< Farawa 23 >
1 Saratu ta yi shekara ɗari da ashirin da bakwai a duniya.
And Sarah was a hundred and twenty-seven years old: [these were] the years of the life of Sarah.
2 Ta rasu a Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar Kan’ana, Ibrahim kuwa ya tafi ya yi makokin Saratu, yana kuka saboda ita.
And Sarah died in Kirjath-arba; the same [is] Hebron in the land of Canaan: And Abraham came to mourn for Sarah, and to weep for her.
3 Sai Ibrahim ya tashi daga gefen matarsa da ta mutu, ya yi magana da Hittiyawa. Ya ce,
And Abraham stood up from before his dead, and spoke to the sons of Heth, saying,
4 “Ni baƙo ne, kuma baƙo a cikinku. Ku sayar mini da wani wuri yă zama wurin binnewa a nan, domin in binne mataccena.”
I [am] a stranger and a sojourner with you; give me a possession of a burying-place with you, that I may bury my dead out of my sight.
5 Hittiyawa suka ce wa Ibrahim,
And the children of Heth answered Abraham, saying to him,
6 “Ranka yă daɗe, ka saurare mu. Kai babban yerima ne a cikinmu. Ka binne mataccenka a kabari mafi kyau na kaburburanmu. Babu waninmu da zai hana ka kabarinsa don binne mataccenka.”
Hear us, my lord; thou [art] a mighty prince among us: in the choice of our sepulchers bury thy dead: none of us will withhold from thee his sepulcher, but that thou mayest bury thy dead.
7 Sai Ibrahim ya tashi ya rusuna a gaban mutanen ƙasar, wato, Hittiyawan.
And Abraham stood up and bowed himself to the people of the land, to the children of Heth.
8 Ya ce musu, “In kuna so in binne mataccena, sai ku ji ni, ku roƙi Efron ɗan Zohar a madadina
And he communed with them, saying, If it is your mind that I should bury my dead out of my sight, hear me, and entreat for me to Ephron the son of Zohar,
9 domin yă sayar mini da kogon Makfela, wanda yake nasa, wannan da yake a ƙarshen filinsa. Ku ce masa yă sayar mini a cikakken farashi, yă zama mallakata domin makabarta tsakaninku.”
That he may give me the cave of Machpelah, which he hath, which [is] in the end of his field; for as much money as it is worth he shall give it me, for a possession of a burying-place among you.
10 Efron mutumin Hitti yana zaune a cikin mutanensa, sai ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birni.
And Ephron dwelt among the children of Heth. And Ephron the Hittite answered Abraham in the audience of the children of Heth, of all that entered the gates of his city, saying,
11 Ya ce, “A’a, ranka yă daɗe, ka ji ni, na ba ka filin, na kuma ba ka kogon da yake cikinsa. Na ba ka shi a gaban mutanena. Ka binne mataccenka.”
Nay, my lord, hear me: the field give I to thee, and the cave that [is] in it, I give it to thee; in the presence of the sons of my people I give it to thee: bury thy dead.
12 Ibrahim ya sāke rusuna a gaban mutanen ƙasar
And Abraham bowed himself before the people of the land.
13 ya ce wa Efron a kunnuwansu, “Ka ji, in ka yarda. Zan biya farashin filin. Ka karɓa daga gare ni don in iya binne mataccena a can.”
And he spoke to Ephron in the audience of the people of the land, saying, But if thou [wilt give it], I pray thee, hear me: I will give thee money for the field: take [it] of me, and I will bury my dead there.
14 Efron ya ce wa Ibrahim,
And Ephron answered Abraham, saying to him,
15 “Ka saurare ni, ranka yă daɗe; darajan filin ya kai shekel ɗari huɗu na azurfa, amma mene ne wannan a tsakanina da kai? Ka binne mataccenka.”
My lord, hearken to me: the land [is worth] four hundred shekels of silver; what [is] that betwixt me and thee? bury therefore thy dead.
16 Ibrahim ya yarda da sharuɗan Efron, sai ya auna masa farashin da ya faɗa a kunnuwan Hittiyawa, shekel ɗari huɗu na azurfa, bisa ga ma’aunin da’yan kasuwa suke amfani da shi a lokacin.
And Abraham hearkened to Ephron; and Abraham weighed to Ephron the silver which he had named in the audience of the sons of Heth, four hundred shekels of silver, current [money] with the merchant.
17 Ta haka filin Efron a Makfela kusa da Mamre, wato, filin da kogon a cikinsa, da kuma dukan itatuwan da suke cikin iyakoki filin, aka
And the field of Ephron, which [was] in Machpelah, which [was] before Mamre, the field and the cave which [was] in it, and all the trees that [were] in the field, that [were] in all the borders round about, were made sure
18 ba wa Ibrahim a matsayin mallakarsa a gaban dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birnin.
To Abraham for a possession in the presence of the children of Heth, before all that entered the gate of his city.
19 Bayan wannan Ibrahim ya binne matarsa Saratu a kogon a filin Makfela kusa da Mamre (wanda yake a Hebron) a ƙasar Kan’ana.
And after this, Abraham buried Sarah his wife in the cave of the field of Machpelah, before Mamre: the same [is] Hebron in the land of Canaan.
20 Da filin da kuma kogon da yake cikinsa, Hittiyawa suka tabbatar wa Ibrahim a matsayin makabarta.
And the field, and the cave that [is] in it were made sure to Abraham for a possession of a burying-place, by the sons of Heth.