33 Sa’an nan aka ajiye abinci a gabansa, amma ya ce, “Ba zan ci ba, sai na faɗi abin da yake tafe da ni.” Sai Laban ya ce, “Faɗa mana.”
Og der blev sat Mad for ham; men han sagde: Jeg vil ikke æde, før jeg har udsagt mit Ærinde; og han sagde: Tal!
34 Saboda haka ya ce, “Ni bawan Ibrahim ne.
Og han sagde: Jeg er Abrahams Svend.
35 Ubangiji ya albarkaci maigidana sosai, ya kuma zama mai arziki. Ya ba shi tumaki, shanu, azurfa, zinariya, bayi maza da mata, raƙuma, da kuma jakuna.
Og Herren har velsignet min Herre meget, at han er bleven mægtig; og han har givet ham Faar og Kvæg og Sølv og Guld og Svende og Tjenestepiger og Kameler og Asener.
36 Saratu matar maigidana ta haifa masa ɗa a tsufanta, ya kuma ba shi duk mallakarsa.
Og Sara, min Herres Hustru, har født min Herre en Søn, efter at hun var gammel, og denne har han givet alt det, han ejer.
37 Maigidana ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, ‘Kada ka ɗauko wa ɗana mata daga’ya’ya matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama a ƙasarsu,
Og min Herre har taget en Ed af mig og sagt: Du skal ikke tage min Søn en Hustru af Kananiternes Døtre, i hvis Land jeg bor.
38 amma ka tafi wajen gidan mahaifina da kuma dangina, ka ɗauko wa ɗana mata.’
Men du skal fare hen til min Faders Hus og til min Slægt og tage min Søn en Hustru.
39 “Sai na ce wa maigidana, ‘A ce matar ba tă yarda tă zo tare da ni ba fa?’
Og jeg sagde til min Herre: Maaske Kvinden ikke vil drage med mig.
40 “Maigidana ya ce, ‘Ubangiji wanda yake tare da ni zai aiki mala’ikansa tare da kai, yă kuma sa tafiyarka tă yi nasara, don ka samo wa ɗana mata daga dangina, daga kuma gidan mahaifina.
Og han sagde til mig: Herren, for hvis Ansigt jeg har vandret, skal sende sin Engel med dig og give dig en lyksalig Rejse, og du skal tage min Søn en Hustru af min Slægt og af min Faders Hus.
41 Ta haka za ka kuɓuta daga rantsuwata sa’ad da ka tafi wurin dangina, ko ma sun ƙi su ba ka ita, za ka kuɓuta daga rantsuwata.’
Da skal du være fri for min Ed, naar du kommer til min Slægt; og om de ikke ville give dig hende, saa er du fri for min Ed.
42 “Sa’ad da na zo rijiya a yau, na ce, ‘Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ina roƙonka ka ba ni nasara a tafiyar da na yi.
Saa kom jeg i Dag til Brønden og sagde: Herre, min Herre Abrahams Gud! Kære, dersom du har givet Lykke paa min Rejse, paa hvilken jeg har vandret,
43 Duba, ina tsaye kusa da wannan rijiya; in wata yarinya ta fito domin tă ɗiba ruwa, wadda in na ce mata, “Ina roƙonki bari in ɗan sha ruwa daga tulunki,”
se, jeg staar ved denne Vandbrønd, og naar det sker, der kommer en Jomfru ud at drage Vand, og jeg siger til hende: Giv mig nu lidet Vand at drikke af din Krukke;
44 in ta ce, “Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma,” bari tă zama wadda Ubangiji ya zaɓar wa ɗan maigidana.’
og hun siger mig: Baade maa du drikke, og jeg vil ogsaa øse til dine Kameler, lad hende være den Kvinde, som Herren har udset til min Herres Søn.
45 “Kafin in gama addu’ar, a zuciyata, sai ga Rebeka ta fito da tulunta a kafaɗarta. Ta gangara zuwa rijiyar ta ɗebo ruwa, na kuma ce mata, ‘Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.’
Førend jeg havde udtalet i mit Hjerte, se, da kom Rebekka ud, og hendes Krukke var paa hendes Skulder, og hun gik ned til Brønden og drog Vand! da sagde jeg til hende: Kære, giv mig at drikke.
46 “Ta yi sauri ta saukar da tulun daga kafaɗarta ta ce, ‘Sha, zan kuma ba wa raƙumanka su ma.’ Sai na sha, ta kuma shayar da raƙumana su ma.
Saa skyndte hun sig og tog sin Krukke ned ad sig og sagde: Drik, og jeg vil ogsaa give dine Kameler at drikke; og jeg drak, og hun gav ogsaa Kamelerne at drikke.
47 “Na tambaye ta, ‘Ke’yar wane ne?’ “Ta ce, ‘’Yar Betuwel ɗan Nahor, wanda Milka ta haifa masa.’ “Sai na sa mata zobe a hancinta, woroworo kuma a hannuwata,
Og jeg spurgte hende og sagde: Hvis Datter er du? og hun sagde: Jeg er en Datter af Bethuel, Nakors Søn, som Milka fødte ham. Saa hængte jeg en Ring i hendes Næse og Armbaand paa hendes Hænder.
48 na kuma sunkuya na yi wa Ubangiji sujada. Na yabi Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim wanda ya bi da ni a hanyar da take daidai, don in samo wa ɗan maigidana jikanyar ɗan’uwansa.
Og jeg bøjede mig og tilbad Herren og lovede Herren, min Herre Abrahams Gud, som havde ledet mig paa den rette Vej at tage min Herres Broders Datter til hans Søn.
49 Yanzu fa in za ku nuna wa maigidana alheri da aminci, ku faɗa mini, in kuma ba haka ba, ku faɗa mini, don in san hanyar da zan juya.”
Og nu, dersom I ville vise Miskundhed og Trofasthed mod min Herre, siger mig det; men dersom I ikke ville det, da siger mig det, at jeg kan vende mig til den højre eller til den venstre Side.
50 Laban da Betuwel suka ce, “Wannan daga wurin Ubangiji ne, ba abin da za mu ce I, ko a’a ba.
Da svarede Laban og Bethuel og sagde: Denne Sag er kommen fra Herren, vi kunne hverken tale til dig ondt eller godt.
51 Ga Rebeka, ɗauke ta ku tafi, bari tă zama matar ɗan maigidanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
Se, der er Rebekka for dig, tag hende og gak, at hmi bliver din Herres Søns Hustru, som Herren har sagt.
52 Sa’ad da bawan Ibrahim ya ji abin da suka ce, sai ya rusuna har ƙasa a gaban Ubangiji.
Og det skete, der Abrahams Svend hørte deres Ord, da bøjede han sig til Jorden for Herren.
53 Sa’an nan bawan ya fito da kayan ado na zinariya da azurfa da kayayyaki na tufafi ya ba wa Rebeka; ya kuma ba wa ɗan’uwanta da mahaifiyarta kyautai masu tsada.
Og Svenden udtog Sølvtøj og Guldtøj og Klæder og gav Rebekka; men hendes Broder og hendes Moder gav han dyrebar Skænk.
54 Sa’an nan shi da mutanen da suke tare da shi suka ci, suka sha, suka kuma kwana a can. Kashegari da safe da suka tashi sai ya ce, “A sallame ni in koma wurin maigidana.”
Saa aade de og drak, han og de Mænd, som vare med ham, og bleve der om Natten, og de stode op om Morgenen, og han sagde: Lader mig fare til min Herre!
55 Amma ɗan’uwanta da mahaifiyarta suka ce, “Bari yarinyar ta ɗan zauna tare da mu kwana goma ko fiye, sa’an nan ka ta fi.”
Da sagde hendes Broder og hendes Moder: Lad Pigen blive hos os nogle Dage eller ti, siden maa du fare.
56 Amma ya ce musu, “Kada ku tsai da ni, tun da Ubangiji ya ba ni nasara a tafiyata. Ku sallame ni domin in tafi wurin maigidana.”
Og han sagde til dem: Holder mig ikke op, thi Herren har givet Lykke paa min Rejse; lader mig fare, og jeg vil vandre til min Herre.
57 Sa’an nan suka ce, “Bari mu kira yarinyar mu tambaye ta game da zancen.”
Og de sagde: Lader os kalde Pigen og spørge, hvad hun siger.
58 Saboda haka suka kira Rebeka suka ce mata, “Za ki tafi tare da mutumin nan?” Sai ta ce, “Zan tafi.”
Saa kaldte de ad Rebekka og sagde til hende: Vil du fare med denne Mand? og hun sagde: Jeg vil fare.
59 Saboda haka suka sallame Rebeka,’yar’uwarsu, duk da uwar goyonta da bawan Ibrahim da mutanensa.
Saa lode de deres Søster Rebekka og hendes Amme og Abrahams Svend og hans Mænd fare.
60 Suka kuma albarkaci Rebeka suka ce mata, “’Yar’uwarmu, bari ki zama mahaifiyar dubu dubbai, bari zuriyarki su mallaki ƙofofin abokan gābansu.”
Og de velsignede Rebekka og sagde til hende: Vor Søster! bliv du til tusinde Gange Titusinde, og din Sæd skal eje sine Fjenders Port.
61 Sa’an nan Rebeka da bayinta mata suka shirya suka hau raƙumansu suka koma tare da mutumin. Da haka bawan ya ɗauki Rebeka ya tafi.
Saa stod Rebekka op og hendes Piger, og de satte sig paa Kameler og fore med Manden, og Svenden annammede Rebekka og for bort.
62 Ishaku kuwa ya zo daga Beyer-Lahai-Royi, gama yana zama a Negeb.
Og Isak kom gaaende fra den Brønd, som kaldes Beer Lakai Roi; thi han boede i Landet imod Sønden.
63 Wata rana da yamma ya fita zuwa fili domin yă yi tunani, sa’ad da ya ɗaga ido, sai ya ga raƙuma suna zuwa.
Og Isak var udgangen til at gøre Bøn paa Marken mod Aften, og han opløftede sine Øjne og saa, og se, Kamelerne kom.
64 Rebeka ma ta ɗaga ido sai ta ga Ishaku. Ta sauka daga raƙuminta da sauri,
Og Rebekka opløftede sine Øjne og saa Isak og steg hastig ned ad Kamelen.
65 ta ce wa bawan, “Wane ne mutumin can a fili, da yake zuwa yă tarye mu?” Bawan ya ce, “Maigidana ne.” Saboda haka ta ɗauki mayafinta to rufe kanta.
Og hun sagde til Svenden: Hvo er den Mand, som gaar paa Marken imod os? og Svenden sagde: Det er min Herre; saa tog hun et Slør og skjulte sig.
66 Sai bawan ya faɗa wa Ishaku duk abin da ya yi.
Og Svenden fortalte Isak hele Sagen, som han havde udrettet.
67 Ishaku ya kawo ta cikin tentin mahaifiyarsa Saratu, ya kuma auri Rebeka. Ta haka ta zama matarsa, ya kuwa ƙaunace ta; Ishaku kuma ya ta’azantu bayan rasuwar mahaifiyarsa.
Saa ledte Isak hende til sin Moder Saras Telt, og han tog Rebekka, og hun blev hans Hustru, og han elskede hende; og Isak blev trøstet efter sin Moder.

< Farawa 24 >